Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 61

وَإِنَّهُۥ لَعِلۡمٞ لِّلسَّاعَةِ فَلَا تَمۡتَرُنَّ بِهَا وَٱتَّبِعُونِۚ هَٰذَا صِرَٰطٞ مُّسۡتَقِيمٞ

Lalle kuma shi (Isa) alama ce ta zuwan alqiyama[1], kada ku yi shakka game da ita, kuma ku bi Ni. Wannan ita ce hanya madaidaiciya


1- Watau lokacin da zai sauko daga sama ta biyu a qarshen zamani, kamar yadda tarin hadisan Annabi () suka tabbatar.


Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 62

وَلَا يَصُدَّنَّكُمُ ٱلشَّيۡطَٰنُۖ إِنَّهُۥ لَكُمۡ عَدُوّٞ مُّبِينٞ

Kada kuma Shaixan ya kange ku; lalle shi maqiyi ne mai bayyana (qiyyaya) a gare ku



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 63

وَلَمَّا جَآءَ عِيسَىٰ بِٱلۡبَيِّنَٰتِ قَالَ قَدۡ جِئۡتُكُم بِٱلۡحِكۡمَةِ وَلِأُبَيِّنَ لَكُم بَعۡضَ ٱلَّذِي تَخۡتَلِفُونَ فِيهِۖ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

Lokacin da kuma Isa ya zo da hujjoji bayyanannu ya ce: “Haqiqa na zo muku da hikima, don kuma in bayyana muku sashin da kuke sassavawa cikinsa; to ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku bi ni



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 64

إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ رَبِّي وَرَبُّكُمۡ فَٱعۡبُدُوهُۚ هَٰذَا صِرَٰطٞ مُّسۡتَقِيمٞ

“Lalle Allah Shi ne Ubangijina kuma Ubangijinku, sai ku bauta masa. Wannan ita ce hanya madaidaiciya.”



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 65

فَٱخۡتَلَفَ ٱلۡأَحۡزَابُ مِنۢ بَيۡنِهِمۡۖ فَوَيۡلٞ لِّلَّذِينَ ظَلَمُواْ مِنۡ عَذَابِ يَوۡمٍ أَلِيمٍ

Sai qungiyoyi suka sassava a tsakaninsu[1]; don haka tsananin azabar yini mai raxaxi ya tabbata ga waxanda suka yi zalunci


1- Wasu suka ce shi Allah ne; wasu kuma suka ce xan Allah ne; wasu kuma suka ce shi da mahaifiyarsa duka alloli ne.


Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 66

هَلۡ يَنظُرُونَ إِلَّا ٱلسَّاعَةَ أَن تَأۡتِيَهُم بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Ba abin da suke jira sai alqiyama kawai ta zo musu kwatsam, alhali ba tare da sun sani ba



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 67

ٱلۡأَخِلَّآءُ يَوۡمَئِذِۭ بَعۡضُهُمۡ لِبَعۡضٍ عَدُوٌّ إِلَّا ٱلۡمُتَّقِينَ

Masoya a wannan ranar maqiyan juna ne sai masu taqawa kaxai



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 68

يَٰعِبَادِ لَا خَوۡفٌ عَلَيۡكُمُ ٱلۡيَوۡمَ وَلَآ أَنتُمۡ تَحۡزَنُونَ

Ya ku bayina, babu wani tsoro gare ku a yau, kuma ba za ku yi baqin ciki ba



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 69

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِـَٔايَٰتِنَا وَكَانُواْ مُسۡلِمِينَ

(Su ne) waxanda suka yi imani da ayoyinmu, suka kuma kasance Musulmi



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 70

ٱدۡخُلُواْ ٱلۡجَنَّةَ أَنتُمۡ وَأَزۡوَٰجُكُمۡ تُحۡبَرُونَ

(Za a ce da su): “Ku shiga Aljanna ku da matanku, za a faranta muku rai.”



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 71

يُطَافُ عَلَيۡهِم بِصِحَافٖ مِّن ذَهَبٖ وَأَكۡوَابٖۖ وَفِيهَا مَا تَشۡتَهِيهِ ٱلۡأَنفُسُ وَتَلَذُّ ٱلۡأَعۡيُنُۖ وَأَنتُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Ana zagayawa tsakaninsu da akusa na zinari da kofuna; a cikinta kuma akwai (duk) abin da rayuka suke sha’awa, idanuwa kuma suke jin daxin (ganinsu); ku kuma a cikinta madawwama ne



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 72

وَتِلۡكَ ٱلۡجَنَّةُ ٱلَّتِيٓ أُورِثۡتُمُوهَا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Waccan kuma ita ce Aljannar da aka gadar muku ita saboda abin da kuka kasance kuma aikatawa



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 73

لَكُمۡ فِيهَا فَٰكِهَةٞ كَثِيرَةٞ مِّنۡهَا تَأۡكُلُونَ

A cikinta kuna da `ya`yan itatuwa na marmari masu yawa, daga gare su kuma za ku riqa ci



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 74

إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي عَذَابِ جَهَنَّمَ خَٰلِدُونَ

