Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 47

۞إِلَيۡهِ يُرَدُّ عِلۡمُ ٱلسَّاعَةِۚ وَمَا تَخۡرُجُ مِن ثَمَرَٰتٖ مِّنۡ أَكۡمَامِهَا وَمَا تَحۡمِلُ مِنۡ أُنثَىٰ وَلَا تَضَعُ إِلَّا بِعِلۡمِهِۦۚ وَيَوۡمَ يُنَادِيهِمۡ أَيۡنَ شُرَكَآءِي قَالُوٓاْ ءَاذَنَّـٰكَ مَامِنَّا مِن شَهِيدٖ

Gare shi ne ake mayar da sanin lokacin alqiyama. Kuma babu wasu ‘ya’yan itatuwa da suke fitowa daga kwansonsu, babu kuma wata mace da take xaukan ciki ko take haifewa sai da saninsa. Kuma a ranar da zai yi kiran su cewa: “Ina abokan tarayyar tawa?” Za su ce: “Mun sanar da Kai (a yau) babu wani mai yin shaida daga cikinmu[1].”


1- Watau babu wani da zai ba da shaidar cewa, Allah yana da abokan tarayya.


Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 48

وَضَلَّ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يَدۡعُونَ مِن قَبۡلُۖ وَظَنُّواْ مَا لَهُم مِّن مَّحِيصٖ

Kuma abin da suka kasance suna bauta wa a da ya vace musu, suka kuma tabbatar ba su da wata matsera



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 49

لَّا يَسۡـَٔمُ ٱلۡإِنسَٰنُ مِن دُعَآءِ ٱلۡخَيۡرِ وَإِن مَّسَّهُ ٱلشَّرُّ فَيَـُٔوسٞ قَنُوطٞ

Mutum ba ya qosawa wajen roqon alheri, idan kuwa wani sharri ya same shi, to sai ya zama mai tsananin xebe qauna



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 50

وَلَئِنۡ أَذَقۡنَٰهُ رَحۡمَةٗ مِّنَّا مِنۢ بَعۡدِ ضَرَّآءَ مَسَّتۡهُ لَيَقُولَنَّ هَٰذَا لِي وَمَآ أَظُنُّ ٱلسَّاعَةَ قَآئِمَةٗ وَلَئِن رُّجِعۡتُ إِلَىٰ رَبِّيٓ إِنَّ لِي عِندَهُۥ لَلۡحُسۡنَىٰۚ فَلَنُنَبِّئَنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِمَا عَمِلُواْ وَلَنُذِيقَنَّهُم مِّنۡ عَذَابٍ غَلِيظٖ

Tabbas kuma idan Muka xanxana masa wata rahama tamu bayan wata cuta da ta same shi, tabbas zai riqa cewa: “Wannan nawa ne, kuma ba na tsammanin alqiyama za ta tashi, kuma tabbas idan ma da za a mayar da ni zuwa ga Ubangijina, lalle zan zama mai samun mafi kyan sakamako a wurinsa.” To tabbas za Mu saka wa waxanda suka kafirta da abin da suka aikata, kuma tabbas za Mu xanxana musu azaba mai gwavi



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 51

وَإِذَآ أَنۡعَمۡنَا عَلَى ٱلۡإِنسَٰنِ أَعۡرَضَ وَنَـَٔا بِجَانِبِهِۦ وَإِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ فَذُو دُعَآءٍ عَرِيضٖ

Idan kuma Muka yi wa mutum ni’ima sai ya bijire ya ja jikinsa nesa (daga tuna Allah), kuma idan sharri ya same shi, sai ya zama mai faffaxar addu’a



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 52

قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِن كَانَ مِنۡ عِندِ ٱللَّهِ ثُمَّ كَفَرۡتُم بِهِۦ مَنۡ أَضَلُّ مِمَّنۡ هُوَ فِي شِقَاقِۭ بَعِيدٖ

Ka ce: “Ku ba ni labari, idan (Alqur’ani) ya kasance daga wajen Allah, sannan kuka kafirce masa, to wane ne ya fi vata fiye da wanda yake cikin savani mai nisa?”



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 53

سَنُرِيهِمۡ ءَايَٰتِنَا فِي ٱلۡأٓفَاقِ وَفِيٓ أَنفُسِهِمۡ حَتَّىٰ يَتَبَيَّنَ لَهُمۡ أَنَّهُ ٱلۡحَقُّۗ أَوَلَمۡ يَكۡفِ بِرَبِّكَ أَنَّهُۥ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Ba da daxewa ba za Mu nuna musu ayoyinmu a cikin nahiyoyi da kuma a kan kawunansu har sai sun gane cewa lalle shi (Alqur’ani) gaskiya ne. Yanzu bai ishe ka ba game da Ubangijinka cewa Shi lalle Mai shaida ne a kan komai?



