Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 31

فَحَقَّ عَلَيۡنَا قَوۡلُ رَبِّنَآۖ إِنَّا لَذَآئِقُونَ

“Saboda haka faxar Ubangijinmu (ta azaba) ta tabbata a kanmu; (cewa) lalle tabbas za mu xanxana kuxarmu



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 32

فَأَغۡوَيۡنَٰكُمۡ إِنَّا كُنَّا غَٰوِينَ

“Don haka muka vatar da ku, domin mu ma lalle mun kasance vatattu ne.”



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 33

فَإِنَّهُمۡ يَوۡمَئِذٖ فِي ٱلۡعَذَابِ مُشۡتَرِكُونَ

Saboda haka su a wannan ranar, masu tarayya ne a cikin azaba



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 34

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفۡعَلُ بِٱلۡمُجۡرِمِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke yi wa masu manyan laifuka



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 35

إِنَّهُمۡ كَانُوٓاْ إِذَا قِيلَ لَهُمۡ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسۡتَكۡبِرُونَ

Lalle sun kasance idan aka ce da su: “Babu abin bauta wa da gaskiya sai Allah,” sai su riqa yin girman kai



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 36

وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓاْ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٖ مَّجۡنُونِۭ

Su kuma riqa cewa: “Yanzu ma bar allolinmu don wani mawaqi mai tavin hankali?”



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 37

بَلۡ جَآءَ بِٱلۡحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Ba haka ba ne, ya dai zo ne da gaskiya, ya kuma gaskata manzanni



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 38

إِنَّكُمۡ لَذَآئِقُواْ ٱلۡعَذَابِ ٱلۡأَلِيمِ

Lalle ku tabbas za ku xanxani azaba mai tsanani



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 39

وَمَا تُجۡزَوۡنَ إِلَّا مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ba kuwa za a saka muku ba sai da irin abin da kuka kasance kuna aikatawa



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 40

إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ

Sai dai bayin Allah waxanda aka tsarkake



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 41

أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ رِزۡقٞ مَّعۡلُومٞ

Waxannan suna da arziki sananne



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 42

فَوَٰكِهُ وَهُم مُّكۡرَمُونَ

(Shi ne) kayan marmari; su kuma ababen karramawa ne



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 43

فِي جَنَّـٰتِ ٱلنَّعِيمِ

A cikin gidajen Aljanna na ni’ima



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 44

عَلَىٰ سُرُرٖ مُّتَقَٰبِلِينَ

A kan gadaje suna fuskantar juna



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 45

يُطَافُ عَلَيۡهِم بِكَأۡسٖ مِّن مَّعِينِۭ

Ana zagaya su da kofuna na giya



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 46

بَيۡضَآءَ لَذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ

Fara fat, ga kuma daxi ga masu sha



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 47

لَا فِيهَا غَوۡلٞ وَلَا هُمۡ عَنۡهَا يُنزَفُونَ

Babu sa ciwon kai a gare ta, kuma ba za a bugar da su da ita ba



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 48

وَعِندَهُمۡ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ عِينٞ

A wurinsu kuma akwai mataye masu taqaita kallonsu ga mazajensu, masu qwala-qwalan ido



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 49

كَأَنَّهُنَّ بَيۡضٞ مَّكۡنُونٞ

Kai ka ce su wani qwai ne a cikin kwasfa



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 50

فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَسَآءَلُونَ

Sannan sashinsu ya fuskanci shashi suna tambayar juna



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 51

قَالَ قَآئِلٞ مِّنۡهُمۡ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٞ

Wani daga cikinsu ya ce: “Lalle a da can ina da wani aboki



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 52

يَقُولُ أَءِنَّكَ لَمِنَ ٱلۡمُصَدِّقِينَ

“Da yake cewa: ‘Yanzu kai kana cikin masu ba da gaskiya?



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 53

أَءِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَدِينُونَ

“Yanzu idan muka mutu muka zama qasa da qasusuwa shin ko za a iya yi mana wani sakamako?’”



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 54

قَالَ هَلۡ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ

Ya ce: “Shin ko za ku leqa ne?”



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 55

فَٱطَّلَعَ فَرَءَاهُ فِي سَوَآءِ ٱلۡجَحِيمِ

Sai shi ya leqa, sai kuwa ya gan shi a tsakiyar wuta



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 56

قَالَ تَٱللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرۡدِينِ

Ya ce: “Wallahi ka kusa ka hallakar da ni



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 57

وَلَوۡلَا نِعۡمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ ٱلۡمُحۡضَرِينَ

“Ba don rahamar Ubangijina ba, da lalle ni ma na zama cikin ‘yan wuta.”



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 58

أَفَمَا نَحۡنُ بِمَيِّتِينَ

(Sai ‘yan Aljanna su ce da juna): “Ashe yanzu ba za mu sake mutuwa ba?



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 59

إِلَّا مَوۡتَتَنَا ٱلۡأُولَىٰ وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ

“Sai fa mutuwarmu ta farko, ba kuma za a azabtar da mu ba?”



Capítulo: Suratus Saffat

Verso : 60

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

Lalle wannan shi ne babban rabo