Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 62

ٱللَّهُ خَٰلِقُ كُلِّ شَيۡءٖۖ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ وَكِيلٞ

Allah ne Mahaliccin komai; kuma Shi ne Wakili a kan komai



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 63

لَّهُۥ مَقَالِيدُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۗ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Mabuxan sammai da qasa nasa ne. Waxanda kuwa suka kafirce wa ayoyin Allah, waxannan su ne asararru



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 64

قُلۡ أَفَغَيۡرَ ٱللَّهِ تَأۡمُرُوٓنِّيٓ أَعۡبُدُ أَيُّهَا ٱلۡجَٰهِلُونَ

Ka ce: “Yanzu wanin Allah kuke umarta ta da in bauta wa, ya ku waxannan wawaye?”



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 65

وَلَقَدۡ أُوحِيَ إِلَيۡكَ وَإِلَى ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِكَ لَئِنۡ أَشۡرَكۡتَ لَيَحۡبَطَنَّ عَمَلُكَ وَلَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡخَٰسِرِينَ

Haqiqa kuma an yi maka wahayi kai da waxanda suka gabace ka cewa: “Tabbas idan ka yi shirka lallai aikinka zai vaci, kuma tabbas za ka kasance daga asararru.”



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 66

بَلِ ٱللَّهَ فَٱعۡبُدۡ وَكُن مِّنَ ٱلشَّـٰكِرِينَ

A’a, Allah kaxai za ka bauta wa, ka kuma kasance daga masu godiya



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 67

وَمَا قَدَرُواْ ٱللَّهَ حَقَّ قَدۡرِهِۦ وَٱلۡأَرۡضُ جَمِيعٗا قَبۡضَتُهُۥ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ وَٱلسَّمَٰوَٰتُ مَطۡوِيَّـٰتُۢ بِيَمِينِهِۦۚ سُبۡحَٰنَهُۥ وَتَعَٰلَىٰ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Ba su kuma girmama Allah ba kamar yadda Ya cancanta a girmama Shi, alhali qasa ga baki xayanta tana cikin Damqarsa ranar alqiyama, sammai kuma suna nannaxe a Hannunsa na dama. Tsarki ya tabbata a gare Shi, Ya kuma xaukaka game da abin da suke yin shirka (da shi)



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 68

وَنُفِخَ فِي ٱلصُّورِ فَصَعِقَ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ إِلَّا مَن شَآءَ ٱللَّهُۖ ثُمَّ نُفِخَ فِيهِ أُخۡرَىٰ فَإِذَا هُمۡ قِيَامٞ يَنظُرُونَ

Aka kuma busa qaho, sai duk abin da yake cikin sammai da qasa ya halaka sai wanda Allah Ya ga dama; sannan aka sake yin wata busar, sai ga su a tsaye suna jiran tsammani



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 69

وَأَشۡرَقَتِ ٱلۡأَرۡضُ بِنُورِ رَبِّهَا وَوُضِعَ ٱلۡكِتَٰبُ وَجِاْيٓءَ بِٱلنَّبِيِّـۧنَ وَٱلشُّهَدَآءِ وَقُضِيَ بَيۡنَهُم بِٱلۡحَقِّ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Qasa kuma ta yi haske da hasken Ubangijinta, aka kuma ajiye takardu (na ayyuka), kuma aka zo da annabawa da masu shaida, kuma aka yi hukunci a tsakaninsu da gaskiya, ba kuma za a zalunce su ba



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 70

وَوُفِّيَتۡ كُلُّ نَفۡسٖ مَّا عَمِلَتۡ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِمَا يَفۡعَلُونَ

Aka kuma yi wa kowane rai cikakken sakamakon abin da ya aikata, Shi ko (Allah) Yana sane da abin da suke aikatawa



