Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 1

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلۡغَٰشِيَةِ

Shin labarin mai lulluvewa da (tsoro) ya zo maka?



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 2

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ خَٰشِعَةٌ

Wasu fuskoki a wannan ranar qasqantattu ne



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 3

عَامِلَةٞ نَّاصِبَةٞ

Masu aiki ne (tuquru)[1] masu shan wahala


1- Watau a wutar Jahannama.


Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 4

تَصۡلَىٰ نَارًا حَامِيَةٗ

Za su shiga wuta mai tsananin quna



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 5

تُسۡقَىٰ مِنۡ عَيۡنٍ ءَانِيَةٖ

Za a shayar da su daga idon ruwa mai tsananin zafi



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 6

لَّيۡسَ لَهُمۡ طَعَامٌ إِلَّا مِن ضَرِيعٖ

Ba su da wani abinci sai na qayar tsidau



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 7

لَّا يُسۡمِنُ وَلَا يُغۡنِي مِن جُوعٖ

Ba ya sa qiba kuma ba ya maganin yunwa



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 8

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ نَّاعِمَةٞ

Waxansu fuskokin kuwa a wannan ranar ni’imtattu ne



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 9

لِّسَعۡيِهَا رَاضِيَةٞ

Masu gamsuwa ne da (sakamakon) ayyukansu



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 10

فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ

(Suna) cikin Aljanna maxaukakiya[1]


1- Watau xaukaka ta daraja da xaukaka ta muhalli, domin gidajen Aljanna benaye ne wasu kan wasu.


Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 11

لَّا تَسۡمَعُ فِيهَا لَٰغِيَةٗ

Ba a jin zancen banza a cikinta



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 12

فِيهَا عَيۡنٞ جَارِيَةٞ

A cikinta akwai marmaro mai gudana



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 13

فِيهَا سُرُرٞ مَّرۡفُوعَةٞ

A cikinta akwai gadaje maxaukaka



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 14

وَأَكۡوَابٞ مَّوۡضُوعَةٞ

Da kofuna a ajijjiye



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 15

وَنَمَارِقُ مَصۡفُوفَةٞ

Da matasan kai a jejjere



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 16

وَزَرَابِيُّ مَبۡثُوثَةٌ

Da dardumai a shisshimfixe



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ

Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 18

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ

Da kuma sama yadda aka xaga ta?



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 19

وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ

Da kuma duwatsu yadda aka kakkafa su?



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 20

وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ

Da kuma qasa yadda aka shimfixa ta?



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 21

فَذَكِّرۡ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٞ

To ka yi wa’azi, lalle kai mai wa’azi ne kawai



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 22

لَّسۡتَ عَلَيۡهِم بِمُصَيۡطِرٍ

Kai ba mai tilasta su ba ne



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 23

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ

Sai dai wanda ya ba da baya ya kuma kafirce



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 24

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَكۡبَرَ

To Allah zai azabtar da shi azaba mafi girma[1]


1- Watau wutar Jahannama inda zai dawwama a cikinta har abada.


Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 25

إِنَّ إِلَيۡنَآ إِيَابَهُمۡ

Lalle zuwa gare Mu ne makomarsu take



Capítulo: Suratul Ghashiya

Verso : 26

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا حِسَابَهُم

Sannan kuma a kanmu ne hisabinsu yake