Capítulo: Suratul An’am

Verso : 54

وَإِذَا جَآءَكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِـَٔايَٰتِنَا فَقُلۡ سَلَٰمٌ عَلَيۡكُمۡۖ كَتَبَ رَبُّكُمۡ عَلَىٰ نَفۡسِهِ ٱلرَّحۡمَةَ أَنَّهُۥ مَنۡ عَمِلَ مِنكُمۡ سُوٓءَۢا بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ تَابَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَصۡلَحَ فَأَنَّهُۥ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Kuma idan waxanda suke yin imani da ayoyinmu sun zo wurinka, to ka ce: “Sallama a gare ku;” Ubangijinku Ya wajabta wa kansa yin rahama cewa, lalle cikinku duk wanda ya aikata wani mummunan aiki bisa ga jahilci, sannan daga baya ya tuba kuma ya kyautata aiki, to Shi Mai gafara ne, Mai jin qai.”



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 145

قُل لَّآ أَجِدُ فِي مَآ أُوحِيَ إِلَيَّ مُحَرَّمًا عَلَىٰ طَاعِمٖ يَطۡعَمُهُۥٓ إِلَّآ أَن يَكُونَ مَيۡتَةً أَوۡ دَمٗا مَّسۡفُوحًا أَوۡ لَحۡمَ خِنزِيرٖ فَإِنَّهُۥ رِجۡسٌ أَوۡ فِسۡقًا أُهِلَّ لِغَيۡرِ ٱللَّهِ بِهِۦۚ فَمَنِ ٱضۡطُرَّ غَيۡرَ بَاغٖ وَلَا عَادٖ فَإِنَّ رَبَّكَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ka ce: “Daga cikin abin da aka sauqar mini na manzanci ban samu wani abinci da aka haramta cinsa ba, sai fa idan ya zamo mushe ne ko jini mai kwarara, ko kuma naman alade, to lalle wannan qazanta ne, ko kuma abin da ya zamo fasiqanci ne wanda aka yanka shi ba da sunan Allah ba.” Sannan wanda ya matsu, ba tare da shisshigi ba, kuma ba yana mai qetare iyaka ba, to lalle Ubangijinka Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 165

وَهُوَ ٱلَّذِي جَعَلَكُمۡ خَلَـٰٓئِفَ ٱلۡأَرۡضِ وَرَفَعَ بَعۡضَكُمۡ فَوۡقَ بَعۡضٖ دَرَجَٰتٖ لِّيَبۡلُوَكُمۡ فِي مَآ ءَاتَىٰكُمۡۗ إِنَّ رَبَّكَ سَرِيعُ ٱلۡعِقَابِ وَإِنَّهُۥ لَغَفُورٞ رَّحِيمُۢ

“Kuma Shi ne Ya sanya ku halifofi a bayan qasa, kuma Ya xaukaka darajar wasunku a kan wasu, don Ya jarrabe ku game da abin da Ya ba ku. Lalle Ubangijinka Mai gaggawar uquba ne, kuma lalle Shi tabbas Mai yawan gafara ne, Mai yawan jin qai.”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 153

وَٱلَّذِينَ عَمِلُواْ ٱلسَّيِّـَٔاتِ ثُمَّ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِهَا وَءَامَنُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Waxanda kuma suka aikata munanan ayyuka, sannan suka tuba daga baya, kuma suka yi imani, lalle Ubangijinka bayansa (tuban), tabbas Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 155

وَٱخۡتَارَ مُوسَىٰ قَوۡمَهُۥ سَبۡعِينَ رَجُلٗا لِّمِيقَٰتِنَاۖ فَلَمَّآ أَخَذَتۡهُمُ ٱلرَّجۡفَةُ قَالَ رَبِّ لَوۡ شِئۡتَ أَهۡلَكۡتَهُم مِّن قَبۡلُ وَإِيَّـٰيَۖ أَتُهۡلِكُنَا بِمَا فَعَلَ ٱلسُّفَهَآءُ مِنَّآۖ إِنۡ هِيَ إِلَّا فِتۡنَتُكَ تُضِلُّ بِهَا مَن تَشَآءُ وَتَهۡدِي مَن تَشَآءُۖ أَنتَ وَلِيُّنَا فَٱغۡفِرۡ لَنَا وَٱرۡحَمۡنَاۖ وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلۡغَٰفِرِينَ

