Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 49

إِذۡ يَقُولُ ٱلۡمُنَٰفِقُونَ وَٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٌ غَرَّ هَـٰٓؤُلَآءِ دِينُهُمۡۗ وَمَن يَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِ فَإِنَّ ٱللَّهَ عَزِيزٌ حَكِيمٞ

Ka tuna lokacin da munafuqai da kuma waxanda suke da rauni a zukatansu suke cewa: “Waxannan addininsu ne ya ruxe su.” Duk wanda ya dogara ga Allah kuwa to lalle Allah Mabuwayi ne Mai hikima



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 52

كَدَأۡبِ ءَالِ فِرۡعَوۡنَ وَٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۚ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ فَأَخَذَهُمُ ٱللَّهُ بِذُنُوبِهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ قَوِيّٞ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

(Al’adar kafiran Makka) kamar al’adar mutanen Fir’auna ce da kuma waxanda suke gabaninsu. Sun kafirce wa ayoyin Allah, saboda haka Allah Ya kama su da zunubansu. Lalle Allah Mai qarfi ne, Mai tsananin uquba



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 53

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ لَمۡ يَكُ مُغَيِّرٗا نِّعۡمَةً أَنۡعَمَهَا عَلَىٰ قَوۡمٍ حَتَّىٰ يُغَيِّرُواْ مَا بِأَنفُسِهِمۡ وَأَنَّ ٱللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٞ

Wannan (kuwa) saboda Allah bai kasance Mai canza wata ni’ima da Ya yi wa wasu mutane ba har sai sun canja halayensu, lalle Allah kuma Mai ji ne Masani



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 60

وَأَعِدُّواْ لَهُم مَّا ٱسۡتَطَعۡتُم مِّن قُوَّةٖ وَمِن رِّبَاطِ ٱلۡخَيۡلِ تُرۡهِبُونَ بِهِۦ عَدُوَّ ٱللَّهِ وَعَدُوَّكُمۡ وَءَاخَرِينَ مِن دُونِهِمۡ لَا تَعۡلَمُونَهُمُ ٱللَّهُ يَعۡلَمُهُمۡۚ وَمَا تُنفِقُواْ مِن شَيۡءٖ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ يُوَفَّ إِلَيۡكُمۡ وَأَنتُمۡ لَا تُظۡلَمُونَ

Ku yi musu tanadin abin da kuke iyawa na qarfi da kuma tanadin xaurarrun dawakai, kuna tsorata maqiya Allah kuma maqiyanku da shi (tanadin), har kuma da wasu ban da su da ba ku san su ba, Allah ne kawai Ya san su. Kuma duk irin abin da kuka ciyar cikin hanyar Allah za a cika muku (ladanku) ba kuwa za a zalunce ku ba



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 61

۞وَإِن جَنَحُواْ لِلسَّلۡمِ فَٱجۡنَحۡ لَهَا وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱللَّهِۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Idan kuma suka karkato ga sulhu, to sai kai ma ka karkato gare shi, ka kuma dogara ga Allah. Lalle Shi Mai ji ne Masani



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 70

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ قُل لِّمَن فِيٓ أَيۡدِيكُم مِّنَ ٱلۡأَسۡرَىٰٓ إِن يَعۡلَمِ ٱللَّهُ فِي قُلُوبِكُمۡ خَيۡرٗا يُؤۡتِكُمۡ خَيۡرٗا مِّمَّآ أُخِذَ مِنكُمۡ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ya kai wannan Annabi, ka ce da fursunonin da suke a hannayenku: “Idan dai har Allah Ya san akwai wani alheri a zukatanku, to zai ba ku fiye da abin da aka karva daga wurinku Ya kuma gafarta muku. Allah kuwa Mai gafara ne Mai jin qai.”