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 71

وَسِيقَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِلَىٰ جَهَنَّمَ زُمَرًاۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءُوهَا فُتِحَتۡ أَبۡوَٰبُهَا وَقَالَ لَهُمۡ خَزَنَتُهَآ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ رُسُلٞ مِّنكُمۡ يَتۡلُونَ عَلَيۡكُمۡ ءَايَٰتِ رَبِّكُمۡ وَيُنذِرُونَكُمۡ لِقَآءَ يَوۡمِكُمۡ هَٰذَاۚ قَالُواْ بَلَىٰ وَلَٰكِنۡ حَقَّتۡ كَلِمَةُ ٱلۡعَذَابِ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Aka kuma ingiza qeyar waxanda suka kafirta zuwa (wutar) Jahannama qungiya-qungiya; har yayin da suka zo wurinta sai aka buxe qofofinta, masu tsaronta suka ce (da su): “Yanzu manzanni daga cikinku ba su zo muku ba ne suna karanta muku ayoyin Ubangijinku, suna kuma gargaxin ku game da haxuwa da wannan ranar taku?” Sai suka ce: “Haka ne, (sun zo mana),” sai dai kuma kalmar azaba ta tabbata a kan kafirai.”



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 72

قِيلَ ٱدۡخُلُوٓاْ أَبۡوَٰبَ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَاۖ فَبِئۡسَ مَثۡوَى ٱلۡمُتَكَبِّرِينَ

Aka ce: “Ku shiga qofofin Jahannama, kuna masu dawwama a cikinta;” to makomar masu girman kai ta munana



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 73

وَسِيقَ ٱلَّذِينَ ٱتَّقَوۡاْ رَبَّهُمۡ إِلَى ٱلۡجَنَّةِ زُمَرًاۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءُوهَا وَفُتِحَتۡ أَبۡوَٰبُهَا وَقَالَ لَهُمۡ خَزَنَتُهَا سَلَٰمٌ عَلَيۡكُمۡ طِبۡتُمۡ فَٱدۡخُلُوهَا خَٰلِدِينَ

Aka kuma raka waxanda suka kiyaye dokokin Ubangijinsu zuwa Aljanna qungiya-qungiya; har yayin da suka zo wurinta, alhali an bubbuxe qofofinta, kuma masu tsaronta suka ce (da su): “Aminci ya tabbata a gare ku, kun kyautata (ayyukanku), sai ku shige ta kuna masu dawwama.”



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 74

وَقَالُواْ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي صَدَقَنَا وَعۡدَهُۥ وَأَوۡرَثَنَا ٱلۡأَرۡضَ نَتَبَوَّأُ مِنَ ٱلۡجَنَّةِ حَيۡثُ نَشَآءُۖ فَنِعۡمَ أَجۡرُ ٱلۡعَٰمِلِينَ

Suka ce: “Mun gode wa Allah Wanda Ya tabbatar mana da alqawarinsa, Ya kuma gadar mana da qasa muna sauka a Aljanna a duk inda muka ga dama; to madalla da sakamakon masu aiki!”



Capítulo: Suratuz Zumar

Verso : 75

وَتَرَى ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ حَآفِّينَ مِنۡ حَوۡلِ ٱلۡعَرۡشِ يُسَبِّحُونَ بِحَمۡدِ رَبِّهِمۡۚ وَقُضِيَ بَيۡنَهُم بِٱلۡحَقِّۚ وَقِيلَ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma za ka ga mala’iku suna kewaye da Al’arshi, suna tasbihi da yabon Ubangijnsu; aka kuma yi hukunci a tsakaninsu (halittu) da gaskiya, aka kuma ce: “Yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai.”



