Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 31

ثُمَّ أَنشَأۡنَا مِنۢ بَعۡدِهِمۡ قَرۡنًا ءَاخَرِينَ

Sannan kuma a bayansu Muka halicci wata al’umma daban



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 32

فَأَرۡسَلۡنَا فِيهِمۡ رَسُولٗا مِّنۡهُمۡ أَنِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥٓۚ أَفَلَا تَتَّقُونَ

Sai Muka aiko musu wani manzon daga cikinsu da cewa: “Ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta in ba Shi ba; me ya sa ne ba za ku yi taqawa ba?”



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 33

وَقَالَ ٱلۡمَلَأُ مِن قَوۡمِهِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَكَذَّبُواْ بِلِقَآءِ ٱلۡأٓخِرَةِ وَأَتۡرَفۡنَٰهُمۡ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا مَا هَٰذَآ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡ يَأۡكُلُ مِمَّا تَأۡكُلُونَ مِنۡهُ وَيَشۡرَبُ مِمَّا تَشۡرَبُونَ

Kuma manyan mutane daga cikin mutanensa waxanda suka kafirce suka kuma qaryata haxuwa da ranar lahira, Muka kuma wadata su a rayuwar duniya, suka ce: “Wannan ba kowa ba ne face mutum kamarku, yana cin irin abin da kuke ci, yana kuma shan irin abin da kuke sha



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 34

وَلَئِنۡ أَطَعۡتُم بَشَرٗا مِّثۡلَكُمۡ إِنَّكُمۡ إِذٗا لَّخَٰسِرُونَ

“Kuma tabbas in har kuka bi mutum kamarku, to lalle tabbas a sannan kun yi asara



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 35

أَيَعِدُكُمۡ أَنَّكُمۡ إِذَا مِتُّمۡ وَكُنتُمۡ تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَنَّكُم مُّخۡرَجُونَ

“Shin yanzu ya riqa yi muku alqawarin cewa idan kun mutu kun kuma zama turvaya da qasusuwa cewa lalle za a tashe ku?”



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 36

۞هَيۡهَاتَ هَيۡهَاتَ لِمَا تُوعَدُونَ

“Faufau-faufau game da abin da ake yi muku alqawarinsa!



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 37

إِنۡ هِيَ إِلَّا حَيَاتُنَا ٱلدُّنۡيَا نَمُوتُ وَنَحۡيَا وَمَا نَحۡنُ بِمَبۡعُوثِينَ

“Ba mu da wata (rayuwa) sai rayuwarmu ta duniya; mu mutu kuma mu rayu, ba kuwa za a tashe mu (daga qaburburanmu) ba



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 38

إِنۡ هُوَ إِلَّا رَجُلٌ ٱفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبٗا وَمَا نَحۡنُ لَهُۥ بِمُؤۡمِنِينَ

“Shi ba kowa ba ne face mutum da ya qaga wa Allah qarya, mu kuwa ba za mu yi imani da shi ba.”



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 39

قَالَ رَبِّ ٱنصُرۡنِي بِمَا كَذَّبُونِ

Ya ce: “Ya Ubangijina, Ka taimake ni game da abin da suke qaryata ni a kansa.”



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 40

قَالَ عَمَّا قَلِيلٖ لَّيُصۡبِحُنَّ نَٰدِمِينَ

Ya ce: “Ba da daxewa ba tabbas za su wayi gari suna masu nadama.”



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 41

فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّيۡحَةُ بِٱلۡحَقِّ فَجَعَلۡنَٰهُمۡ غُثَآءٗۚ فَبُعۡدٗا لِّلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Sai tsawa ta far musu bisa cancanta, sai Muka mai da su dudduga. To nisanta (daga rahamar Allah) ta tabbata ga mutane azzalumai



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 42

ثُمَّ أَنشَأۡنَا مِنۢ بَعۡدِهِمۡ قُرُونًا ءَاخَرِينَ

Sannan kuma a bayansu Muka halitta wasu al’ummun daban



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 43

مَا تَسۡبِقُ مِنۡ أُمَّةٍ أَجَلَهَا وَمَا يَسۡتَـٔۡخِرُونَ

Babu wata al’umma da take rigayar ajalinta, babu kuma wadda take jinkiri



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 44

ثُمَّ أَرۡسَلۡنَا رُسُلَنَا تَتۡرَاۖ كُلَّ مَا جَآءَ أُمَّةٗ رَّسُولُهَا كَذَّبُوهُۖ فَأَتۡبَعۡنَا بَعۡضَهُم بَعۡضٗا وَجَعَلۡنَٰهُمۡ أَحَادِيثَۚ فَبُعۡدٗا لِّقَوۡمٖ لَّا يُؤۡمِنُونَ

Sannan Muka aiko manzanninmu suna biye da juna; duk sanda manzon (kowacce) al’umma ya zo musu sai su qaryata shi. Sai Muka hallaka su xaya bayan xaya, Muka kuma mai da su tarihi. To nisanta (daga rahamar Allah) ta tabbata ga mutanen da ba sa yin imani