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 18

إِنَّمَا يَعۡمُرُ مَسَٰجِدَ ٱللَّهِ مَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَأَقَامَ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتَى ٱلزَّكَوٰةَ وَلَمۡ يَخۡشَ إِلَّا ٱللَّهَۖ فَعَسَىٰٓ أُوْلَـٰٓئِكَ أَن يَكُونُواْ مِنَ ٱلۡمُهۡتَدِينَ

Lalle mai raya masallatan Allah shi ne kawai wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira ya kuma tsayar da salla, kuma ya ba da zakka, bai kuma ji tsoron wani ba sai Allah. To waxannan tabbas suna cikin shiryayyu



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 19

۞أَجَعَلۡتُمۡ سِقَايَةَ ٱلۡحَآجِّ وَعِمَارَةَ ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِ كَمَنۡ ءَامَنَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَجَٰهَدَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۚ لَا يَسۡتَوُۥنَ عِندَ ٱللَّهِۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Yanzu kwa mayar da shayar da alhazai da raya Masallaci mai alfarma kamar wanda ya yi imani da Allah da ranar lahira ya kuma yi jihadi saboda Allah? Ai ba za su zama xaya ba a wurin Allah. Allah kuma ba Ya shiryar da mutane azzalumai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 20

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَهَاجَرُواْ وَجَٰهَدُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡ أَعۡظَمُ دَرَجَةً عِندَ ٱللَّهِۚ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡفَآئِزُونَ

Waxanda suka yi imani kuma suka yi hijira suka yi jihadi saboda Allah da dukiyoyinsu da kawunansu su suka fi girman daraja a wurin Allah kuma waxannan su ne marabauta



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 27

ثُمَّ يَتُوبُ ٱللَّهُ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ عَلَىٰ مَن يَشَآءُۗ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Sannan bayan wannan Allah zai karvi tuban wanda Ya ga dama. Allah kuwa Mai gafara ne, Mai rahama



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 31

ٱتَّخَذُوٓاْ أَحۡبَارَهُمۡ وَرُهۡبَٰنَهُمۡ أَرۡبَابٗا مِّن دُونِ ٱللَّهِ وَٱلۡمَسِيحَ ٱبۡنَ مَرۡيَمَ وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُوٓاْ إِلَٰهٗا وَٰحِدٗاۖ لَّآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۚ سُبۡحَٰنَهُۥ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Sun xauki malamansu da masu ibadarsu da kuma Almasihu xan Maryamu iyayen giji maimakon Allah[1], alhali kuwa ba abin da aka umarce su sai su bauta wa Abin bauta Xaya, babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi. Ya tsarkaka daga abin da suke tara Shi da shi


1- Watau suna yi wa malamansu da masu bauta a cikinsu makauniyar biyayya, suna haramta musu halal, su kuma halatta musu haram. Nasara sun xauki Annabi Isa () abin bauta ba Allah ba.


Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 39

إِلَّا تَنفِرُواْ يُعَذِّبۡكُمۡ عَذَابًا أَلِيمٗا وَيَسۡتَبۡدِلۡ قَوۡمًا غَيۡرَكُمۡ وَلَا تَضُرُّوهُ شَيۡـٔٗاۗ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Idan ba za ku fita (yaqi ba to (Allah) zai azabtar da ku da azaba mai raxaxi, Ya kuma canja wasu mutanen daban, ba kuwa za ku cutar da Shi da komai ba. Allah kuwa Mai iko ne a kan komai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 44

لَا يَسۡتَـٔۡذِنُكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ أَن يُجَٰهِدُواْ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلۡمُتَّقِينَ

Waxanda suka yi imani da Allah da ranar lahira ba sa neman izininka don kada su yi yaqi da dukiyoyinsu da kawunansu. Allah kuwa yana sane da masu taqawa



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 47

لَوۡ خَرَجُواْ فِيكُم مَّا زَادُوكُمۡ إِلَّا خَبَالٗا وَلَأَوۡضَعُواْ خِلَٰلَكُمۡ يَبۡغُونَكُمُ ٱلۡفِتۡنَةَ وَفِيكُمۡ سَمَّـٰعُونَ لَهُمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلظَّـٰلِمِينَ

