Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 1

إِذَا ٱلسَّمَآءُ ٱنشَقَّتۡ

Idan sama ta tsattsage[1]


1- Watau mala’iku suka yi ta saukowa.


Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 2

وَأَذِنَتۡ لِرَبِّهَا وَحُقَّتۡ

Ta kuma saurari Ubangijinta, kuma ya wajaba (ta saurara)



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 3

وَإِذَا ٱلۡأَرۡضُ مُدَّتۡ

Kuma idan qasa aka miqe ta



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 4

وَأَلۡقَتۡ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتۡ

Ta kuma jefar da abin da yake cikinta ta wofinta[1]


1- Watau cikinta ya koma fayau babu sauran wani abu.


Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 5

وَأَذِنَتۡ لِرَبِّهَا وَحُقَّتۡ

Ta kuma saurari Ubangijinta kuma ya wajaba (ta saurara)



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡإِنسَٰنُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدۡحٗا فَمُلَٰقِيهِ

Ya kai mutum, lalle kai mai yin aiki ne tuquru zuwa ga Ubangijinka, to mai haxuwa da Shi ne



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 7

فَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ بِيَمِينِهِۦ

To amma duk wanda aka bai wa littafinsa a hannunsa na dama



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 8

فَسَوۡفَ يُحَاسَبُ حِسَابٗا يَسِيرٗا

To za a yi masa hisabi mai sauqi[1]


1- Watau ta hanyar bijiro ayyukansa a dunqule ba tare da binciken qwaqwaf ba.


Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 9

وَيَنقَلِبُ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ مَسۡرُورٗا

Ya kuma juyo zuwa ga iyalinsa yana farin ciki



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 10

وَأَمَّا مَنۡ أُوتِيَ كِتَٰبَهُۥ وَرَآءَ ظَهۡرِهِۦ

Amma wanda kuwa aka bai wa littafinsa ta bayan bayansa



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 11

فَسَوۡفَ يَدۡعُواْ ثُبُورٗا

To zai yi kiran halaka



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 12

وَيَصۡلَىٰ سَعِيرًا

Zai kuma shiga (wutar) Sa’ira



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 13

إِنَّهُۥ كَانَ فِيٓ أَهۡلِهِۦ مَسۡرُورًا

Lalle a da shi ya kasance mai farin ciki ne cikin iyalinsa



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 14

إِنَّهُۥ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ

Lalle ya yi zaton ba zai koma (ga Allah) ba



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 15

بَلَىٰٓۚ إِنَّ رَبَّهُۥ كَانَ بِهِۦ بَصِيرٗا

Haka yake, (zai koma), lalle Ubangijinsa Ya kasance Mai ganin sa ne



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 16

فَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلشَّفَقِ

To ina rantsuwa da shafaqi



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 17

وَٱلَّيۡلِ وَمَا وَسَقَ

Da kuma dare da abin da ya tattara



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 18

وَٱلۡقَمَرِ إِذَا ٱتَّسَقَ

Da kuma wata idan ya cika



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 19

لَتَرۡكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٖ

Tabbas za ku hau wani mataki bayan wani mataki[1]


1- Watau na halittarsu, sai sun kasance xigon maniyyi, sannan su zama gudan jini sai kuma gudar tsoka, har zuwa cikar halittarsu.


Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 20

فَمَا لَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

To me ya same su ne ba sa yin imani?



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 21

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقُرۡءَانُ لَا يَسۡجُدُونَۤ۩

Idan kuma an karanta musu Alqur’ani ba sa yin sujjada?



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 22

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يُكَذِّبُونَ

A’a, su dai waxanda suka kafirce suna qaryatawa ne



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 23

وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا يُوعُونَ

Allah kuwa (Shi) Ya fi sanin abin da suke voyewa (a zukatansu)



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 24

فَبَشِّرۡهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ

To ka yi musu albishir da azaba mai raxaxi



Capítulo: Suratul Inshiqaq

Verso : 25

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونِۭ

Sai dai waxanda suka yi imani, suka kuma yi ayyuka nagari, to suna da lada marar yankewa