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 45

ثُمَّ أَرۡسَلۡنَا مُوسَىٰ وَأَخَاهُ هَٰرُونَ بِـَٔايَٰتِنَا وَسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٍ

Sannan Muka aiko Musa da xan’uwansa Haruna da ayoyinmu da kuma hujja bayyananniya



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 46

إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ وَمَلَإِيْهِۦ فَٱسۡتَكۡبَرُواْ وَكَانُواْ قَوۡمًا عَالِينَ

Zuwa ga Fir’auna da manyan (‘yan majalisarsa), sai suka yi girman kai kuma suka kasance mutane masu haike wa (jama’a da zalunci)



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 47

فَقَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لِبَشَرَيۡنِ مِثۡلِنَا وَقَوۡمُهُمَا لَنَا عَٰبِدُونَ

Sai suka ce: “Yanzu ma ba da gaskiya da mutum biyu irinmu, alhali kuwa mutanensu masu yi mana bauta ne?”



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 48

فَكَذَّبُوهُمَا فَكَانُواْ مِنَ ٱلۡمُهۡلَكِينَ

Sai suka qaryata su (wato Musa da Haruna), sannan suka kasance daga waxanda aka hallaka



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 49

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ لَعَلَّهُمۡ يَهۡتَدُونَ

Haqiqa kuma Mun bai wa Musa Littafi (wato Attaura) don su shiriya



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 50

وَجَعَلۡنَا ٱبۡنَ مَرۡيَمَ وَأُمَّهُۥٓ ءَايَةٗ وَءَاوَيۡنَٰهُمَآ إِلَىٰ رَبۡوَةٖ ذَاتِ قَرَارٖ وَمَعِينٖ

Muka kuma sanya Xan Maryamu da mahaifiyarsa (don su zama) aya, Muka kuma zaunar da su a wata jigawa ta hutawa da kuma ruwa mai gudana



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 51

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلرُّسُلُ كُلُواْ مِنَ ٱلطَّيِّبَٰتِ وَٱعۡمَلُواْ صَٰلِحًاۖ إِنِّي بِمَا تَعۡمَلُونَ عَلِيمٞ

Ya ku manzanni, ku ci daga halal, kuma ku yi aiki na gari; Lalle Ni ina sane da abin da kuke aikatawa



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 52

وَإِنَّ هَٰذِهِۦٓ أُمَّتُكُمۡ أُمَّةٗ وَٰحِدَةٗ وَأَنَا۠ رَبُّكُمۡ فَٱتَّقُونِ

Kuma lalle wannan addininku ne, addini guda xaya (wato Musulunci), kuma Ni ne Ubangijinku, sai ku kiyaye dokokina



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 53

فَتَقَطَّعُوٓاْ أَمۡرَهُم بَيۡنَهُمۡ زُبُرٗاۖ كُلُّ حِزۡبِۭ بِمَا لَدَيۡهِمۡ فَرِحُونَ

Sai suka sassava al’amarinsu a tsakaninsu (suka kasu) qungiya-qungiya; kowacce qungiya tana alfahari da nata



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 54

فَذَرۡهُمۡ فِي غَمۡرَتِهِمۡ حَتَّىٰ حِينٍ

Sai ka bar su cikin ximuwarsu har zuwa xan wani lokaci



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 55

أَيَحۡسَبُونَ أَنَّمَا نُمِدُّهُم بِهِۦ مِن مَّالٖ وَبَنِينَ

Yanzu suna tsammanin cewa abin da Muke ba su na dukiya da ‘ya’yaye (a duniya)



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 56

نُسَارِعُ لَهُمۡ فِي ٱلۡخَيۡرَٰتِۚ بَل لَّا يَشۡعُرُونَ

Muna gaggauto musu sakamakon alheri ne? Ba haka ba ne; su dai ba sa ganewa ne



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 57

إِنَّ ٱلَّذِينَ هُم مِّنۡ خَشۡيَةِ رَبِّهِم مُّشۡفِقُونَ

Lalle waxanda su suke cike da tsoron Ubangijinsu



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 58

وَٱلَّذِينَ هُم بِـَٔايَٰتِ رَبِّهِمۡ يُؤۡمِنُونَ

Kuma waxanda suke imani da ayoyin Ubangijinsu



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 59

وَٱلَّذِينَ هُم بِرَبِّهِمۡ لَا يُشۡرِكُونَ

Kuma waxanda ba sa shirka da Ubangijinsu



Capítulo: Suratul Mu’uminun

Verso : 60

وَٱلَّذِينَ يُؤۡتُونَ مَآ ءَاتَواْ وَّقُلُوبُهُمۡ وَجِلَةٌ أَنَّهُمۡ إِلَىٰ رَبِّهِمۡ رَٰجِعُونَ

Kuma waxanda suke ba da abin da suka bayar (na ayyukan kirki), alhali kuwa zukatansu suna tsorace[1], don kuwa lalle su masu komawa ne zuwa ga Ubangijinsu


1- Watau suna cike da tsoron za a karva ko ba za a karva ba.