Da sun fito cikinku xin, to ba abin da za su qare ku da shi sai tavarvarewa, kuma lalle da sun yi ta shige da fice a tsakaninku suna qoqarin haifar muku da fitina, a cikinku kuma akwai masu jiyo musu (wato abokan gaba) magana. Allah kuwa Masanin azzalumai ne



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 51

قُل لَّن يُصِيبَنَآ إِلَّا مَا كَتَبَ ٱللَّهُ لَنَا هُوَ مَوۡلَىٰنَاۚ وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ

Ka ce: “Ba abin da zai same mu sai abin da Allah Ya rubuta mana, shi ne Majivincin al’amuranmu; kuma ga Allah kaxai muminai sai su dogara.”



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 61

وَمِنۡهُمُ ٱلَّذِينَ يُؤۡذُونَ ٱلنَّبِيَّ وَيَقُولُونَ هُوَ أُذُنٞۚ قُلۡ أُذُنُ خَيۡرٖ لَّكُمۡ يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَيُؤۡمِنُ لِلۡمُؤۡمِنِينَ وَرَحۡمَةٞ لِّلَّذِينَ ءَامَنُواْ مِنكُمۡۚ وَٱلَّذِينَ يُؤۡذُونَ رَسُولَ ٱللَّهِ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Daga cikinsu kuma akwai waxanda suke cutar Annabi suna kuma cewa: “Shi mai saurare ne kawai[1].” Ka ce (da su: Shi) “Mai sauraren alheri ne dominku; yana imani da Allah, yana kuma gaskata muminai, kuma rahama ne ga waxanda suka yi imani daga cikinku.” Waxanda kuwa suke cutar Manzon Allah suna da azaba mai raxaxi


1- Wai shi mai xaukar maganganu ne kawai yana yarda da su ba tare da ya tantance gaskiyarsu da rashinta ba.


Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 78

أَلَمۡ يَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ سِرَّهُمۡ وَنَجۡوَىٰهُمۡ وَأَنَّ ٱللَّهَ عَلَّـٰمُ ٱلۡغُيُوبِ

Yanzu ba su sani ba cewa, lalle Allah Ya san asirinsu da kuma ganawar da suke yi, lalle kuma Allah Shi ne cikakken Masanin gaibu?



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 99

وَمِنَ ٱلۡأَعۡرَابِ مَن يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَيَتَّخِذُ مَا يُنفِقُ قُرُبَٰتٍ عِندَ ٱللَّهِ وَصَلَوَٰتِ ٱلرَّسُولِۚ أَلَآ إِنَّهَا قُرۡبَةٞ لَّهُمۡۚ سَيُدۡخِلُهُمُ ٱللَّهُ فِي رَحۡمَتِهِۦٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Daga mutanen qauye xin kuma akwai waxanda suke yin imani da Allah da ranar lahira, suke kuma xaukar abin da suke ciyarwa (hanyoyi ne) na samun kusanci ga Allah da kuma addu’o’in Manzo. Lalle wannan ibada ce gare su. Allah zai shigar da su cikin rahamarsa. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 101

وَمِمَّنۡ حَوۡلَكُم مِّنَ ٱلۡأَعۡرَابِ مُنَٰفِقُونَۖ وَمِنۡ أَهۡلِ ٱلۡمَدِينَةِ مَرَدُواْ عَلَى ٱلنِّفَاقِ لَا تَعۡلَمُهُمۡۖ نَحۡنُ نَعۡلَمُهُمۡۚ سَنُعَذِّبُهُم مَّرَّتَيۡنِ ثُمَّ يُرَدُّونَ إِلَىٰ عَذَابٍ عَظِيمٖ

