أَلَمۡ يَرَوۡاْ أَنَّا جَعَلۡنَا ٱلَّيۡلَ لِيَسۡكُنُواْ فِيهِ وَٱلنَّهَارَ مُبۡصِرًاۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ
Yanzu ba sa gani cewa Mu Muka samar da dare don su nutsu a cikinsa, da kuma rana mai haskakawa (don su yi harka)? Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutanen da suke yin imani
وَيَوۡمَ يُنفَخُ فِي ٱلصُّورِ فَفَزِعَ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ إِلَّا مَن شَآءَ ٱللَّهُۚ وَكُلٌّ أَتَوۡهُ دَٰخِرِينَ
(Ka tuna) kuma ranar da za a busa qaho sai duk mahaluqin da yake cikin sammai da qasa ya firgita, sai dai wanda Allah Ya toge. Kuma gaba xayansu za su zo masa suna masu miqa wuya
وَتَرَى ٱلۡجِبَالَ تَحۡسَبُهَا جَامِدَةٗ وَهِيَ تَمُرُّ مَرَّ ٱلسَّحَابِۚ صُنۡعَ ٱللَّهِ ٱلَّذِيٓ أَتۡقَنَ كُلَّ شَيۡءٍۚ إِنَّهُۥ خَبِيرُۢ بِمَا تَفۡعَلُونَ
Kuma za ka ga duwatsu ka zaci a tsaye suke cak, alhali kuwa su suna tafiya ne irin tafiyar gizagizai. Aikin Allah kenan wanda Ya kyautata halittar kowane irin abu. Lalle Shi Masanin abin da kuke aikatawa ne
مَن جَآءَ بِٱلۡحَسَنَةِ فَلَهُۥ خَيۡرٞ مِّنۡهَا وَهُم مِّن فَزَعٖ يَوۡمَئِذٍ ءَامِنُونَ
Duk waxanda suka zo da kyakkyawan (aiki), to suna da (lada) fiye da shi, kuma su amintattu ne daga firgitar wannan ranar
وَمَن جَآءَ بِٱلسَّيِّئَةِ فَكُبَّتۡ وُجُوهُهُمۡ فِي ٱلنَّارِ هَلۡ تُجۡزَوۡنَ إِلَّا مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ
Waxanda kuwa suka zo da mummunan (aiki), to an kifar da fuskokinsu cikin wuta, to ba za a saka muku ba sai da irin abin da kuka zamanto kuna aikatawa
إِنَّمَآ أُمِرۡتُ أَنۡ أَعۡبُدَ رَبَّ هَٰذِهِ ٱلۡبَلۡدَةِ ٱلَّذِي حَرَّمَهَا وَلَهُۥ كُلُّ شَيۡءٖۖ وَأُمِرۡتُ أَنۡ أَكُونَ مِنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ
(Ka ce da su): “Ni dai an umarce ni ne kawai da in bauta wa Ubangijin wannan garin (Makka) wanda Ya mayar da shi mai alfarma, kuma komai nasa ne; kuma an umarce ni da in zama cikin Musulmi
وَأَنۡ أَتۡلُوَاْ ٱلۡقُرۡءَانَۖ فَمَنِ ٱهۡتَدَىٰ فَإِنَّمَا يَهۡتَدِي لِنَفۡسِهِۦۖ وَمَن ضَلَّ فَقُلۡ إِنَّمَآ أَنَا۠ مِنَ ٱلۡمُنذِرِينَ
“An kuma (umarce ni) da in karanta Alqur’ani; don haka duk wanda ya shiriya, to ya shiriya ne don amfanin kansa; wanda kuwa ya vace sai ka ce (da shi): ‘Da ma ni ina cikin masu gargaxi ne kawai’”
وَقُلِ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ سَيُرِيكُمۡ ءَايَٰتِهِۦ فَتَعۡرِفُونَهَاۚ وَمَا رَبُّكَ بِغَٰفِلٍ عَمَّا تَعۡمَلُونَ
Ka kuma ce: “Dukkan yabo ya tabbata ga Allah; ba da daxewa ba zai nuna muku ayoyinsa, za kuma ku san su. Ubangijinka kuma ba rafkananne ba ne game da abin da kuke aikatawa.”