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 54

أَلَآ إِنَّهُمۡ فِي مِرۡيَةٖ مِّن لِّقَآءِ رَبِّهِمۡۗ أَلَآ إِنَّهُۥ بِكُلِّ شَيۡءٖ مُّحِيطُۢ

Ku saurara, lalle su suna cikin kokwanto ne game da haxuwa da Ubangijnsu. Ku saurara, lalle Shi Mai kewaye komai ne da saninsa



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 1

حمٓ

HA MIM



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 2

عٓسٓقٓ

AIN SIN QAF[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Capítulo: Suratus Shura

Verso : 3

كَذَٰلِكَ يُوحِيٓ إِلَيۡكَ وَإِلَى ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِكَ ٱللَّهُ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Kamar haka ne Allah Mabuwayi, Mai hikima Yake yi maka wahayi da kuma waxanda suka gabace ka



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 4

لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۖ وَهُوَ ٱلۡعَلِيُّ ٱلۡعَظِيمُ

Abin da yake cikin sammai da abin da yake cikin qasa nasa ne; kuma Shi Maxaukaki ne, Mai girma



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 5

تَكَادُ ٱلسَّمَٰوَٰتُ يَتَفَطَّرۡنَ مِن فَوۡقِهِنَّۚ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ يُسَبِّحُونَ بِحَمۡدِ رَبِّهِمۡ وَيَسۡتَغۡفِرُونَ لِمَن فِي ٱلۡأَرۡضِۗ أَلَآ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Sammai suna neman su tsattsage ta samansu (don girmansa). Mala’iku kuma suna yin tasbihi da yabon Ubangijinsu, suna kuma neman gafara ga waxanda suke cikin qasa. Ku saurara, Lalle Allah Shi ne Mai gafara, Mai rahama



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 6

وَٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَ ٱللَّهُ حَفِيظٌ عَلَيۡهِمۡ وَمَآ أَنتَ عَلَيۡهِم بِوَكِيلٖ

Waxanda kuwa suka riqi wasu majivinta ba shi ba, Allah Mai kiyaye da su ne, kai kuma ba wakili ne ba a kansu



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 7

وَكَذَٰلِكَ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ قُرۡءَانًا عَرَبِيّٗا لِّتُنذِرَ أُمَّ ٱلۡقُرَىٰ وَمَنۡ حَوۡلَهَا وَتُنذِرَ يَوۡمَ ٱلۡجَمۡعِ لَا رَيۡبَ فِيهِۚ فَرِيقٞ فِي ٱلۡجَنَّةِ وَفَرِيقٞ فِي ٱلسَّعِيرِ

Kuma kamar haka Muka yiwo maka wahayin Alqur’ani Balarabe, don ka gargaxi mutanen Makka da waxanda suke kewaye da ita (watau duniya baki xaya), ka kuma yi gargaxin ranar taruwa da babu kokwanto a game da ita. Wata qungiya tana cikin Aljanna, wata qungiya kuma tana cikin wutar Sa’ira



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 8

وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَجَعَلَهُمۡ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ وَلَٰكِن يُدۡخِلُ مَن يَشَآءُ فِي رَحۡمَتِهِۦۚ وَٱلظَّـٰلِمُونَ مَا لَهُم مِّن وَلِيّٖ وَلَا نَصِيرٍ

Da kuma Allah Ya ga dama da Ya sanya su al’umma xaya (watau a kan addini xaya), sai dai kuma Yana shigar da wanda Ya ga dama cikin rahamarsa. Azzalumai kuma ba su da wani majivinci ko wani mataimaki



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 9

أَمِ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ أَوۡلِيَآءَۖ فَٱللَّهُ هُوَ ٱلۡوَلِيُّ وَهُوَ يُحۡيِ ٱلۡمَوۡتَىٰ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Ko dai sun riqi wasu majivinta ne ba Shi ba. To Allah Shi ne Majivinci, Shi ne kuma Yake raya matattu, Shi kuma Mai iko ne a kan komai



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 10

وَمَا ٱخۡتَلَفۡتُمۡ فِيهِ مِن شَيۡءٖ فَحُكۡمُهُۥٓ إِلَى ٱللَّهِۚ ذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبِّي عَلَيۡهِ تَوَكَّلۡتُ وَإِلَيۡهِ أُنِيبُ

Kuma duk wani abu da kuka yi savani a kansa, to sai ku mai da hukuncinsa ga Allah. Wannan Shi ne Allah Ubangijina, gare Shi kawai na dogara, kuma wurinsa kawai nake mayar da al’amarina



