إِلَٰهُكُمۡ إِلَٰهٞ وَٰحِدٞۚ فَٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ قُلُوبُهُم مُّنكِرَةٞ وَهُم مُّسۡتَكۡبِرُونَ
Abin bautarku Abin bauta ne Xaya, sai dai waxanda ba sa yin imani da ranar lahira zukatansu masu musun hakan ne, kuma su masu girman kai ne
وَمَا نُرۡسِلُ ٱلۡمُرۡسَلِينَ إِلَّا مُبَشِّرِينَ وَمُنذِرِينَۚ وَيُجَٰدِلُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِٱلۡبَٰطِلِ لِيُدۡحِضُواْ بِهِ ٱلۡحَقَّۖ وَٱتَّخَذُوٓاْ ءَايَٰتِي وَمَآ أُنذِرُواْ هُزُوٗا
Ba Mu kuma aiko da manzanni ba sai don su zama masu albishir mai gargaxi. Su kuma waxanda suka kafirce sai su dinga jayayya da qarya don su kawar da gaskiya da ita; suka kuma riqi ayoyina da kuma abin da aka yi musu gargaxi da shi a matsayin abin izgili
أَلَمۡ تَرَ أَنَّآ أَرۡسَلۡنَا ٱلشَّيَٰطِينَ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ تَؤُزُّهُمۡ أَزّٗا
Shin ba ka san Mu Muka xora shaixanu a kan kafirai ba suna ingiza su (cikin vata) ingizawa?
وَلَا يَزَالُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي مِرۡيَةٖ مِّنۡهُ حَتَّىٰ تَأۡتِيَهُمُ ٱلسَّاعَةُ بَغۡتَةً أَوۡ يَأۡتِيَهُمۡ عَذَابُ يَوۡمٍ عَقِيمٍ
Waxanda kuwa suka kafirce ba za su daina kokwanton sa ba (watau Alqur’ani) har sai alqiyama ta zo musu ba zato ba tsammani, ko kuma azabar rana bakarara[1] ta zo musu
1- Watau ranar da kafirai ba za su samu wata rahama ko wani alheri ba.
وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ تَعۡرِفُ فِي وُجُوهِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلۡمُنكَرَۖ يَكَادُونَ يَسۡطُونَ بِٱلَّذِينَ يَتۡلُونَ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتِنَاۗ قُلۡ أَفَأُنَبِّئُكُم بِشَرّٖ مِّن ذَٰلِكُمُۚ ٱلنَّارُ وَعَدَهَا ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ
Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu bayyanannu, to za ka ga alamar musantawa a fuskokin waxanda suka kafirta, suna kamar za su auka wa waxanda suke karanta musu ayoyinmu. To ka ce: “Shin ba na ba ku labarin abin da ya fi wannan muni ba[1]? Wuta ce da Allah Ya yi alqawari ga waxanda suka kafirta; makoma kuwa ta munana.”
1- Watau fiye da abin da suke ganin muninsa idan ana karanta musu shi, watau ayoyin Alqur’ani.
وَمَن يَدۡعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ لَا بُرۡهَٰنَ لَهُۥ بِهِۦ فَإِنَّمَا حِسَابُهُۥ عِندَ رَبِّهِۦٓۚ إِنَّهُۥ لَا يُفۡلِحُ ٱلۡكَٰفِرُونَ
Duk wanda ya bauta wa wani abin bauta tare da Allah ba da wata hujja ba game da (wannan bautar), to sakamakonsa wajen Ubangijinsa kawai yake. Lalle su dai kafirai ba za su rabauta ba
إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ زَيَّنَّا لَهُمۡ أَعۡمَٰلَهُمۡ فَهُمۡ يَعۡمَهُونَ
Lalle waxanda ba sa imani da ranar lahira Mun qawata musu ayyukansu, don haka suke ximuwa
وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَءِذَا كُنَّا تُرَٰبٗا وَءَابَآؤُنَآ أَئِنَّا لَمُخۡرَجُونَ
Waxanda suka kafirta, kuma suka ce: “Yanzu bayan mun zama qasa mu da iyayenmu, ashe lalle za a (sake) fito da mu?
لَقَدۡ وُعِدۡنَا هَٰذَا نَحۡنُ وَءَابَآؤُنَا مِن قَبۡلُ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّآ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
“Haqiqa an yi mana alqawarin wannan mu da iyayenmu tun a da can, wannan ba komai ba ne face tatsuniyoyin mutanen farko.”
وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَلِقَآئِهِۦٓ أُوْلَـٰٓئِكَ يَئِسُواْ مِن رَّحۡمَتِي وَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ
Waxanda kuma suka kafirce wa ayoyin Allah da kuma gamuwa da Shi, waxannan sun xebe qauna daga rahamata, kuma waxannan suna da azaba mai raxaxi
هُوَ ٱلَّذِي جَعَلَكُمۡ خَلَـٰٓئِفَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ فَمَن كَفَرَ فَعَلَيۡهِ كُفۡرُهُۥۖ وَلَا يَزِيدُ ٱلۡكَٰفِرِينَ كُفۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ إِلَّا مَقۡتٗاۖ وَلَا يَزِيدُ ٱلۡكَٰفِرِينَ كُفۡرُهُمۡ إِلَّا خَسَارٗا
Shi ne wanda Ya sanya ku halifofi a bayan qasa. Saboda haka wanda ya kafirta sakamakon kafircinsa yana kansa, kuma kafircin kafirai ba zai qara musu komai ba a wurin Ubangijinsu sai qiyayya; kuma kafircin kafirai ba zai qara musu komai ba sai hasara
بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي عِزَّةٖ وَشِقَاقٖ
Sai dai waxanda suka kafirta suna cikin girman kai ne da jayayya
وَإِذَا ذُكِرَ ٱللَّهُ وَحۡدَهُ ٱشۡمَأَزَّتۡ قُلُوبُ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِۖ وَإِذَا ذُكِرَ ٱلَّذِينَ مِن دُونِهِۦٓ إِذَا هُمۡ يَسۡتَبۡشِرُونَ
Idan kuma aka ambaci Allah Shi kaxai sai zukatan waxanda ba sa ba da gaskiya da ranar lahira su takura; idan kuwa aka ambaci waxanda suke ba Shi ba sai ka gan su suna ta walwala
مَا يُجَٰدِلُ فِيٓ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ إِلَّا ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَلَا يَغۡرُرۡكَ تَقَلُّبُهُمۡ فِي ٱلۡبِلَٰدِ
Babu mai yin jayayya game da ayoyin Allah sai waxanda suka kafirta, saboda haka kada yawan zirga-zirgarsu a garuruwa ya ruxe ka
ذَٰلِكُم بِأَنَّهُۥٓ إِذَا دُعِيَ ٱللَّهُ وَحۡدَهُۥ كَفَرۡتُمۡ وَإِن يُشۡرَكۡ بِهِۦ تُؤۡمِنُواْۚ فَٱلۡحُكۡمُ لِلَّهِ ٱلۡعَلِيِّ ٱلۡكَبِيرِ
Wannan (sakamakon) saboda cewa, idan aka kira Allah Shi kaxai sai ku kafirce, idan kuwa aka yi shirka da Shi, sai ku yi imani. To hukuncin na Allah ne Maxaukaki, Mai girma
وَلَوۡ جَعَلۡنَٰهُ قُرۡءَانًا أَعۡجَمِيّٗا لَّقَالُواْ لَوۡلَا فُصِّلَتۡ ءَايَٰتُهُۥٓۖ ءَا۬عۡجَمِيّٞ وَعَرَبِيّٞۗ قُلۡ هُوَ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْ هُدٗى وَشِفَآءٞۚ وَٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ فِيٓ ءَاذَانِهِمۡ وَقۡرٞ وَهُوَ عَلَيۡهِمۡ عَمًىۚ أُوْلَـٰٓئِكَ يُنَادَوۡنَ مِن مَّكَانِۭ بَعِيدٖ
Da Mun sanya shi Alqur’ani Ba’ajame da tabbas za su ce: “Me ya hana a bayyana ayoyinsa? Yanzu (a ce Alqur’ani) Ba’ajame (Annabi kuma) Balarabe?” Ka ce: “Shi ga waxanda suka yi imani shiriya ne da waraka. Waxanda kuwa ba sa yin imani akwai nauyi cikin kunnuwansu, shi kuma makanta ne a gare su.” Waxannan (sun yi kama da waxanda) ake kira daga wuri mai nisa
وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَتَعۡسٗا لَّهُمۡ وَأَضَلَّ أَعۡمَٰلَهُمۡ
Waxanda kuwa suka kafirce to kaiconsu, (Allah) kuma Ya lalata ayyukansu[1]
1- Watau ba za su sami ladan wani aiki nasu na qwarai ba, kuma ayyukansu na qoqarin rushe Musulunci ba za su yi nasara ba.
ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ كَرِهُواْ مَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ فَأَحۡبَطَ أَعۡمَٰلَهُمۡ
Wannan kuwa saboda cewa sun qi abin da Allah Ya saukar, sai Ya lalata ayyukansu
ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ مَوۡلَى ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَأَنَّ ٱلۡكَٰفِرِينَ لَا مَوۡلَىٰ لَهُمۡ
Wannan kuwa saboda lalle Allah ne Majivincin al’amuran waxanda suka yi imani, lalle kuma su kafirai ba su da wani majivinci
إِنَّ ٱللَّهَ يُدۡخِلُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يَتَمَتَّعُونَ وَيَأۡكُلُونَ كَمَا تَأۡكُلُ ٱلۡأَنۡعَٰمُ وَٱلنَّارُ مَثۡوٗى لَّهُمۡ
Lalle Allah Yana shigar da waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki nagari gidajen Aljanna (waxanda) qoramu suke gudana ta qarqashinsu; waxanda kuwa suka kafirta suna jin daxi (a duniya), suna kuma ta ciye-ciye kamar yadda dabbobi suke yi, wuta ce kuma makomarsu
ضَرَبَ ٱللَّهُ مَثَلٗا لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱمۡرَأَتَ نُوحٖ وَٱمۡرَأَتَ لُوطٖۖ كَانَتَا تَحۡتَ عَبۡدَيۡنِ مِنۡ عِبَادِنَا صَٰلِحَيۡنِ فَخَانَتَاهُمَا فَلَمۡ يُغۡنِيَا عَنۡهُمَا مِنَ ٱللَّهِ شَيۡـٔٗا وَقِيلَ ٱدۡخُلَا ٱلنَّارَ مَعَ ٱلدَّـٰخِلِينَ
Allah Ya ba da wani misali ga waxanda suka kafirta da matar Nuhu da matar Luxu; sun kasance qarqashin (igiyar auren) wasu bayi su biyu salihai daga bayinmu, sai suka ha’ince su[1], saboda haka ba su wadatar musu komai ba (daga azabar) Allah, aka kuma ce: “Ku shiga wuta tare da masu shiga.”
1- Watau suka kafirce musu, suka riqa hana mutane bin addinin Allah, suka kuma riqa goyon bayan kafirai.