Kuma daga mutanen qauye waxanda suke kewaye da ku akwai munafukai, haka kuma daga mutan Madina; sun qware a kan munafunci, kai ba ka san su ba; Mu ne Muka san su. Za Mu azabtar da su sau biyu, sannan a komar da su zuwa ga azaba mai girma



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 102

وَءَاخَرُونَ ٱعۡتَرَفُواْ بِذُنُوبِهِمۡ خَلَطُواْ عَمَلٗا صَٰلِحٗا وَءَاخَرَ سَيِّئًا عَسَى ٱللَّهُ أَن يَتُوبَ عَلَيۡهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

Wasu kuwa sun yi iqirari da laifinsu, sun gauraya kyakkyawan aiki da wani mummuna, to tabbas Allah zai karvi tubansu. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 104

أَلَمۡ يَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ هُوَ يَقۡبَلُ ٱلتَّوۡبَةَ عَنۡ عِبَادِهِۦ وَيَأۡخُذُ ٱلصَّدَقَٰتِ وَأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Shin yanzu ba su sani ba ne cewa Allah Shi Yake karvar tuba daga bayinsa Yake kuma karvar sadakoki, kuma lalle Shi ne Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai?



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 105

وَقُلِ ٱعۡمَلُواْ فَسَيَرَى ٱللَّهُ عَمَلَكُمۡ وَرَسُولُهُۥ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَۖ وَسَتُرَدُّونَ إِلَىٰ عَٰلِمِ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِ فَيُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Ka kuma ce: “Ku yi aiki, Allah ne zai ga aikinku shi da Manzonsa da kuma muminai, kuma za a mayar da ku zuwa ga Masanin abin da yake voye da na sarari, sannan Ya ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 115

وَمَا كَانَ ٱللَّهُ لِيُضِلَّ قَوۡمَۢا بَعۡدَ إِذۡ هَدَىٰهُمۡ حَتَّىٰ يُبَيِّنَ لَهُم مَّا يَتَّقُونَۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٌ

Allah kuwa ba zai tava vatar da wasu mutane ba bayan Ya riga Ya shiryar da su, har sai Ya bayyana musu abin da za su kiyaye. Lalle Allah Masanin komai ne



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 116

إِنَّ ٱللَّهَ لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ يُحۡيِۦ وَيُمِيتُۚ وَمَا لَكُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ مِن وَلِيّٖ وَلَا نَصِيرٖ

Lalle Allah Shi ne Mai mulkin sammai da qasa, Yana rayawa kuma Yana kashewa. Ba ku da wani majivincin lamarinku in ban da Allah, ba ku kuma da wani mai taimako



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 117

لَّقَد تَّابَ ٱللَّهُ عَلَى ٱلنَّبِيِّ وَٱلۡمُهَٰجِرِينَ وَٱلۡأَنصَارِ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُوهُ فِي سَاعَةِ ٱلۡعُسۡرَةِ مِنۢ بَعۡدِ مَا كَادَ يَزِيغُ قُلُوبُ فَرِيقٖ مِّنۡهُمۡ ثُمَّ تَابَ عَلَيۡهِمۡۚ إِنَّهُۥ بِهِمۡ رَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Tabbas haqiqa Allah Ya yafe wa Annabi da masu hijira da kuma Ansaru waxanda suka bi shi a lokacin tsanani bayan har zukatan wasu qungiyoyi daga cikinsu sun kusa su karkace, sannan (Allah) Ya karvi tubansu. Lalle Shi Mai tausasawa ne, Mai jin qai a gare su



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 118

وَعَلَى ٱلثَّلَٰثَةِ ٱلَّذِينَ خُلِّفُواْ حَتَّىٰٓ إِذَا ضَاقَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلۡأَرۡضُ بِمَا رَحُبَتۡ وَضَاقَتۡ عَلَيۡهِمۡ أَنفُسُهُمۡ وَظَنُّوٓاْ أَن لَّا مَلۡجَأَ مِنَ ٱللَّهِ إِلَّآ إِلَيۡهِ ثُمَّ تَابَ عَلَيۡهِمۡ لِيَتُوبُوٓاْۚ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma (Ya yafe wa) mutanen nan guda uku waxanda aka dakatar da karvar tubansu[1], har sai yayin da duniya ta yi musu qunci duk da yalwarta, kuma zukatansu suka quntata, suka tabbatar da cewa dai babu wata mafaka daga Allah sai dai a wajensa. Sannan sai Ya yi musu muwafaqar tuba don su tuba. Lalle Allah Shi ne Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai


