Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 1

وَٱلۡفَجۡرِ

Na rantse da alfijir



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 2

وَلَيَالٍ عَشۡرٖ

Da kuma darare goma[1]


1- Watau kwanaki goma na farkon watan Zulhijja.


Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 3

وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ

Da kuma abin da yake cika[1] da kuma mara[2]


1- Watau bibbiyu ko hurhuxu ko shida-shida da sauransu.


2- Watau xaya ko uku ko biyar da sauransu.


Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ

Da kuma dare lokacin da yake tafiya (cikin duhu)



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 5

هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ

Shin a game da waxannan akwai rantsuwa (mai gamsarwa) ga mai hankali[1]?


1- Watau duk mai hankali zai gamsu da waxannan rantse-rantse.


Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 6

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ba ga Adawa?



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 7

إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ

(Watau qabilar) Iramu ma’abociyar tsawo



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 8

ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Wadda ba a halicci irinta ba a cikin garuruwa (a tsananin qarfi)



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ

Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 10

وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ

Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 11

ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 12

فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ

Suka kuma yawaita varna a cikinsu



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 13

فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ

Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 14

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ

Lalle Ubangijinka tabbas Yana nan a madakata[1]


1- Watau yana wurin da yake hangen xaukacin ayyukan bayinsa.


Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 15

فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ

Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 16

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيۡهِ رِزۡقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَهَٰنَنِ

Amma kuma idan Ya jarrabe shi sai Ya quntata masa a arzikinsa, sai ya ce: “Ubangijina Ya wulaqanta ni.”



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 17

كَلَّاۖ بَل لَّا تُكۡرِمُونَ ٱلۡيَتِيمَ

Faufau, ba haka ba ne; ku ba kwa karrama maraya ne



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 18

وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ

Kuma ba kwa kwaxaitar da juna kan ciyar da miskinai



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 19

وَتَأۡكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكۡلٗا لَّمّٗا

Kuma kuna cinye dukiyar gadon marayu mummunan ci



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 20

وَتُحِبُّونَ ٱلۡمَالَ حُبّٗا جَمّٗا

Kuma kuna son dukiya so mai yawa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 21

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا

Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا

Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu


1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.


Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 23

وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ

Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 24

يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي

Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 25

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ

To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ

Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata