Capítulo: Suratu Sad

Verso : 23

إِنَّ هَٰذَآ أَخِي لَهُۥ تِسۡعٞ وَتِسۡعُونَ نَعۡجَةٗ وَلِيَ نَعۡجَةٞ وَٰحِدَةٞ فَقَالَ أَكۡفِلۡنِيهَا وَعَزَّنِي فِي ٱلۡخِطَابِ

“Lalle wannan xan’uwana ne yana da awaki guda casa’in da tara, ni kuma ina da akuya guda xaya, sai ya ce: ‘Ka ba ni ita;’ ya kuma rinjaye ni game da maganar.”



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 24

قَالَ لَقَدۡ ظَلَمَكَ بِسُؤَالِ نَعۡجَتِكَ إِلَىٰ نِعَاجِهِۦۖ وَإِنَّ كَثِيرٗا مِّنَ ٱلۡخُلَطَآءِ لَيَبۡغِي بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٍ إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَقَلِيلٞ مَّا هُمۡۗ وَظَنَّ دَاوُۥدُ أَنَّمَا فَتَنَّـٰهُ فَٱسۡتَغۡفَرَ رَبَّهُۥ وَخَرَّۤ رَاكِعٗاۤ وَأَنَابَ۩

(Dawuda) Ya ce: “Haqiqa ya zalunce ka saboda neman haxe akuyarka cikin awakinsa; kuma lalle yawancin masu haxa dukiyarsu tabbas wasunsu suna zaluntar wasu, sai fa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, su kuwa kaxan ne qwarai. Sai kuma Dawuda ya tabbata cewa Mun jarraba shi ne, sai ya nemi gafarar Ubangijinsa, ya kuma faxi yana sujjada kuma ya koma (ga Allah)



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 25

فَغَفَرۡنَا لَهُۥ ذَٰلِكَۖ وَإِنَّ لَهُۥ عِندَنَا لَزُلۡفَىٰ وَحُسۡنَ مَـَٔابٖ

Sai Muka gafarta masa wannan; lalle kuma yana da kusanci da Mu da kuma kyakkyawar makoma



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 26

يَٰدَاوُۥدُ إِنَّا جَعَلۡنَٰكَ خَلِيفَةٗ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَٱحۡكُم بَيۡنَ ٱلنَّاسِ بِٱلۡحَقِّ وَلَا تَتَّبِعِ ٱلۡهَوَىٰ فَيُضِلَّكَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ يَضِلُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ لَهُمۡ عَذَابٞ شَدِيدُۢ بِمَا نَسُواْ يَوۡمَ ٱلۡحِسَابِ

Ya Dawuda, lalle Mun sanya ka halifa a bayan qasa, sai ka yi hukunci a tsakanin mutane da gaskiya, kada ka bi son zuciya sai ya vatar da kai daga hanyar Allah. Lalle waxanda suke vacewa daga hanyar Allah suna da (sakamakon) azaba mai tsanani saboda mantawar da suka yi da ranar hisabi



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 27

وَمَا خَلَقۡنَا ٱلسَّمَآءَ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا بَٰطِلٗاۚ ذَٰلِكَ ظَنُّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۚ فَوَيۡلٞ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنَ ٱلنَّارِ

Kuma ba Mu halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu a banza ba. Wannan zato ne na waxanda suka kafirta. Saboda haka tsananin azabar wuta ya tabbata ga waxanda suka kafirce



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 28

أَمۡ نَجۡعَلُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ كَٱلۡمُفۡسِدِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِ أَمۡ نَجۡعَلُ ٱلۡمُتَّقِينَ كَٱلۡفُجَّارِ

Shin za Mu mayar da waxanda suka yi imani suka yi ayyuka nagari kamar masu varna a bayan qasa, ko kuma za Mu mayar da masu taqawa kamar lalatattu?



