Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 31

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ مَفَازًا

Lalle masu taqawa suna da babban rabo



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 32

حَدَآئِقَ وَأَعۡنَٰبٗا

(Su ne) gonaki da inabai



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 33

وَكَوَاعِبَ أَتۡرَابٗا

Da ‘yan mata tsaraiku



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 34

وَكَأۡسٗا دِهَاقٗا

Da kofin (giya) cikakke



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 35

لَّا يَسۡمَعُونَ فِيهَا لَغۡوٗا وَلَا كِذَّـٰبٗا

Ba sa jin maganar banza a cikinta ko kuma qarya



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 36

جَزَآءٗ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابٗا

Sakamako ne daga Ubangijinka, kyauta ce a lissafe (gwargwadon aikin kowa)



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 37

رَّبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا ٱلرَّحۡمَٰنِۖ لَا يَمۡلِكُونَ مِنۡهُ خِطَابٗا

Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu (watau Allah) Mai rahama; (halittu) ba sa samun ikon yi masa magana daga gare Shi



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 38

يَوۡمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ صَفّٗاۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنۡ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَقَالَ صَوَابٗا

Ranar da Jibrilu da mala’iku za su tsaya sahu-sahu; (halittu) ba sa iya magana sai fa wanda (Allah) Mai rahama Ya yi wa izini, ya kuma faxi abin da ya dace[1]


1- Watau kalmar tauhidi.


Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 39

ذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمُ ٱلۡحَقُّۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا

Wannan rana ce tabbatacciya; saboda haka wanda ya ga dama sai ya riqi kyakkyawar makoma zuwa ga Ubangijinsa



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 40

إِنَّآ أَنذَرۡنَٰكُمۡ عَذَابٗا قَرِيبٗا يَوۡمَ يَنظُرُ ٱلۡمَرۡءُ مَا قَدَّمَتۡ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلۡكَافِرُ يَٰلَيۡتَنِي كُنتُ تُرَٰبَۢا

Lalle Mun yi muku gargaxin azaba ta kurkusa, a ranar da mutum zai ga abin da hannayensa suka gabatar (na alheri ko na sharri), kafiri kuma ya riqa cewa: “Ina ma da na zama turvaya[1]!”


1- Watau kamar sauran dabbobi da za a ce musu su zama turvaya.