Capítulo: Qadar

Verso : 4

تَنَزَّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ فِيهَا بِإِذۡنِ رَبِّهِم مِّن كُلِّ أَمۡرٖ

Mala’iku da Jibrilu suna ta saukowa da dukkanin al’amura a cikinsa da izinin Ubangijinsu



Capítulo: Qadar

Verso : 5

سَلَٰمٌ هِيَ حَتَّىٰ مَطۡلَعِ ٱلۡفَجۡرِ

Aminci ne shi (daren dukkansa) har zuwa hudowar alfijir



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 1

لَمۡ يَكُنِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ مُنفَكِّينَ حَتَّىٰ تَأۡتِيَهُمُ ٱلۡبَيِّنَةُ

Waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushirikai ba su zamanto masu barin abin da suke kai (na kafirci) ba har sai hujja bayyananniya ta zo musu



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 2

رَسُولٞ مِّنَ ٱللَّهِ يَتۡلُواْ صُحُفٗا مُّطَهَّرَةٗ

(Watau) Manzo daga Allah da zai riqa karanta (musu) takardu masu tsarki



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 3

فِيهَا كُتُبٞ قَيِّمَةٞ

(Waxanda) a cikinsu akwai hukunce-hukunce masu qima



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 4

وَمَا تَفَرَّقَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡهُمُ ٱلۡبَيِّنَةُ

Waxanda kuma aka bai wa littafi ba su rarraba ba[1] sai bayan da hujja bayyananniya ta zo musu


1- Watau Yahudawa da Nasara ba su rarrabu ba suka zama qungiya-qungiya wasu suka yi imani da Manzo Allah (), wasu kuma suka kafirce.


Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 5

وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ

Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 6

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ فِي نَارِ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ شَرُّ ٱلۡبَرِيَّةِ

Lalle waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushirikai suna cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta. Waxannan su ne mafiya sharrin halitta



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 7

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ خَيۡرُ ٱلۡبَرِيَّةِ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, waxannan su ne mafiya alherin halitta



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 8

جَزَآؤُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ رَّضِيَ ٱللَّهُ عَنۡهُمۡ وَرَضُواْ عَنۡهُۚ ذَٰلِكَ لِمَنۡ خَشِيَ رَبَّهُۥ

Sakamakonsu a wajen Ubangijinsu gidajen Aljanna ne na dawwama waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu suna madawwama a cikinsu har abada; Allah Ya yarda da su, su ma sun yarda da Shi. Wannan kuma (sakamako ne) ga wanda ya ji tsoron Ubangijinsa



Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 1

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta



Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 2

وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا

Qasar kuma ta fitar da nauyaye-nauyayenta[1]


1- Watau ta fitar da mutanen da ke cikinta da sauran ma’adanan qarqashinta.


Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 3

وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا

Mutum kuma ya ce: “Me ya same ta?”



Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 4

يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا

A wannan ranar ne za ta ba da labaranta[1]


1- Watau ayyukan da aka yi a kanta masu kyau da munana.


Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 5

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا

Don Ubangijinka Ya umarce ta (da yin haka)



Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 6

يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ

A wannan ranar mutane za su fito a warwatse, don a nuna musu ayyukansu



Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 7

فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ

To duk wanda ya yi aikin alheri daidai da zarra zai gan shi



Capítulo: Suratuz Zalzala

Verso : 8

وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ

Wanda kuma duk ya yi aikin sharri daidai da zarra zai gan shi



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 1

وَٱلۡعَٰدِيَٰتِ ضَبۡحٗا

Na rantse da (dawaki) masu sukuwa suna kukan ciki



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 2

فَٱلۡمُورِيَٰتِ قَدۡحٗا

Sannan masu bugun qyastu da kofatai[1]


1- Watau suna qyasta wuta da kofatansu idan suka daki duwatsu da su.


Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 3

فَٱلۡمُغِيرَٰتِ صُبۡحٗا

Sannan masu kai hari da asuba



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 4

فَأَثَرۡنَ بِهِۦ نَقۡعٗا

Sai suka tayar da qura da ita (sukawar tasu)



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 5

فَوَسَطۡنَ بِهِۦ جَمۡعًا

Sai kuma suka shiga tsakiyar taro (da mahayansu)



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 6

إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لِرَبِّهِۦ لَكَنُودٞ

Lalle mutum tabbas mai yawan butulci ne ga Ubangijinsa



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 7

وَإِنَّهُۥ عَلَىٰ ذَٰلِكَ لَشَهِيدٞ

Lalle kuma shi shaida ne a kan haka



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 8

وَإِنَّهُۥ لِحُبِّ ٱلۡخَيۡرِ لَشَدِيدٌ

Lalle shi kuma mai tsananin son alheri ne[1]


1- Watau yana da tsananin son dukiya, wannan ne kuma yake sanya shi rowa.


Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 9

۞أَفَلَا يَعۡلَمُ إِذَا بُعۡثِرَ مَا فِي ٱلۡقُبُورِ

Shin bai sani ba ne idan aka bankaxo abubuwan da suke cikin qaburbura?



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 10

وَحُصِّلَ مَا فِي ٱلصُّدُورِ

Aka kuma tattaro abubuwan da suke cikin qiraza?



Capítulo: Suratul Adiyat

Verso : 11

إِنَّ رَبَّهُم بِهِمۡ يَوۡمَئِذٖ لَّخَبِيرُۢ

Lalle a wannan ranar tabbas Ubangijinsu Masani ne game da su



Capítulo: Suratul Qari’a

Verso : 1

ٱلۡقَارِعَةُ

Mai qwanqwasa (zukata da tsoro)