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 29

كِتَٰبٌ أَنزَلۡنَٰهُ إِلَيۡكَ مُبَٰرَكٞ لِّيَدَّبَّرُوٓاْ ءَايَٰتِهِۦ وَلِيَتَذَكَّرَ أُوْلُواْ ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Littafi ne mai albarka da Muka saukar maka da shi domin su yi tuntuntuni game da ayoyinsa, don kuma masu hankula su wa’azantu



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 30

وَوَهَبۡنَا لِدَاوُۥدَ سُلَيۡمَٰنَۚ نِعۡمَ ٱلۡعَبۡدُ إِنَّهُۥٓ أَوَّابٌ

Muka kuma yi wa Dawuda baiwar (xa) Sulaimanu. Madalla da wannan bawan; lalle shi mai yawan komawa ne (ga Allah)



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 31

إِذۡ عُرِضَ عَلَيۡهِ بِٱلۡعَشِيِّ ٱلصَّـٰفِنَٰتُ ٱلۡجِيَادُ

(Ka tuna) lokacin da aka jera masa ingarmun dawakai masu tsayawa da qafa uku da yamma



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 32

فَقَالَ إِنِّيٓ أَحۡبَبۡتُ حُبَّ ٱلۡخَيۡرِ عَن ذِكۡرِ رَبِّي حَتَّىٰ تَوَارَتۡ بِٱلۡحِجَابِ

Sai ya ce: “Lalle ni na fifita son dukiya (watau dawakai) a kan ambaton Ubangijina (watau sallar La’asar) har sai da (rana) ta faxi.”



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 33

رُدُّوهَا عَلَيَّۖ فَطَفِقَ مَسۡحَۢا بِٱلسُّوقِ وَٱلۡأَعۡنَاقِ

(Ya ce): “Ku dawo min da su;” sai ya riqa saran su ta qafafu da wuyoyi



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 34

وَلَقَدۡ فَتَنَّا سُلَيۡمَٰنَ وَأَلۡقَيۡنَا عَلَىٰ كُرۡسِيِّهِۦ جَسَدٗا ثُمَّ أَنَابَ

Kuma haqiqa Mun jarrabi Sulaimanu Muka xora wani jiki a kan gadonsa na mulki[1], sannan ya koma (kan mulkinsa)


1- Wannan wata jarrrabawa ce da Allah ya yi wa Annabi Sulaimanu () game da mulkinsa, lokacin da ya xora wani jiki a kan kujerarsa ta mulki. Mafi yawan malamai sun ce wani shaixani ne Allah ya ba shi ikon hayewa kujerarsa.


Capítulo: Suratu Sad

Verso : 35

قَالَ رَبِّ ٱغۡفِرۡ لِي وَهَبۡ لِي مُلۡكٗا لَّا يَنۢبَغِي لِأَحَدٖ مِّنۢ بَعۡدِيٓۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡوَهَّابُ

Ya ce: “Ya Ubangijina, Ka gafarta min, Ka kuma ba ni wani mulki wanda bai kamaci wani ba a bayana ya sami irinsa; lalle Kai Kai ne Mai yawan kyauta.”



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 36

فَسَخَّرۡنَا لَهُ ٱلرِّيحَ تَجۡرِي بِأَمۡرِهِۦ رُخَآءً حَيۡثُ أَصَابَ

Sai Muka hore masa iska tana tafiya da umarninsa a natse duk inda ya fuskanta



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 37

وَٱلشَّيَٰطِينَ كُلَّ بَنَّآءٖ وَغَوَّاصٖ

Da kuma shaixanu masu yin kowane irin gini da kuma masu yin nutso (a ruwa)



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 38

وَءَاخَرِينَ مُقَرَّنِينَ فِي ٱلۡأَصۡفَادِ

Wasu kuma an xaxxaure su cikin maruruwa



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 39

هَٰذَا عَطَآؤُنَا فَٱمۡنُنۡ أَوۡ أَمۡسِكۡ بِغَيۡرِ حِسَابٖ

Wannan kyautarmu ce, to ka yi kyauta ko ka hana ba da wani bincike ba



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 40

وَإِنَّ لَهُۥ عِندَنَا لَزُلۡفَىٰ وَحُسۡنَ مَـَٔابٖ

Lalle kuma shi tabbas yana da kusanci a wurinmu, da kuma kyakkyawar makoma



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 41

وَٱذۡكُرۡ عَبۡدَنَآ أَيُّوبَ إِذۡ نَادَىٰ رَبَّهُۥٓ أَنِّي مَسَّنِيَ ٱلشَّيۡطَٰنُ بِنُصۡبٖ وَعَذَابٍ

Ka kuma tuna bawanmu Ayyuba lokacin da ya kira Ubangijinsa (yana cewa): “Lalle ni Shaixan ya shafe ni da wata wahala da azaba.”