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 1

حمٓ

HA MIM



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 2

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡعَلِيمِ

Saukarwar Littafi daga Allah ne Mabuwayi, Masani



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 3

غَافِرِ ٱلذَّنۢبِ وَقَابِلِ ٱلتَّوۡبِ شَدِيدِ ٱلۡعِقَابِ ذِي ٱلطَّوۡلِۖ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ إِلَيۡهِ ٱلۡمَصِيرُ

Mai gafarta zunubi, Mai kuma karvar tuba, Mai tsananin uquba, Mai ni’imatarwa; babu abin bauta wa da gaskiya sai Shi; makoma zuwa gare Shi ne



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 4

مَا يُجَٰدِلُ فِيٓ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ إِلَّا ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَلَا يَغۡرُرۡكَ تَقَلُّبُهُمۡ فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Babu mai yin jayayya game da ayoyin Allah sai waxanda suka kafirta, saboda haka kada yawan zirga-zirgarsu a garuruwa ya ruxe ka



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 5

كَذَّبَتۡ قَبۡلَهُمۡ قَوۡمُ نُوحٖ وَٱلۡأَحۡزَابُ مِنۢ بَعۡدِهِمۡۖ وَهَمَّتۡ كُلُّ أُمَّةِۭ بِرَسُولِهِمۡ لِيَأۡخُذُوهُۖ وَجَٰدَلُواْ بِٱلۡبَٰطِلِ لِيُدۡحِضُواْ بِهِ ٱلۡحَقَّ فَأَخَذۡتُهُمۡۖ فَكَيۡفَ كَانَ عِقَابِ

Mutanen Nuhu sun qaryata kafin su, da kuma qungiyoyi (na kafirai) bayansu; kowace al’umma kuma sun yi mummunan nufi da manzonsu don su kama shi (su cutar da shi); suka kuma yi jayayya da (hujja ta) qarya don su rusa gaskiya da ita, sai Na kama su; to yaya uqubata ta kasance?



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 6

وَكَذَٰلِكَ حَقَّتۡ كَلِمَتُ رَبِّكَ عَلَى ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَنَّهُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِ

Kamar haka ne kuma kalmar Ubangijinka (ta azaba) ta tabbata a kan waxanda suka kafirta cewa, lalle su ‘yan wuta ne



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 7

ٱلَّذِينَ يَحۡمِلُونَ ٱلۡعَرۡشَ وَمَنۡ حَوۡلَهُۥ يُسَبِّحُونَ بِحَمۡدِ رَبِّهِمۡ وَيُؤۡمِنُونَ بِهِۦ وَيَسۡتَغۡفِرُونَ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْۖ رَبَّنَا وَسِعۡتَ كُلَّ شَيۡءٖ رَّحۡمَةٗ وَعِلۡمٗا فَٱغۡفِرۡ لِلَّذِينَ تَابُواْ وَٱتَّبَعُواْ سَبِيلَكَ وَقِهِمۡ عَذَابَ ٱلۡجَحِيمِ

Waxanda suke xauke da Al’arshi da waxanda suke kewaye da shi suna yin tasbihi da yabon Ubangijinsu, suna kuma yin imani da Shi, kuma suna nema wa waxanda suka yi imani gafara, (suna cewa): “Ya Ubangiijnmu, ka yalwaci kowane abu da rahama da ilimi, to Ka gafarta wa waxanda suka tuba suka kuma bi hanyarka, Ka kuma kiyaye su daga azabar (wutar) Jahimu



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 8

رَبَّنَا وَأَدۡخِلۡهُمۡ جَنَّـٰتِ عَدۡنٍ ٱلَّتِي وَعَدتَّهُمۡ وَمَن صَلَحَ مِنۡ ءَابَآئِهِمۡ وَأَزۡوَٰجِهِمۡ وَذُرِّيَّـٰتِهِمۡۚ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

“Ya Ubangijinmu, Ka kuma shigar da su gidajen Aljannar zama waxanda ka alqawarta musu, tare da waxanda suke salihai daga iyayensu da matayensu da kuma zuriyarsu. Lalle Kai Mabuwayi ne, Mai hikima



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 9

وَقِهِمُ ٱلسَّيِّـَٔاتِۚ وَمَن تَقِ ٱلسَّيِّـَٔاتِ يَوۡمَئِذٖ فَقَدۡ رَحِمۡتَهُۥۚ وَذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

“Ka kuma kiyaye su munanan (ayyuka). Duk kuwa wanda Ka kiyaye shi daga munanan (sakamako) a wannan rana, haqiqa Ka yi masa rahama. Wannan kuwa shi ne babban rabo.”



