Capítulo: Suratux Xariq

Verso : 8

إِنَّهُۥ عَلَىٰ رَجۡعِهِۦ لَقَادِرٞ

Lalle Shi (Allah) Mai iko ne a kan dawo da shi



Capítulo: Suratul A’ala

Verso : 7

إِلَّا مَا شَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلۡجَهۡرَ وَمَا يَخۡفَىٰ

Sai abin da Allah Ya ga dama, Lalle Shi Yana sane da bayyanannen (abu) da kuma abin da yake vuya



Capítulo: Suratud Dhuha

Verso : 11

وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ

Amma kuma game da ni’imar Ubangijinka sai ka ba da labari



Capítulo: Suratul Alaq

Verso : 14

أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?



Capítulo: Suratul Bayyina

Verso : 5

وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ

Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya



Capítulo: Suratun Nasr

Verso : 3

فَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ وَٱسۡتَغۡفِرۡهُۚ إِنَّهُۥ كَانَ تَوَّابَۢا

To ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka, ka kuma nemi gafararsa. Lalle Shi Ya kasance Mai karvar tuba ne



Capítulo: Suratul Ikhlas

Verso : 1

قُلۡ هُوَ ٱللَّهُ أَحَدٌ

Ka ce: “Shi Allah Xaya ne[1]


1- Watau a Zatinsa da siffofinsa da ayyukansa, kuma shi kaxai ya cancanci a bauta masa.


Capítulo: Suratul Ikhlas

Verso : 2

ٱللَّهُ ٱلصَّمَدُ

“Allah Abin nufa da buqatu[1]


1- Watau wanda shugabanci ya tuqe zuwa gare shi, domin ya tattara dukkan siffofin kamala da xaukaka.


Capítulo: Suratul Ikhlas

Verso : 3

لَمۡ يَلِدۡ وَلَمۡ يُولَدۡ

“Bai haifa ba, kuma ba a haife Shi ba



Capítulo: Suratul Ikhlas

Verso : 4

وَلَمۡ يَكُن لَّهُۥ كُفُوًا أَحَدُۢ

“Kuma babu wani da ya kasance kini a gare Shi[1].”


1- Domin babu mai kama da shi a sunayensa da siffofinsa da ayyukansa.


Capítulo: Suratun Nas

Verso : 2

مَلِكِ ٱلنَّاسِ

“Sarkin mutane