Lalle masu manyan laifuka suna cikin azabar (wutar) Jahannama suna masu dawwama



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 75

لَا يُفَتَّرُ عَنۡهُمۡ وَهُمۡ فِيهِ مُبۡلِسُونَ

Ba a yanke musu ita (azabar), su kuwa masu yanke qaunar (fita) ne daga cikinta



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 76

وَمَا ظَلَمۡنَٰهُمۡ وَلَٰكِن كَانُواْ هُمُ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Ba Mu kuwa zalunce su ba, sai dai su ne suka kasance azzalumai



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 77

وَنَادَوۡاْ يَٰمَٰلِكُ لِيَقۡضِ عَلَيۡنَا رَبُّكَۖ قَالَ إِنَّكُم مَّـٰكِثُونَ

Suka kuma yi kiran: “Ya (kai mai tsaron wuta) Maliku, Ubangijinka Ya kashe mu mana!” Ya ce: “Lalle ku masu dawwama ne.”



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 78

لَقَدۡ جِئۡنَٰكُم بِٱلۡحَقِّ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَكُمۡ لِلۡحَقِّ كَٰرِهُونَ

Haqiqa Mun zo muku da gaskiya sai dai kuma mafiya yawanku masu qin gaskiya ne



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 79

أَمۡ أَبۡرَمُوٓاْ أَمۡرٗا فَإِنَّا مُبۡرِمُونَ

A’a, sun dai shirya wani makirci ne, Mu ma lalle Masu yin namu shirin ne



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 80

أَمۡ يَحۡسَبُونَ أَنَّا لَا نَسۡمَعُ سِرَّهُمۡ وَنَجۡوَىٰهُمۚ بَلَىٰ وَرُسُلُنَا لَدَيۡهِمۡ يَكۡتُبُونَ

Ko suna tsammanin cewa Mu ba Ma jin asirinsu da ganawarsu ne? Ba haka ba ne, manzanninmu suna tare da su suna rubutawa



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 81

قُلۡ إِن كَانَ لِلرَّحۡمَٰنِ وَلَدٞ فَأَنَا۠ أَوَّلُ ٱلۡعَٰبِدِينَ

Ka ce: “Idan da (Allah) Mai rahama zai zamanto Yana da xa, to ni ne farkon masu bauta[1].”


1- Watau shi ne farkon masu bauta wa wannan xan, domin kuwa ya zama wani sashi ne na Allah.


Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 82

سُبۡحَٰنَ رَبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ رَبِّ ٱلۡعَرۡشِ عَمَّا يَصِفُونَ

Tsarki ya tabbata ga Ubangijin sammai da qasa, Ubangiijn Al’arshi game da abin da suke siffantawa



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 83

فَذَرۡهُمۡ يَخُوضُواْ وَيَلۡعَبُواْ حَتَّىٰ يُلَٰقُواْ يَوۡمَهُمُ ٱلَّذِي يُوعَدُونَ

Sai ka bar su su yi ta kutse suna wasanni, har su haxu da ranar da ake alqawarta musu



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 84

وَهُوَ ٱلَّذِي فِي ٱلسَّمَآءِ إِلَٰهٞ وَفِي ٱلۡأَرۡضِ إِلَٰهٞۚ وَهُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ

Shi ne kuma Wanda Yake Abin bauta a cikin sama kuma Abin bauta a qasa. Kuma Shi Mai hikima ne, Masani



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 85

وَتَبَارَكَ ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَعِندَهُۥ عِلۡمُ ٱلسَّاعَةِ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Kuma wanda Yake da mulkin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu alhairansa sun yi yawa, kuma a wurinsa sanin (ranar) alqiyama yake, wurinsa kuma za a komar da ku



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 86

وَلَا يَمۡلِكُ ٱلَّذِينَ يَدۡعُونَ مِن دُونِهِ ٱلشَّفَٰعَةَ إِلَّا مَن شَهِدَ بِٱلۡحَقِّ وَهُمۡ يَعۡلَمُونَ

Waxanda kuwa suke bauta wa wani abu ba Shi ba, ba sa mallakar ceto, sai dai waxanda suka yi Kalmar Shahada ta gaskiya, alhalin suna sane (da ma’anarta)



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 87

وَلَئِن سَأَلۡتَهُم مَّنۡ خَلَقَهُمۡ لَيَقُولُنَّ ٱللَّهُۖ فَأَنَّىٰ يُؤۡفَكُونَ

Tabbas kuma da za ka tambaye su, wane ne ya halicce su? Lalle za su ce: “Allah ne;” to ta yaya ake kautar da su?



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 88

وَقِيلِهِۦ يَٰرَبِّ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ قَوۡمٞ لَّا يُؤۡمِنُونَ

Kuma (sanin) faxarsa (wato Ma’aiki) cewa: “Ya Ubangiji lalle waxannan mutane ne da ba sa yin imani,” (yana a wurinsa)



Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 89

فَٱصۡفَحۡ عَنۡهُمۡ وَقُلۡ سَلَٰمٞۚ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ

To ka kawar musu kai, kuma ka ce: “Na kuvuta (daga haqqinku). Don haka ba da daxewa ba za ku sani.”