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 11

فَاطِرُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ جَعَلَ لَكُم مِّنۡ أَنفُسِكُمۡ أَزۡوَٰجٗا وَمِنَ ٱلۡأَنۡعَٰمِ أَزۡوَٰجٗا يَذۡرَؤُكُمۡ فِيهِۚ لَيۡسَ كَمِثۡلِهِۦ شَيۡءٞۖ وَهُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡبَصِيرُ

(Shi ne) Mahaliccin sammai da qasa. Ya halitta muku mataye daga jinsinku, daga dabbobi ma (Ya halicce su) maza da mata; Yana yaxa ku ta hanyarsa (haxin jinsin biyu). Babu wani abu da ya yi kama da Shi[1]; kuma Shi Mai ji ne, Mai gani


1- Watau ba ya da mai kama da shi a Zatinsa da siffofinsa da sunayensa da ayyukansa.


Capítulo: Suratus Shura

Verso : 12

لَهُۥ مَقَالِيدُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ وَيَقۡدِرُۚ إِنَّهُۥ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Mabuxan taskokin sammai da qasa nasa ne; Yana shimfixa arziki ga wanda Ya ga dama, yana kuma quntatawa. Lalle shi Masanin komai ne



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 13

۞شَرَعَ لَكُم مِّنَ ٱلدِّينِ مَا وَصَّىٰ بِهِۦ نُوحٗا وَٱلَّذِيٓ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ وَمَا وَصَّيۡنَا بِهِۦٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَمُوسَىٰ وَعِيسَىٰٓۖ أَنۡ أَقِيمُواْ ٱلدِّينَ وَلَا تَتَفَرَّقُواْ فِيهِۚ كَبُرَ عَلَى ٱلۡمُشۡرِكِينَ مَا تَدۡعُوهُمۡ إِلَيۡهِۚ ٱللَّهُ يَجۡتَبِيٓ إِلَيۡهِ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِيٓ إِلَيۡهِ مَن يُنِيبُ

Ya shar’anta muku (irin) abin da Ya yi wa Nuhu wahayi da shi na addini, da kuma wanda Muka yiwo maka wahayinsa, da kuma abin da Muka yi wa Ibrahimu da Musa da Isa wasiyya da shi cewa: “Ku tsayar da addini, kuma kada ku rarraba a cikinsa.” Abin da kake kiran kafirai zuwa gare shi ya yi musu nauyi. Allah Yana zavar wanda Ya ga dama zuwa gare shi (addini) Yana kuma shiryar da wanda Ya mayar da al’amarinsa zuwa gare Shi



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 14

وَمَا تَفَرَّقُوٓاْ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَهُمُ ٱلۡعِلۡمُ بَغۡيَۢا بَيۡنَهُمۡۚ وَلَوۡلَا كَلِمَةٞ سَبَقَتۡ مِن رَّبِّكَ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗى لَّقُضِيَ بَيۡنَهُمۡۚ وَإِنَّ ٱلَّذِينَ أُورِثُواْ ٱلۡكِتَٰبَ مِنۢ بَعۡدِهِمۡ لَفِي شَكّٖ مِّنۡهُ مُرِيبٖ

Ba su kuma rarrabu ba sai bayan ilimi ya zo musu don zalunci da ke tsakaninsu. Ba don kalmar da ta riga ta gabata daga Ubangijinka ba (ta jinkirta musu) zuwa ga wani lokaci qayyadajje, da lalle an yi hukunci tsakaninsu. Kuma lalle waxanda aka gadar wa da littafi a bayansu lallai suna cikin shakka mai sa kokwanto game da shi (Annabi Muhammadu)



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 15

فَلِذَٰلِكَ فَٱدۡعُۖ وَٱسۡتَقِمۡ كَمَآ أُمِرۡتَۖ وَلَا تَتَّبِعۡ أَهۡوَآءَهُمۡۖ وَقُلۡ ءَامَنتُ بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ مِن كِتَٰبٖۖ وَأُمِرۡتُ لِأَعۡدِلَ بَيۡنَكُمُۖ ٱللَّهُ رَبُّنَا وَرَبُّكُمۡۖ لَنَآ أَعۡمَٰلُنَا وَلَكُمۡ أَعۡمَٰلُكُمۡۖ لَا حُجَّةَ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَكُمُۖ ٱللَّهُ يَجۡمَعُ بَيۡنَنَاۖ وَإِلَيۡهِ ٱلۡمَصِيرُ