طسٓمٓ
XA SIN MIM[1]
1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.
تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ
Waxannan ayoyi ne na Littafi mabayyani
نَتۡلُواْ عَلَيۡكَ مِن نَّبَإِ مُوسَىٰ وَفِرۡعَوۡنَ بِٱلۡحَقِّ لِقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ
Muna karanta maka labarin Musa da Fir’auna da gaskiya don mutane da suke yin imani
إِنَّ فِرۡعَوۡنَ عَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَجَعَلَ أَهۡلَهَا شِيَعٗا يَسۡتَضۡعِفُ طَآئِفَةٗ مِّنۡهُمۡ يُذَبِّحُ أَبۡنَآءَهُمۡ وَيَسۡتَحۡيِۦ نِسَآءَهُمۡۚ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلۡمُفۡسِدِينَ
Lalle Fir’auna ya yi xagawa a cikin qasar (Masar) ya kuma mayar da mutanenta qungiyoyi daban-daban, yana bautar da wata qungiyar daga cikinsu, yana yanka ‘ya’yayensu maza, yana kuma qyale matansu da rai. Lalle shi ya kasance cikin mavarnata
وَنُرِيدُ أَن نَّمُنَّ عَلَى ٱلَّذِينَ ٱسۡتُضۡعِفُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَنَجۡعَلَهُمۡ أَئِمَّةٗ وَنَجۡعَلَهُمُ ٱلۡوَٰرِثِينَ
Muna kuma nufin za Mu yi baiwa ga waxanda aka wulaqanta a cikin qasar (Masar) Mu kuma mayar da su shugabanni, kuma Mu mayar da su magadan (mulkin Fir’auna)
وَنُمَكِّنَ لَهُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَنُرِيَ فِرۡعَوۡنَ وَهَٰمَٰنَ وَجُنُودَهُمَا مِنۡهُم مَّا كَانُواْ يَحۡذَرُونَ
Mu kuma kafa su a qasar, kuma Mu nuna wa Fir’auna da Hamana da rundunoninsu gaba xayansu abin da suke jin tsoro game da su (Banu Isra’ila)
وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰٓ أُمِّ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَرۡضِعِيهِۖ فَإِذَا خِفۡتِ عَلَيۡهِ فَأَلۡقِيهِ فِي ٱلۡيَمِّ وَلَا تَخَافِي وَلَا تَحۡزَنِيٓۖ إِنَّا رَآدُّوهُ إِلَيۡكِ وَجَاعِلُوهُ مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Muka kuma yi wa mahaifiyar Musa wahayi da cewa: “Ki shayar da shi; to yayin da kika ji masa tsoro, sai ki jefa shi a cikin kogi, kada kuma ki ji tsoro, kuma kada ki yi baqin ciki; lalle Mu Masu dawo miki da shi ne, kuma Masu sanya shi ne cikin manzanni.”