Musa kuma ya zavi mutanensa, maza (na musamman) su saba’in don alqawarinmu[1]; to yayin da wata tsawa ta kama su, sai ya ce: “Ya Ubangijina, idan da Ka ga dama da tun tuni Ka hallakar da su har da ni kaina. Yanzu Ka halaka mu saboda abin da wasu wawaye daga cikinmu suka aikata? Lalle wannan ba komai ba ne face jarrabawa daga gare Ka, Kana vatar da wanda Ka ga dama; Kana kuma shiryar da wanda Ka ga dama; Kai ne Majivincin lamarinmu, don haka Ka gafarta mana, kuma Ka ji qan mu, kuma Kai ne Fiyayyen masu gafara


1- Watau ganawa da Allah don su gabatar da uzurinsu game da bautar xan maraqi da suka yi, su wakilci ‘yan’uwansu wajen neman gafarar Allah.


Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 156

۞وَٱكۡتُبۡ لَنَا فِي هَٰذِهِ ٱلدُّنۡيَا حَسَنَةٗ وَفِي ٱلۡأٓخِرَةِ إِنَّا هُدۡنَآ إِلَيۡكَۚ قَالَ عَذَابِيٓ أُصِيبُ بِهِۦ مَنۡ أَشَآءُۖ وَرَحۡمَتِي وَسِعَتۡ كُلَّ شَيۡءٖۚ فَسَأَكۡتُبُهَا لِلَّذِينَ يَتَّقُونَ وَيُؤۡتُونَ ٱلزَّكَوٰةَ وَٱلَّذِينَ هُم بِـَٔايَٰتِنَا يُؤۡمِنُونَ

“Kuma Ka rubuta mana kyakkyawan abu a cikin wannan duniyar, haka ma a lahira, lalle mu mun tuba zuwa gare Ka.” (Allah) Ya ce: “Ina saukar da azabata a kan wanda Na ga dama; rahamata kuwa ta yalwaci komai. Don haka da sannu zan rubuta ta ga waxanda suke kiyaye dokokin Allah, kuma suke bayar da zakka da kuma waxanda suke yin imani da ayoyinmu



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 167

وَإِذۡ تَأَذَّنَ رَبُّكَ لَيَبۡعَثَنَّ عَلَيۡهِمۡ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ مَن يَسُومُهُمۡ سُوٓءَ ٱلۡعَذَابِۗ إِنَّ رَبَّكَ لَسَرِيعُ ٱلۡعِقَابِ وَإِنَّهُۥ لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Kuma ka tuna lokacin da Ubangijinka Ya yi shela, lalle zai aiko musu da wanda zai xanxana musu mummunar azaba, har ya zuwa ranar tashin alqiyama. Lalle Ubangijinka Mai gaggawar uquba ne, kuma lalle shi tabbas Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 29

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِن تَتَّقُواْ ٱللَّهَ يَجۡعَل لَّكُمۡ فُرۡقَانٗا وَيُكَفِّرۡ عَنكُمۡ سَيِّـَٔاتِكُمۡ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡۗ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan kuka kiyaye dokokin Allah, to zai sanya muku (hanyar) tsira Ya kuma kankare muku munanan ayyukanku kuma Ya gafarta muku. Allah kuwa Ma’abocin babbar falala ne



Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 38

قُل لِّلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ إِن يَنتَهُواْ يُغۡفَرۡ لَهُم مَّا قَدۡ سَلَفَ وَإِن يَعُودُواْ فَقَدۡ مَضَتۡ سُنَّتُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Ka ce da waxanda suka kafirta idan suka daina, to za a gafarta musu abin da ya riga ya wuce, idan kuma suka koma to fa ba shakka al’adar mutanen farko ta gabata[1]


1- Watau yadda Allah () ya hallaka al’ummun da suka gabata waxanda suka qaryata annabawansu.


Capítulo: Suratul Anfal

Verso : 70

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّبِيُّ قُل لِّمَن فِيٓ أَيۡدِيكُم مِّنَ ٱلۡأَسۡرَىٰٓ إِن يَعۡلَمِ ٱللَّهُ فِي قُلُوبِكُمۡ خَيۡرٗا يُؤۡتِكُمۡ خَيۡرٗا مِّمَّآ أُخِذَ مِنكُمۡ وَيَغۡفِرۡ لَكُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ya kai wannan Annabi, ka ce da fursunonin da suke a hannayenku: “Idan dai har Allah Ya san akwai wani alheri a zukatanku, to zai ba ku fiye da abin da aka karva daga wurinku Ya kuma gafarta muku. Allah kuwa Mai gafara ne Mai jin qai.”



