Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 10

فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنِّي مَغۡلُوبٞ فَٱنتَصِرۡ

Sai ya roqi Ubangijinsa (cewa): “Lalle an fi qarfina, sai Ka taimaka.”



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 11

فَفَتَحۡنَآ أَبۡوَٰبَ ٱلسَّمَآءِ بِمَآءٖ مُّنۡهَمِرٖ

Sai Muka buxe qofofin sama da ruwa mai kwararowa



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 12

وَفَجَّرۡنَا ٱلۡأَرۡضَ عُيُونٗا فَٱلۡتَقَى ٱلۡمَآءُ عَلَىٰٓ أَمۡرٖ قَدۡ قُدِرَ

Muka kuma vuvvugar da idanuwan ruwa daga qasa, sai ruwayen suka haxu a bisa al’amarin da aka riga aka qaddara



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 13

وَحَمَلۡنَٰهُ عَلَىٰ ذَاتِ أَلۡوَٰحٖ وَدُسُرٖ

Muka kuma xauke shi a kan (jirgin ruwa) mai alluna da qusoshi



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 14

تَجۡرِي بِأَعۡيُنِنَا جَزَآءٗ لِّمَن كَانَ كُفِرَ

Yana gudu a kan idonmu, don ya zama sakayya ga wanda aka kafirce wa (watau Nuhu)



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 15

وَلَقَد تَّرَكۡنَٰهَآ ءَايَةٗ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun bar (abin da ya faru) ya zama aya, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 16

فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 17

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunasarwa da hadda, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 18

كَذَّبَتۡ عَادٞ فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

Adawa sun qaryata (Annabinsu), to qaqa azabata da gargaxina suka kasance?



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 19

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ رِيحٗا صَرۡصَرٗا فِي يَوۡمِ نَحۡسٖ مُّسۡتَمِرّٖ

Lalle Mu Mun aiko musu da iska mai qarfi a ranar shu’umci mai zarcewa



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 20

تَنزِعُ ٱلنَّاسَ كَأَنَّهُمۡ أَعۡجَازُ نَخۡلٖ مُّنقَعِرٖ

Tana tumvuko mutane[1] ta kayar su, kai ka ce su kututturan dabinai ne da aka tuttunvuke


1- Watau daga doron qasa ta yi sama da su sannan ta kifo da su ta kawunansu su faxo qasa a mace.


Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 21

فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 22

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Kuma haqiqa Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 23

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِٱلنُّذُرِ

Samudawa sun qaryata gargaxi



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 24

فَقَالُوٓاْ أَبَشَرٗا مِّنَّا وَٰحِدٗا نَّتَّبِعُهُۥٓ إِنَّآ إِذٗا لَّفِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٍ

Sannan suka ce: “Yanzu mutum xaya daga cikinmu ne za mu bi? To lalle idan mun yi haka, mun tabbata cikin vata da hauka



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 25

أَءُلۡقِيَ ٱلذِّكۡرُ عَلَيۡهِ مِنۢ بَيۡنِنَا بَلۡ هُوَ كَذَّابٌ أَشِرٞ

“Yanzu (zai yiwu) a saukar masa da wahayi a tsakaninmu? A’a, shi dai maqaryaci ne mai tsananin girman kai.”



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 26

سَيَعۡلَمُونَ غَدٗا مَّنِ ٱلۡكَذَّابُ ٱلۡأَشِرُ

A gobe lalle za su san wane ne maqaryacin mai girman kai



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 27

إِنَّا مُرۡسِلُواْ ٱلنَّاقَةِ فِتۡنَةٗ لَّهُمۡ فَٱرۡتَقِبۡهُمۡ وَٱصۡطَبِرۡ

Lalle Mu Masu aiko taguwa ne don ta zama fitina a gare su, saboda haka ka saurara musu, kuma ka jure



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 28

وَنَبِّئۡهُمۡ أَنَّ ٱلۡمَآءَ قِسۡمَةُۢ بَيۡنَهُمۡۖ كُلُّ شِرۡبٖ مُّحۡتَضَرٞ

Kuma ka ba su labarin cewa ruwan sha an raba ne tsakaninsu (da ita taguwar); kowane akwai ranar shansa



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 29

فَنَادَوۡاْ صَاحِبَهُمۡ فَتَعَاطَىٰ فَعَقَرَ

Sai suka kirawo (shaqiyin) abokin nasu sai ya xauki (abin sara) sai ya sare ta



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 30

فَكَيۡفَ كَانَ عَذَابِي وَنُذُرِ

To qaqa azabata da gargaxina suka kasance?



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 31

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ فَكَانُواْ كَهَشِيمِ ٱلۡمُحۡتَظِرِ

Lalle Mun aika musu da tsawa guda xaya, sai suka zamo kamar duddugar ciyawa a garken makiyayi



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 32

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 33

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطِۭ بِٱلنُّذُرِ

Mutanen Luxu sun qaryata gargaxi



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 34

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ حَاصِبًا إِلَّآ ءَالَ لُوطٖۖ نَّجَّيۡنَٰهُم بِسَحَرٖ

Lalle Mun aika musu da iska cike da duwatsu (ta hallaka su), sai dai iyalin Luxu kaxai Muka tserar da su a lokacin asuba



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 35

نِّعۡمَةٗ مِّنۡ عِندِنَاۚ كَذَٰلِكَ نَجۡزِي مَن شَكَرَ

(Wannan) ni’ima ce daga wurinmu. Kamar haka Muke saka wa wanda ya yi godiya



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 36

وَلَقَدۡ أَنذَرَهُم بَطۡشَتَنَا فَتَمَارَوۡاْ بِٱلنُّذُرِ

Kuma haqiqa ya tsoratar da su irin damqarmu, sai suka yi jayayya da gargaxin (da ya yi musu)



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 37

وَلَقَدۡ رَٰوَدُوهُ عَن ضَيۡفِهِۦ فَطَمَسۡنَآ أَعۡيُنَهُمۡ فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ

Haqiqa kuma sun nemi baqinsa[1] da lalata, sai Muka shafe idanuwansu, (Muka ce da su): “Sai ku xanxani azabata da gargaxina.


1- Su ne mala’iku da suka zo masa a siffar mutane matasa kyawawa.


Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 38

وَلَقَدۡ صَبَّحَهُم بُكۡرَةً عَذَابٞ مُّسۡتَقِرّٞ

Haqiqa kuma azaba matabbaciya ta yi musu sammako da asuba.



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 39

فَذُوقُواْ عَذَابِي وَنُذُرِ

Saboda haka ku xanxani azabata da gargaxina.”