فَٱلۡتَقَطَهُۥٓ ءَالُ فِرۡعَوۡنَ لِيَكُونَ لَهُمۡ عَدُوّٗا وَحَزَنًاۗ إِنَّ فِرۡعَوۡنَ وَهَٰمَٰنَ وَجُنُودَهُمَا كَانُواْ خَٰطِـِٔينَ
Sai mutanen Fir’auna suka tsince shi domin (daga baya) ya zama abokin gaba da kuma baqin ciki a gare su. Lalle Fir’auna da Hamana da rundunoninsu sun kasance masu laifi
وَقَالَتِ ٱمۡرَأَتُ فِرۡعَوۡنَ قُرَّتُ عَيۡنٖ لِّي وَلَكَۖ لَا تَقۡتُلُوهُ عَسَىٰٓ أَن يَنفَعَنَآ أَوۡ نَتَّخِذَهُۥ وَلَدٗا وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ
Matar Fir’auna kuma ta ce: “(Shi) farin ciki ne a gare ni har da kai; kada ku kashe shi, muna fatan ya amfane mu ko kuma mu xauke shi a matsayin xa,” alhali kuwa su ba su san (abin da zai faru ba)
وَأَصۡبَحَ فُؤَادُ أُمِّ مُوسَىٰ فَٰرِغًاۖ إِن كَادَتۡ لَتُبۡدِي بِهِۦ لَوۡلَآ أَن رَّبَطۡنَا عَلَىٰ قَلۡبِهَا لِتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Zuciyar mahaifiyar Musa kuma ta wayi gari ba komai a cikinta (sai tunaninsa); ba shakka sauran qiris ta bayyana shi, ba don Mun xaure zuciyarta ba don ta zama cikin muminai
وَقَالَتۡ لِأُخۡتِهِۦ قُصِّيهِۖ فَبَصُرَتۡ بِهِۦ عَن جُنُبٖ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ
Ta kuma ce da ‘yar’uwarsa: “Ki bi sawunsa”; sai ta hango shi daga nesa, su kuwa ba su gane ita (‘yar’uwarsa ba ce)
۞وَحَرَّمۡنَا عَلَيۡهِ ٱلۡمَرَاضِعَ مِن قَبۡلُ فَقَالَتۡ هَلۡ أَدُلُّكُمۡ عَلَىٰٓ أَهۡلِ بَيۡتٖ يَكۡفُلُونَهُۥ لَكُمۡ وَهُمۡ لَهُۥ نَٰصِحُونَ
Da ma kuma can Mun haramta masa (nonon) masu shayarwa[1], sai (‘yar’uwar tasa) ta ce: “Yanzu ba na nuna muku mutanen wani gida da za su shayar muku da shi ba, su kuma za su kyautata masa?”
1- Watau ya qi karvar nonon duk wata mai shayarwa da aka kawo don shayar da shi a gidan Fir’auna.
فَرَدَدۡنَٰهُ إِلَىٰٓ أُمِّهِۦ كَيۡ تَقَرَّ عَيۡنُهَا وَلَا تَحۡزَنَ وَلِتَعۡلَمَ أَنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ
Sai Muka dawo da shi wurin mahaifiyarsa don hankalinta ya kwanta kuma don kada ta yi baqin ciki, don kuma ta san cewa alqawarin Allah gaskiya ne, sai dai kuma yawancinsu ba sa fahimtar (haka)
وَلَمَّا بَلَغَ أَشُدَّهُۥ وَٱسۡتَوَىٰٓ ءَاتَيۡنَٰهُ حُكۡمٗا وَعِلۡمٗاۚ وَكَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
Lokacin kuma da ya kai ganiyar qarfinsa ya kuma kammala, sai Muka ba shi hukunci da ilimi. Kamar haka kuwa Muke saka wa masu kyautatawa
وَدَخَلَ ٱلۡمَدِينَةَ عَلَىٰ حِينِ غَفۡلَةٖ مِّنۡ أَهۡلِهَا فَوَجَدَ فِيهَا رَجُلَيۡنِ يَقۡتَتِلَانِ هَٰذَا مِن شِيعَتِهِۦ وَهَٰذَا مِنۡ عَدُوِّهِۦۖ فَٱسۡتَغَٰثَهُ ٱلَّذِي مِن شِيعَتِهِۦ عَلَى ٱلَّذِي مِنۡ عَدُوِّهِۦ فَوَكَزَهُۥ مُوسَىٰ فَقَضَىٰ عَلَيۡهِۖ قَالَ هَٰذَا مِنۡ عَمَلِ ٱلشَّيۡطَٰنِۖ إِنَّهُۥ عَدُوّٞ مُّضِلّٞ مُّبِينٞ
Sai ya shiga cikin birnin a lokacin hutawar mutanensa, sai ya sami mutum biyu a cikinsa suna faxa; wannan xan qabilarsa ne, wannan kuma daga maqiyansa, sai xan qabilar tasa ya nemi taimakonsa a kan wanda yake daga maqiyansa; to sai Musa ya naushe shi, sai kuwa ya kashe shi; (da ya ga haka sai) ya ce: “Wannan yana daga aikin Shaixan, lalle shi kuwa maqiyi ne mai vatarwa na fili.”