1- Su ne sahabban nan uku, watau Ka’abu xan Maliku da Muraratu xan Rabi’atu da Hilal xan Umayyatu Al-Waqifi. Sun qi fita yaqin Tabuka tare da Annabi () ba tare da wani uzuri ba.


Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 129

فَإِن تَوَلَّوۡاْ فَقُلۡ حَسۡبِيَ ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ عَلَيۡهِ تَوَكَّلۡتُۖ وَهُوَ رَبُّ ٱلۡعَرۡشِ ٱلۡعَظِيمِ

To idan sun ba da baya sai ka ce: “Allah Ya ishe ni, babu wani abin bautawa da gaskiya sai Shi, a gare Shi kaxai na dogara; kuma Shi ne Ubangijin Al’arshi mai girma.”



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 3

إِنَّ رَبَّكُمُ ٱللَّهُ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰ عَلَى ٱلۡعَرۡشِۖ يُدَبِّرُ ٱلۡأَمۡرَۖ مَا مِن شَفِيعٍ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ إِذۡنِهِۦۚ ذَٰلِكُمُ ٱللَّهُ رَبُّكُمۡ فَٱعۡبُدُوهُۚ أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

Lalle Ubangijinku Shi ne Allah wanda Ya halicci sammai da qasa cikin kwana shida, sannan Ya daidaita a kan Al’arshi[1]; Yana tsara al’amari (yadda Ya ga dama). Babu wani mai ceto sai da izininsa. Wannan Shi ne Allah Ubangijinku. To sai ku bauta masa. Ashe ba za ku wa’azantu ba?


1- Duba Suratul A’araf aya ta 54. hashiya ta 126.


Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 4

إِلَيۡهِ مَرۡجِعُكُمۡ جَمِيعٗاۖ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقًّاۚ إِنَّهُۥ يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥ لِيَجۡزِيَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ بِٱلۡقِسۡطِۚ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَهُمۡ شَرَابٞ مِّنۡ حَمِيمٖ وَعَذَابٌ أَلِيمُۢ بِمَا كَانُواْ يَكۡفُرُونَ

Zuwa gare Shi ne makomarku take gaba xaya; alqawarin Allah ne da gaske. Lalle Shi ne Yake farar da halitta sannan Ya maido da ita (bayan mutuwa) don Ya saka wa waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki nagari da adalci. Waxanda suka kafirce kuwa suna da abin sha mai tsananin quna da kuma azaba mai raxaxi saboda kafircewa da suke yi



Capítulo: Suratu Yunus

Verso : 5

هُوَ ٱلَّذِي جَعَلَ ٱلشَّمۡسَ ضِيَآءٗ وَٱلۡقَمَرَ نُورٗا وَقَدَّرَهُۥ مَنَازِلَ لِتَعۡلَمُواْ عَدَدَ ٱلسِّنِينَ وَٱلۡحِسَابَۚ مَا خَلَقَ ٱللَّهُ ذَٰلِكَ إِلَّا بِٱلۡحَقِّۚ يُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ لِقَوۡمٖ يَعۡلَمُونَ

Shi ne Wanda Ya sanya muku rana ta zamo mai haske da kuma wata ya zamo mai haskakawa, Ya kuma sanya shi mai masaukai don ku san adadin shekaru da kuma (sanin) lissafi (na lokuta). Allah bai halicci wannan ba sai da gaskiya. Yana bayyana ayoyi ne ga mutanen da suke da sani