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُنَادَوۡنَ لَمَقۡتُ ٱللَّهِ أَكۡبَرُ مِن مَّقۡتِكُمۡ أَنفُسَكُمۡ إِذۡ تُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلۡإِيمَٰنِ فَتَكۡفُرُونَ

Lalle waxanda suka kafirta ana kiran su cewa: “Tabbas fushin Allah da ku ya fi girman fushinku ga kawunanku, lokacin da ake kiran ku zuwa imani (a duniya) sai kuke kafircewa.”



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 11

قَالُواْ رَبَّنَآ أَمَتَّنَا ٱثۡنَتَيۡنِ وَأَحۡيَيۡتَنَا ٱثۡنَتَيۡنِ فَٱعۡتَرَفۡنَا بِذُنُوبِنَا فَهَلۡ إِلَىٰ خُرُوجٖ مِّن سَبِيلٖ

Suka ce: “Ya Ubangijinmu, Ka kashe mu sau biyu Ka kuma raya mu sau biyu[1], to mun amsa laifukanmu, shin ko akwai wata hanya ta fita (daga wuta)?”


1- Watau ya samar da su bayan babu su, sannan ya kashe su, sannan ya sake raya su domin yi musu hisabi.


Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 12

ذَٰلِكُم بِأَنَّهُۥٓ إِذَا دُعِيَ ٱللَّهُ وَحۡدَهُۥ كَفَرۡتُمۡ وَإِن يُشۡرَكۡ بِهِۦ تُؤۡمِنُواْۚ فَٱلۡحُكۡمُ لِلَّهِ ٱلۡعَلِيِّ ٱلۡكَبِيرِ

Wannan (sakamakon) saboda cewa, idan aka kira Allah Shi kaxai sai ku kafirce, idan kuwa aka yi shirka da Shi, sai ku yi imani. To hukuncin na Allah ne Maxaukaki, Mai girma



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 13

هُوَ ٱلَّذِي يُرِيكُمۡ ءَايَٰتِهِۦ وَيُنَزِّلُ لَكُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ رِزۡقٗاۚ وَمَا يَتَذَكَّرُ إِلَّا مَن يُنِيبُ

Shi ne wanda Yake nuna muku ayoyinsa, Yake kuma saukar muku da arziki daga sama (watau ruwan sama). Ba kuma kowa ne yake wa’azantuwa ba sai mai komawa (ga Allah)



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 14

فَٱدۡعُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ وَلَوۡ كَرِهَ ٱلۡكَٰفِرُونَ

Sai ku bauta wa Allah kuna masu tsantsanta addini gare Shi, ko da kuwa kafirai ba sa so



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 15

رَفِيعُ ٱلدَّرَجَٰتِ ذُو ٱلۡعَرۡشِ يُلۡقِي ٱلرُّوحَ مِنۡ أَمۡرِهِۦ عَلَىٰ مَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦ لِيُنذِرَ يَوۡمَ ٱلتَّلَاقِ

(Shi ne) Mai maxaukakan darajoji, Ma’abocin Al’arshi, Yana sauko da wahayi daga umarninsa ga wanda Ya ga dama daga bayinsa don Ya yi gargaxin ranar haxuwa



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 16

يَوۡمَ هُم بَٰرِزُونَۖ لَا يَخۡفَىٰ عَلَى ٱللَّهِ مِنۡهُمۡ شَيۡءٞۚ لِّمَنِ ٱلۡمُلۡكُ ٱلۡيَوۡمَۖ لِلَّهِ ٱلۡوَٰحِدِ ٱلۡقَهَّارِ

Ranar da za su bayyana; babu wani abu nasu da zai vuya ga Allah. (Zai ce): “Mulki na wane ne a yau?” (Sai Ya ce): “Na Allah Makaxaici, Mai rinjaye ne.”