Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 91

أَن دَعَوۡاْ لِلرَّحۡمَٰنِ وَلَدٗا

Saboda sun yi da’awar Allah Yana da xa!



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 92

وَمَا يَنۢبَغِي لِلرَّحۡمَٰنِ أَن يَتَّخِذَ وَلَدًا

Bai kuwa dace da (Allah) Mai rahama Ya zama Yana da xa ba



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 93

إِن كُلُّ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ إِلَّآ ءَاتِي ٱلرَّحۡمَٰنِ عَبۡدٗا

Ba wani abu da yake cikin sammai da qasa face ya zo wa (Allah) Mai rahama a matsayin bawa



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 94

لَّقَدۡ أَحۡصَىٰهُمۡ وَعَدَّهُمۡ عَدّٗا

Lalle Ya kiyaye da su Ya kuma qididdige su sosai



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 95

وَكُلُّهُمۡ ءَاتِيهِ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فَرۡدًا

Kuma dukkansu kowa zai zo masa a ranar alqiyama shi kaxai



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 96

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ سَيَجۡعَلُ لَهُمُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وُدّٗا

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki na gari, to (Allah) Mai rahama zai sanya musu qauna[1]


1- Watau zanya farin jininsu a zukatan masoyansa a sama da qasa. Shi ma kuma zai qaunace su.


Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 97

فَإِنَّمَا يَسَّرۡنَٰهُ بِلِسَانِكَ لِتُبَشِّرَ بِهِ ٱلۡمُتَّقِينَ وَتُنذِرَ بِهِۦ قَوۡمٗا لُّدّٗا

To Mun dai sauqaqe shi (Alqur’ani) da harshenka ne don kawai ka yi wa masu taqawa albishir da shi, ka kuma gargaxi mutane masu tsananin jayayya da shi



Capítulo: Suratu Maryam

Verso : 98

وَكَمۡ أَهۡلَكۡنَا قَبۡلَهُم مِّن قَرۡنٍ هَلۡ تُحِسُّ مِنۡهُم مِّنۡ أَحَدٍ أَوۡ تَسۡمَعُ لَهُمۡ رِكۡزَۢا

Al’umma nawa Muka hallaka a gabaninsu, shin kana jin xuriyar wani daga cikinsu, ko kuwa kana jin ‘yar muryarsu?