Saboda wannan sai ka yi kira (zuwa ga addinin Allah), kuma ka tsaya kyam kamar yadda aka umarce ka, kada ka bi son ransu; ka kuma ce: “Na yi imani da abin da Allah Ya saukar na littattafai; an kuma umarce ni da yin adalci a tsakaninku; Allah ne Ubangijinmu kuma Ubangijinku; (sakamakon) ayyukanmu namu ne, ku ma (sakamakon) ayyukanku naku ne; babu wata jayayya a tsakaninmu da ku; Allah zai tara mu; kuma zuwa gare Shi ne kaxai makoma



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 16

وَٱلَّذِينَ يُحَآجُّونَ فِي ٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ مَا ٱسۡتُجِيبَ لَهُۥ حُجَّتُهُمۡ دَاحِضَةٌ عِندَ رَبِّهِمۡ وَعَلَيۡهِمۡ غَضَبٞ وَلَهُمۡ عَذَابٞ شَدِيدٌ

Waxanda kuma suke jayayya game da Allah bayan an amsa masa (kiransa), to hujjarsu vatacciya ce a wurin Ubangijinsu, kuma fushi ya hau kansu, kuma suna da azaba mai tsanani



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 17

ٱللَّهُ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ وَٱلۡمِيزَانَۗ وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّ ٱلسَّاعَةَ قَرِيبٞ

Allah ne Ya saukar da Littafi da gaskiya da kuma adalci. Me yake sanar da kai cewa ko alqiyama kusa take



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 18

يَسۡتَعۡجِلُ بِهَا ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِهَاۖ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مُشۡفِقُونَ مِنۡهَا وَيَعۡلَمُونَ أَنَّهَا ٱلۡحَقُّۗ أَلَآ إِنَّ ٱلَّذِينَ يُمَارُونَ فِي ٱلسَّاعَةِ لَفِي ضَلَٰلِۭ بَعِيدٍ

Waxanda ba sa yin imani da ita suna gaggauto da ita; waxanda kuwa suka yi imani a tsorace suke da ita, kuma suna sane da cewa ita gaskiya ce. Ku saurara, lalle waxanda suke jayayya game da tashin alqiyama tabbas suna cikin vata mai nisa



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 19

ٱللَّهُ لَطِيفُۢ بِعِبَادِهِۦ يَرۡزُقُ مَن يَشَآءُۖ وَهُوَ ٱلۡقَوِيُّ ٱلۡعَزِيزُ

Allah Mai tausasa wa bayinsa ne, Yana arzuta wanda ya ga dama; kuma Shi Qaqqarfa ne, Mabuwayi



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 20

مَن كَانَ يُرِيدُ حَرۡثَ ٱلۡأٓخِرَةِ نَزِدۡ لَهُۥ فِي حَرۡثِهِۦۖ وَمَن كَانَ يُرِيدُ حَرۡثَ ٱلدُّنۡيَا نُؤۡتِهِۦ مِنۡهَا وَمَا لَهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ مِن نَّصِيبٍ

Wanda ya kasance yana nufin ladan lahira to za Mu qara masa a kan ladansa; wanda kuwa ya kasance yana nufin ladan duniya to za Mu ba shi (wani abu) daga gare ta, kuma ba shi da wani rabo a lahira



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 21

أَمۡ لَهُمۡ شُرَكَـٰٓؤُاْ شَرَعُواْ لَهُم مِّنَ ٱلدِّينِ مَا لَمۡ يَأۡذَنۢ بِهِ ٱللَّهُۚ وَلَوۡلَا كَلِمَةُ ٱلۡفَصۡلِ لَقُضِيَ بَيۡنَهُمۡۗ وَإِنَّ ٱلظَّـٰلِمِينَ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Ko dai suna da wasu abokan tarayya ne da suka shar’anta musu wani abu na addini wanda Allah bai yi izinin yin sa ba? Ba don kalmar yin hukunci (a lahira) ta tabbata ba, da lalle an yi hukunci a tsakaninsu (tun a duniya). Lalle kuma azzalumai suna da azaba mai raxaxi



Capítulo: Suratus Shura

Verso : 22

تَرَى ٱلظَّـٰلِمِينَ مُشۡفِقِينَ مِمَّا كَسَبُواْ وَهُوَ وَاقِعُۢ بِهِمۡۗ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فِي رَوۡضَاتِ ٱلۡجَنَّاتِۖ لَهُم مَّا يَشَآءُونَ عِندَ رَبِّهِمۡۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَضۡلُ ٱلۡكَبِيرُ

Za ka ga azzalumai suna tsoron sakamakon abin da suka aikata, alhali kuwa ga shi zai faxa musu. Waxanda kuwa suka yi imani suka kuma yi aiki nagari, to suna cikin dausayoyin gidajen Aljanna; suna samun duk abin da suka ga dama a wurin Ubangijinsu. Wannan ita ce falala mai girma