Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 121

وَلَا يُنفِقُونَ نَفَقَةٗ صَغِيرَةٗ وَلَا كَبِيرَةٗ وَلَا يَقۡطَعُونَ وَادِيًا إِلَّا كُتِبَ لَهُمۡ لِيَجۡزِيَهُمُ ٱللَّهُ أَحۡسَنَ مَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Ba kuma za su bayar da wata sadaka ba, qarama ko kuma babba, kuma ba wani kwazazzabo da za su keta sai an rubuta musu ladansu don Allah Ya saka musu da mafi kyawun abin da suka zamanto suna aikatawa



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 122

۞وَمَا كَانَ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ لِيَنفِرُواْ كَآفَّةٗۚ فَلَوۡلَا نَفَرَ مِن كُلِّ فِرۡقَةٖ مِّنۡهُمۡ طَآئِفَةٞ لِّيَتَفَقَّهُواْ فِي ٱلدِّينِ وَلِيُنذِرُواْ قَوۡمَهُمۡ إِذَا رَجَعُوٓاْ إِلَيۡهِمۡ لَعَلَّهُمۡ يَحۡذَرُونَ

Bai kamata muminai su fita yaqi gaba xaya ba. Me zai hana wasu jama’a daga kowace qabila (su zauna) don su koyi ilimin addini, su kuma yi wa mutanensu gargaxi idan sun dawo musu don su kiyaye (dokokin Allah)?



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 123

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ قَٰتِلُواْ ٱلَّذِينَ يَلُونَكُم مِّنَ ٱلۡكُفَّارِ وَلۡيَجِدُواْ فِيكُمۡ غِلۡظَةٗۚ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ مَعَ ٱلۡمُتَّقِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku yaqi kafirai waxanda suke maqota da ku, kuma su sami kausasawa daga wajenku. Ku kuma sani cewa Allah Yana tare da masu taqawa



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 124

وَإِذَا مَآ أُنزِلَتۡ سُورَةٞ فَمِنۡهُم مَّن يَقُولُ أَيُّكُمۡ زَادَتۡهُ هَٰذِهِۦٓ إِيمَٰنٗاۚ فَأَمَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ فَزَادَتۡهُمۡ إِيمَٰنٗا وَهُمۡ يَسۡتَبۡشِرُونَ

Idan kuwa aka saukar da wata sura, daga cikinsu akwai waxanda suke cewa: “Wane ne daga cikinku wannan ta qara masa imani?” To amma waxanda suka yi imani su kam ta qara musu imani alhali suna cike da farin ciki



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 125

وَأَمَّا ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ فَزَادَتۡهُمۡ رِجۡسًا إِلَىٰ رِجۡسِهِمۡ وَمَاتُواْ وَهُمۡ كَٰفِرُونَ

Amma kuma waxanda suke da munafunci a zukatansu sai (surar) ta qara musu wata dauxa a kan dauxarsu (ta munafunci) suka kuma mutu suna kafirai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 126

أَوَلَا يَرَوۡنَ أَنَّهُمۡ يُفۡتَنُونَ فِي كُلِّ عَامٖ مَّرَّةً أَوۡ مَرَّتَيۡنِ ثُمَّ لَا يَتُوبُونَ وَلَا هُمۡ يَذَّكَّرُونَ

Shin yanzu ba sa ganin cewa ana jarrabar su a kowace shekara sau xaya ko sau biyu, sannan ba sa tuba kuma ba sa wa’azantuwa?



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 127

وَإِذَا مَآ أُنزِلَتۡ سُورَةٞ نَّظَرَ بَعۡضُهُمۡ إِلَىٰ بَعۡضٍ هَلۡ يَرَىٰكُم مِّنۡ أَحَدٖ ثُمَّ ٱنصَرَفُواْۚ صَرَفَ ٱللَّهُ قُلُوبَهُم بِأَنَّهُمۡ قَوۡمٞ لَّا يَفۡقَهُونَ

Idan kuma an saukar da wata surar sai su kalli junansu (su ce): “Shin akwai wani mai ganin ku?” Sannan sai su juya. To Allah Ya juyar da zukatansu saboda su mutane ne da ba sa fahimta



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 128

لَقَدۡ جَآءَكُمۡ رَسُولٞ مِّنۡ أَنفُسِكُمۡ عَزِيزٌ عَلَيۡهِ مَا عَنِتُّمۡ حَرِيصٌ عَلَيۡكُم بِٱلۡمُؤۡمِنِينَ رَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Haqiqa Manzo ya zo muku daga jinsinku; abin da zai wahalar da ku yana damun sa; mai kwaxayin alheri ne gare ku, mai tausayawa kuma mai jin qai ga muminai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 129

فَإِن تَوَلَّوۡاْ فَقُلۡ حَسۡبِيَ ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ عَلَيۡهِ تَوَكَّلۡتُۖ وَهُوَ رَبُّ ٱلۡعَرۡشِ ٱلۡعَظِيمِ

To idan sun ba da baya sai ka ce: “Allah Ya ishe ni, babu wani abin bautawa da gaskiya sai Shi, a gare Shi kaxai na dogara; kuma Shi ne Ubangijin Al’arshi mai girma.”