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 27

ثُمَّ يَتُوبُ ٱللَّهُ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ عَلَىٰ مَن يَشَآءُۗ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Sannan bayan wannan Allah zai karvi tuban wanda Ya ga dama. Allah kuwa Mai gafara ne, Mai rahama



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 99

وَمِنَ ٱلۡأَعۡرَابِ مَن يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ وَيَتَّخِذُ مَا يُنفِقُ قُرُبَٰتٍ عِندَ ٱللَّهِ وَصَلَوَٰتِ ٱلرَّسُولِۚ أَلَآ إِنَّهَا قُرۡبَةٞ لَّهُمۡۚ سَيُدۡخِلُهُمُ ٱللَّهُ فِي رَحۡمَتِهِۦٓۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Daga mutanen qauye xin kuma akwai waxanda suke yin imani da Allah da ranar lahira, suke kuma xaukar abin da suke ciyarwa (hanyoyi ne) na samun kusanci ga Allah da kuma addu’o’in Manzo. Lalle wannan ibada ce gare su. Allah zai shigar da su cikin rahamarsa. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 102

وَءَاخَرُونَ ٱعۡتَرَفُواْ بِذُنُوبِهِمۡ خَلَطُواْ عَمَلٗا صَٰلِحٗا وَءَاخَرَ سَيِّئًا عَسَى ٱللَّهُ أَن يَتُوبَ عَلَيۡهِمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

Wasu kuwa sun yi iqirari da laifinsu, sun gauraya kyakkyawan aiki da wani mummuna, to tabbas Allah zai karvi tubansu. Lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 104

أَلَمۡ يَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ هُوَ يَقۡبَلُ ٱلتَّوۡبَةَ عَنۡ عِبَادِهِۦ وَيَأۡخُذُ ٱلصَّدَقَٰتِ وَأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Shin yanzu ba su sani ba ne cewa Allah Shi Yake karvar tuba daga bayinsa Yake kuma karvar sadakoki, kuma lalle Shi ne Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai?



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 117

لَّقَد تَّابَ ٱللَّهُ عَلَى ٱلنَّبِيِّ وَٱلۡمُهَٰجِرِينَ وَٱلۡأَنصَارِ ٱلَّذِينَ ٱتَّبَعُوهُ فِي سَاعَةِ ٱلۡعُسۡرَةِ مِنۢ بَعۡدِ مَا كَادَ يَزِيغُ قُلُوبُ فَرِيقٖ مِّنۡهُمۡ ثُمَّ تَابَ عَلَيۡهِمۡۚ إِنَّهُۥ بِهِمۡ رَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Tabbas haqiqa Allah Ya yafe wa Annabi da masu hijira da kuma Ansaru waxanda suka bi shi a lokacin tsanani bayan har zukatan wasu qungiyoyi daga cikinsu sun kusa su karkace, sannan (Allah) Ya karvi tubansu. Lalle Shi Mai tausasawa ne, Mai jin qai a gare su



Capítulo: Suratut Tauba

Verso : 118

وَعَلَى ٱلثَّلَٰثَةِ ٱلَّذِينَ خُلِّفُواْ حَتَّىٰٓ إِذَا ضَاقَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلۡأَرۡضُ بِمَا رَحُبَتۡ وَضَاقَتۡ عَلَيۡهِمۡ أَنفُسُهُمۡ وَظَنُّوٓاْ أَن لَّا مَلۡجَأَ مِنَ ٱللَّهِ إِلَّآ إِلَيۡهِ ثُمَّ تَابَ عَلَيۡهِمۡ لِيَتُوبُوٓاْۚ إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma (Ya yafe wa) mutanen nan guda uku waxanda aka dakatar da karvar tubansu[1], har sai yayin da duniya ta yi musu qunci duk da yalwarta, kuma zukatansu suka quntata, suka tabbatar da cewa dai babu wata mafaka daga Allah sai dai a wajensa. Sannan sai Ya yi musu muwafaqar tuba don su tuba. Lalle Allah Shi ne Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai


1- Su ne sahabban nan uku, watau Ka’abu xan Maliku da Muraratu xan Rabi’atu da Hilal xan Umayyatu Al-Waqifi. Sun qi fita yaqin Tabuka tare da Annabi () ba tare da wani uzuri ba.