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 42

ٱرۡكُضۡ بِرِجۡلِكَۖ هَٰذَا مُغۡتَسَلُۢ بَارِدٞ وَشَرَابٞ

(Aka ce da shi): “Ka hauri qasa da qafarka; (sai ruwa ya vuvvugo, aka ce da shi): “Wannan ruwan wanka ne mai sanyi da na sha.”



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 43

وَوَهَبۡنَا لَهُۥٓ أَهۡلَهُۥ وَمِثۡلَهُم مَّعَهُمۡ رَحۡمَةٗ مِّنَّا وَذِكۡرَىٰ لِأُوْلِي ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Muka kuma yi masa baiwar iyalinsa da kuma (qarin) wasu kamarsu (na `ya`ya da jikoki) don jin qai daga gare Mu da kuma wa’azi ga masu hankula



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 44

وَخُذۡ بِيَدِكَ ضِغۡثٗا فَٱضۡرِب بِّهِۦ وَلَا تَحۡنَثۡۗ إِنَّا وَجَدۡنَٰهُ صَابِرٗاۚ نِّعۡمَ ٱلۡعَبۡدُ إِنَّهُۥٓ أَوَّابٞ

Ka xauki danqi na ciyawa da hannunka ka bugi (matarka da shi)[1], kada ka karya rantsuwarka. Lalle Mun same shi mai haquri. Madalla da wannan bawan; lalle shi mai yawan komawa ne (ga Allah)


1- Yayin da matarsa ta yi masa laifi ya yi rantsuwa cewa, idan ya warke sai ya yi mata bulala xari. Allah () ya umarce shi da ya cika rantsuwarsa ta wannan hanyar.


Capítulo: Suratu Sad

Verso : 45

وَٱذۡكُرۡ عِبَٰدَنَآ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ أُوْلِي ٱلۡأَيۡدِي وَٱلۡأَبۡصَٰرِ

Ka kuma tuna bayinmu Ibrahimu da Is’haqa da Yaqubu ma’abota qarfi da basira



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 46

إِنَّآ أَخۡلَصۡنَٰهُم بِخَالِصَةٖ ذِكۡرَى ٱلدَّارِ

Lalle Mun kevance su da wata kevantacciyar xabi’a, (ita ce) tuna lahira



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 47

وَإِنَّهُمۡ عِندَنَا لَمِنَ ٱلۡمُصۡطَفَيۡنَ ٱلۡأَخۡيَارِ

Kuma lalle su a wurinmu tabbas suna daga cikin zavavvu nagari



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 48

وَٱذۡكُرۡ إِسۡمَٰعِيلَ وَٱلۡيَسَعَ وَذَا ٱلۡكِفۡلِۖ وَكُلّٞ مِّنَ ٱلۡأَخۡيَارِ

Ka kuma tuna Isma’ila da Alyasa’u da Zulkifli; dukkaninsu kuma suna cikin zavavvu



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 49

هَٰذَا ذِكۡرٞۚ وَإِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ لَحُسۡنَ مَـَٔابٖ

Wannan kyakkyawan ambato ne (a gare su). Kuma lalle masu taqawa tabbas suna da kyakkyawar makoma



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 50

جَنَّـٰتِ عَدۡنٖ مُّفَتَّحَةٗ لَّهُمُ ٱلۡأَبۡوَٰبُ

(Wato) gidajen Aljannar dawwama, alhali qofofi suna buxe saboda su



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 51

مُتَّكِـِٔينَ فِيهَا يَدۡعُونَ فِيهَا بِفَٰكِهَةٖ كَثِيرَةٖ وَشَرَابٖ

Suna kishingixe a cikinsu, suna kiran a kawo musu ababen marmari masu yawa da abin sha a cikinsu



Capítulo: Suratu Sad

Verso : 52

۞وَعِندَهُمۡ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ أَتۡرَابٌ

Kuma a wurinsu akwai tsaraikun mata masu taqaita kallo (ga mazansu kawai)