Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 1

وَٱلسَّمَآءِ وَٱلطَّارِقِ

Na rantse da sama da (tauraro) mai zuwa cikin dare



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 2

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلطَّارِقُ

Me ya sanar da kai mai zuwa cikin dare?



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 3

ٱلنَّجۡمُ ٱلثَّاقِبُ

Tauraro ne mai keta (duhu) da haskensa



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 4

إِن كُلُّ نَفۡسٖ لَّمَّا عَلَيۡهَا حَافِظٞ

Ba wani rai face akwai mai tsaron sa



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 5

فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ مِمَّ خُلِقَ

To mutum ya duba mana, daga me aka halicce shi?



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 6

خُلِقَ مِن مَّآءٖ دَافِقٖ

An halicce shi ne daga wani ruwa mai ingizar juna[1]


1- Watau maniyyi.


Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 7

يَخۡرُجُ مِنۢ بَيۡنِ ٱلصُّلۡبِ وَٱلتَّرَآئِبِ

Mai fita daga tsakanin tsatso da karankarma[1]


1- Watau daga tsakanin qashin bayan namiji da qasusuwan qirjinsa.


Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 8

إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ

Lalle Shi (Allah) Mai iko ne a kan dawo da shi



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 9

يَوۡمَ تُبۡلَى ٱلسَّرَآئِرُ

A ranar da za a bayyana asirai[1]


1- Watau abubuwan da suke cikin zukata na niyyoyi da aqidu da sauransu.


Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 10

فَمَا لَهُۥ مِن قُوَّةٖ وَلَا نَاصِرٖ

To ba shi da wani qarfi ko wani mataimaki



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 11

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلرَّجۡعِ

Na rantse da sama ma’abociyar dawo (da ruwa)



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 12

وَٱلۡأَرۡضِ ذَاتِ ٱلصَّدۡعِ

Da kuma qasa ma’abociyar tsagewa (shuka ta fito)



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 13

إِنَّهُۥ لَقَوۡلٞ فَصۡلٞ

Lalle shi (Alqur’ani) magana ce mai tsage gaskiya



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 14

وَمَا هُوَ بِٱلۡهَزۡلِ

Kuma shi ba zancen banza ba ne



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 15

إِنَّهُمۡ يَكِيدُونَ كَيۡدٗا

Lalle su (kafirai) suna qulla mummunan makirci



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 16

وَأَكِيدُ كَيۡدٗا

Ni kuma ina shirya musu mummunan sakamako



Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 17

فَمَهِّلِ ٱلۡكَٰفِرِينَ أَمۡهِلۡهُمۡ رُوَيۡدَۢا

To sai ka saurara wa kafirai, ka saurara musu kaxan