Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 61

فَلَمَّا جَآءَ ءَالَ لُوطٍ ٱلۡمُرۡسَلُونَ

To lokacin da manzannin suka zo wa iyalin Luxu



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 62

قَالَ إِنَّكُمۡ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ

Ya ce: “Lalle ku wasu mutane ne da ba a san su ba.”



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 63

قَالُواْ بَلۡ جِئۡنَٰكَ بِمَا كَانُواْ فِيهِ يَمۡتَرُونَ

Suka ce: “A’a, mu mun zo maka ne da abin da (mutanenka) suke kokwanto game da shi



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 64

وَأَتَيۡنَٰكَ بِٱلۡحَقِّ وَإِنَّا لَصَٰدِقُونَ

“Mun kuma zo maka da dahir, lalle kuma tabbas mu masu gaskiya ne



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 65

فَأَسۡرِ بِأَهۡلِكَ بِقِطۡعٖ مِّنَ ٱلَّيۡلِ وَٱتَّبِعۡ أَدۡبَٰرَهُمۡ وَلَا يَلۡتَفِتۡ مِنكُمۡ أَحَدٞ وَٱمۡضُواْ حَيۡثُ تُؤۡمَرُونَ

“Sai ka tafi da iyalinka cikin wani yankin dare ka kuma riqa bin su a baya, kada kuwa xaya daga cikinku ya waiwaya, kuma ku tafi inda aka umarce ku.”



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 66

وَقَضَيۡنَآ إِلَيۡهِ ذَٰلِكَ ٱلۡأَمۡرَ أَنَّ دَابِرَ هَـٰٓؤُلَآءِ مَقۡطُوعٞ مُّصۡبِحِينَ

Muka kuwa sanar da shi abin da Muka qaddara na wannan al’amari cewa, qarshen waxannan zai yanke ne da asuba



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 67

وَجَآءَ أَهۡلُ ٱلۡمَدِينَةِ يَسۡتَبۡشِرُونَ

Mutanen garin kuma suka zo suna murna (da ganin baqin)



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 68

قَالَ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ ضَيۡفِي فَلَا تَفۡضَحُونِ

Ya ce: “Lalle waxannan baqina ne, kada fa ku kunyata ni



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 69

وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَلَا تُخۡزُونِ

“Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kada ku tozarta ni[1].”


1- Annabi Luxu ya yi wannan maganar ne kafin ya san cewa waxannan baqi nasa mala’iku ne.


Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 70

قَالُوٓاْ أَوَلَمۡ نَنۡهَكَ عَنِ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Suka ce: “Ashe ba mu hana ka (ka saukar da) mutane (baqi ba)?”



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 71

قَالَ هَـٰٓؤُلَآءِ بَنَاتِيٓ إِن كُنتُمۡ فَٰعِلِينَ

Ya ce: “Ga ‘ya’yana nan (ku aura)[1] idan kun kasance masu aikata (haka)


1- Yana nufin matan al’ummarsa.


Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 72

لَعَمۡرُكَ إِنَّهُمۡ لَفِي سَكۡرَتِهِمۡ يَعۡمَهُونَ

“Na rantse da rayuwarka lalle su tabbas suna cikin mayensu suna ta ximuwa.”



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 73

فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّيۡحَةُ مُشۡرِقِينَ

Sai tsawa ta auka musu lokacin hudowar rana



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 74

فَجَعَلۡنَا عَٰلِيَهَا سَافِلَهَا وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِمۡ حِجَارَةٗ مِّن سِجِّيلٍ

Sai Muka mayar da samanta ya koma qasa, Muka kuma yi musu ruwan duwatsu soyayyu



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 75

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّلۡمُتَوَسِّمِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga masu hangen nesa



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 76

وَإِنَّهَا لَبِسَبِيلٖ مُّقِيمٍ

Lalle kuma ita (alqaryar) tabbas tana kan wani gwadabe ne miqaqqe



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 77

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai izina ga muminai



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 78

وَإِن كَانَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأَيۡكَةِ لَظَٰلِمِينَ

Lalle kuma mutanen (alqaryar) Mai duhuwa tabbas sun zamanto azzalumai



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 79

فَٱنتَقَمۡنَا مِنۡهُمۡ وَإِنَّهُمَا لَبِإِمَامٖ مُّبِينٖ

Sai Muka azabtar da su, lalle kuma su biyun suna kan wani gwadabe ne fitacce



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 80

وَلَقَدۡ كَذَّبَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡحِجۡرِ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Haqiqa kuma mutanen Hijiru (Samudawa) sun qaryata manzanni



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 81

وَءَاتَيۡنَٰهُمۡ ءَايَٰتِنَا فَكَانُواْ عَنۡهَا مُعۡرِضِينَ

Muka kuma kawo musu ayoyinmu, sai suka zamanto masu bijirewa daga gare su



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 82

وَكَانُواْ يَنۡحِتُونَ مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتًا ءَامِنِينَ

Sun zamanto suna fafe duwatsu suna yin gidaje su zama cikin aminci



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 83

فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّيۡحَةُ مُصۡبِحِينَ

Sai tsawa ta auka musu da asuba



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 84

فَمَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يَكۡسِبُونَ

Sai abin da suka zamanto suna aikatawa bai amfane su ba



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 85

وَمَا خَلَقۡنَا ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَآ إِلَّا بِٱلۡحَقِّۗ وَإِنَّ ٱلسَّاعَةَ لَأٓتِيَةٞۖ فَٱصۡفَحِ ٱلصَّفۡحَ ٱلۡجَمِيلَ

Ba Mu kuma halicci sammai da qasa ba sai da gaskiya. Kuma lalle alqiyama tabbas mai zuwa ce, sai ka yi afuwa kyakkyawar afuwa[1]


1- Watau afuwar da babu cutarwa a cikinta sai dai kyautatawa ga wanda ya munana.


Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 86

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ ٱلۡخَلَّـٰقُ ٱلۡعَلِيمُ

Lalle Ubangijinka Shi ne Mai halitta, Masani



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 87

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَٰكَ سَبۡعٗا مِّنَ ٱلۡمَثَانِي وَٱلۡقُرۡءَانَ ٱلۡعَظِيمَ

Haqiqa kuma Mun ba ka (ayoyi) bakwai waxanda ake ta nanatawa (wato Suratul Fatiha) da kuma Alqur’ani mai girma



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 88

لَا تَمُدَّنَّ عَيۡنَيۡكَ إِلَىٰ مَا مَتَّعۡنَا بِهِۦٓ أَزۡوَٰجٗا مِّنۡهُمۡ وَلَا تَحۡزَنۡ عَلَيۡهِمۡ وَٱخۡفِضۡ جَنَاحَكَ لِلۡمُؤۡمِنِينَ

Kada ka zura idanuwanka ga abubuwan jin daxi da Muka ba wa wasu dangogi daga cikinsu, kada kuma ka yi baqin ciki a kansu, kuma ka qasqantar da kanka ga muminai



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 89

وَقُلۡ إِنِّيٓ أَنَا ٱلنَّذِيرُ ٱلۡمُبِينُ

Ka kuma ce: “Lalle ni, ni ne mai gargaxi mabayyani»



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 90

كَمَآ أَنزَلۡنَا عَلَى ٱلۡمُقۡتَسِمِينَ

Kamar yadda Muka saukar wa masu rarrabawa (wato ma’abota littafi)