Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 25

كَذَّبَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ فَأَتَىٰهُمُ ٱلۡعَذَابُ مِنۡ حَيۡثُ لَا يَشۡعُرُونَ

Waxanda suke gabaninsu sun qaryata, sai azaba ta zo musu daga inda ba sa tsammani



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 26

فَأَذَاقَهُمُ ٱللَّهُ ٱلۡخِزۡيَ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَكۡبَرُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Sannan Allah Ya xanxana musu azabar wulaqanci a rayuwar duniya, kuma lalle azabar lahira ta fi girma. Da sun kasance sun san (hakan)



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 27

وَلَقَدۡ ضَرَبۡنَا لِلنَّاسِ فِي هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ مِن كُلِّ مَثَلٖ لَّعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ

Kuma haqiqa Mun ba wa mutane kowane nau’i na misali a cikin wannan Alqur’ani don su wa’azantu



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 28

قُرۡءَانًا عَرَبِيًّا غَيۡرَ ذِي عِوَجٖ لَّعَلَّهُمۡ يَتَّقُونَ

Alqur’ani Balarabe marar karkata don su sami taqawa



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 29

ضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا رَّجُلٗا فِيهِ شُرَكَآءُ مُتَشَٰكِسُونَ وَرَجُلٗا سَلَمٗا لِّرَجُلٍ هَلۡ يَسۡتَوِيَانِ مَثَلًاۚ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِۚ بَلۡ أَكۡثَرُهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ

Allah Ya ba da misali na wani namiji (bawa) wanda yake da iyayen giji masu tarayya a kansa masu jayayya (a kan ba shi umarni) da kuma wani namiiji (bawa) da ya kevanta ga wani namiji guda, shin misalinsu za su yi daidai? Dukkan yabo ya tabbata ga Allah. A’a, yawancinsu dai ba su sani ba ne



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 30

إِنَّكَ مَيِّتٞ وَإِنَّهُم مَّيِّتُونَ

Lalle kai mai mutuwa ne, su ma kuma lalle masu mutuwa ne



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 31

ثُمَّ إِنَّكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ عِندَ رَبِّكُمۡ تَخۡتَصِمُونَ

Sannan kuma lalle ku xin nan a ranar alqiyama a wurin Ubangijinku za ku yi husuma