قَالَ رَبِّ إِنِّي ظَلَمۡتُ نَفۡسِي فَٱغۡفِرۡ لِي فَغَفَرَ لَهُۥٓۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ
Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni na zalunci kaina, sai Ka yi min gafara,” sai ko Ya yi masa gafara. Lalle Shi kuwa Mai gafara ne, Mai jin qai
قَالَ رَبِّ بِمَآ أَنۡعَمۡتَ عَلَيَّ فَلَنۡ أَكُونَ ظَهِيرٗا لِّلۡمُجۡرِمِينَ
Ya ce: “Ya Ubangijina, saboda ni’imar da Ka yi min, ba zan tava zama mai taimakon masu laifi ba.”
فَأَصۡبَحَ فِي ٱلۡمَدِينَةِ خَآئِفٗا يَتَرَقَّبُ فَإِذَا ٱلَّذِي ٱسۡتَنصَرَهُۥ بِٱلۡأَمۡسِ يَسۡتَصۡرِخُهُۥۚ قَالَ لَهُۥ مُوسَىٰٓ إِنَّكَ لَغَوِيّٞ مُّبِينٞ
Sai ya wayi gari a cikin birnin a tsorace yana xar-xar, sai ga wanda ya nemi taimakon nan nasa a jiya yana sake neman taimakonsa, (sai) Musa ya ce da shi: “Lalle kai dai vatacce ne a fili!”
فَلَمَّآ أَنۡ أَرَادَ أَن يَبۡطِشَ بِٱلَّذِي هُوَ عَدُوّٞ لَّهُمَا قَالَ يَٰمُوسَىٰٓ أَتُرِيدُ أَن تَقۡتُلَنِي كَمَا قَتَلۡتَ نَفۡسَۢا بِٱلۡأَمۡسِۖ إِن تُرِيدُ إِلَّآ أَن تَكُونَ جَبَّارٗا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا تُرِيدُ أَن تَكُونَ مِنَ ٱلۡمُصۡلِحِينَ
To lokacin da ya nufi wawurar abokin gabar tasu (sai mai neman taimakon) ya ce: “Ya Musa, shin yanzu nufi kake ka kashe ni kamar yadda ka kashe rai a jiya? Ba abin da kake nufi sai ka zama mai tsaurin rai a bayan qasa; ba ka kuma nufin ka zama cikin masu kawo gyara.”
وَجَآءَ رَجُلٞ مِّنۡ أَقۡصَا ٱلۡمَدِينَةِ يَسۡعَىٰ قَالَ يَٰمُوسَىٰٓ إِنَّ ٱلۡمَلَأَ يَأۡتَمِرُونَ بِكَ لِيَقۡتُلُوكَ فَٱخۡرُجۡ إِنِّي لَكَ مِنَ ٱلنَّـٰصِحِينَ
Sai wani mutum (mumini daga mutanen Fir’auna) ya zo daga can qarshen birnin yana gaggawa, ya ce: “Ya Musa, lalle manyan gari (suna can) suna shawara a kanka don su kashe ka, to ka fita (daga birnin nan), lalle ni ina cikin masu yi maka nasiha.”
فَخَرَجَ مِنۡهَا خَآئِفٗا يَتَرَقَّبُۖ قَالَ رَبِّ نَجِّنِي مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ
Sai ya fita daga cikinsa (wato birnin) a tsorace yana ta xar-xar, ya ce: “Ya Ubangijina, Ka tserar da ni daga azzaluman mutanen nan.”
وَلَمَّا تَوَجَّهَ تِلۡقَآءَ مَدۡيَنَ قَالَ عَسَىٰ رَبِّيٓ أَن يَهۡدِيَنِي سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ
Yayin da kuma ya sa gaba ya nufi wajen (birnin) Madyana, sai ya ce: “Ina fatan Ubangijina Ya shiryar da ni hanyar da ta fi dacewa.”