Capítulo: Suratur Ra’ad

Verso : 6

وَيَسۡتَعۡجِلُونَكَ بِٱلسَّيِّئَةِ قَبۡلَ ٱلۡحَسَنَةِ وَقَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِهِمُ ٱلۡمَثُلَٰتُۗ وَإِنَّ رَبَّكَ لَذُو مَغۡفِرَةٖ لِّلنَّاسِ عَلَىٰ ظُلۡمِهِمۡۖ وَإِنَّ رَبَّكَ لَشَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Suna kuma nemanka da gaggauto musu da azaba tun kafin (su nemi) kyakkyawa (wato rahamar Allah), alhali kuwa haqiqa misalai (na waxanda aka halakar) a gabansu sun wuce. Lalle kuma Ubangijinka Ma’abocin gafara ne ga mutane a kan laifuffukansu, kuma lalle Ubangijinka tabbas Mai tsananin azaba ne



Capítulo: Suratu Ibrahim

Verso : 10

۞قَالَتۡ رُسُلُهُمۡ أَفِي ٱللَّهِ شَكّٞ فَاطِرِ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ يَدۡعُوكُمۡ لِيَغۡفِرَ لَكُم مِّن ذُنُوبِكُمۡ وَيُؤَخِّرَكُمۡ إِلَىٰٓ أَجَلٖ مُّسَمّٗىۚ قَالُوٓاْ إِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا تُرِيدُونَ أَن تَصُدُّونَا عَمَّا كَانَ يَعۡبُدُ ءَابَآؤُنَا فَأۡتُونَا بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ

Mazanninsu suka ce: “Yanzu kuwa ashe akwai wata shakka game da Allah, Maqagin sammai da qasa? Yana kiran ku ne don ya gafarta muku zunubanku kuma ya saurara muku har zuwa wani lokaci qayyadajje.” Suka ce: “Ku ba wasu ba ne daban in ban da mutane kamar mu, kuna so ne ku hana mu bin abin da iyanenmu suka kasance suna bauta wa, to sai ku kawo mana hujjoji bayyanannu.”



Capítulo: Suratul Hijr

Verso : 49

۞نَبِّئۡ عِبَادِيٓ أَنِّيٓ أَنَا ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Ka bai wa bayina labarin cewa lalle Ni, Ni ne Mai gafara, Mai jin qai



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 18

وَإِن تَعُدُّواْ نِعۡمَةَ ٱللَّهِ لَا تُحۡصُوهَآۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Idan kuma da za ku qirga ni’imar Allah to ba za ku iya qididdige ta ba. Lalle Allah tabbas Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 110

ثُمَّ إِنَّ رَبَّكَ لِلَّذِينَ هَاجَرُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا فُتِنُواْ ثُمَّ جَٰهَدُواْ وَصَبَرُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Sannan lalle Ubangjinka (Mai gafara ne da jin qai) ga waxanda suka yi hijira bayan an fitine su, sannan suka yi jihadi suka kuma yi haquri, lalle Ubangijinka, bayansu (waxannan ayyuka) Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 115

إِنَّمَا حَرَّمَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡمَيۡتَةَ وَٱلدَّمَ وَلَحۡمَ ٱلۡخِنزِيرِ وَمَآ أُهِلَّ لِغَيۡرِ ٱللَّهِ بِهِۦۖ فَمَنِ ٱضۡطُرَّ غَيۡرَ بَاغٖ وَلَا عَادٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Abin da kawai Ya haramta muku (shi ne) mushe da jini (mai kwarara) da naman alade da kuma abin da aka yanka da (sunan) wanin Allah; amma wanda ya matsu (ya ci) ba yana mai zalunci ko qetare iyaka ba, to lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 119

ثُمَّ إِنَّ رَبَّكَ لِلَّذِينَ عَمِلُواْ ٱلسُّوٓءَ بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِ ذَٰلِكَ وَأَصۡلَحُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٌ

Sannan lalle Ubangijinka (Mai gafara ne) ga waxanda suka aikata mummuna a cikin jahilci sannan suka tuba bayan haka suka kuma gyara, lalle Ubagijinka Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Isra’i

Verso : 25

رَّبُّكُمۡ أَعۡلَمُ بِمَا فِي نُفُوسِكُمۡۚ إِن تَكُونُواْ صَٰلِحِينَ فَإِنَّهُۥ كَانَ لِلۡأَوَّـٰبِينَ غَفُورٗا

Ubangijinku ne Mafi sanin abin da yake zukatanku. Idan kuka zamanto nagari, to lalle Shi Ya tabbata Mai gafara ne ga masu komawa gare Shi da tuba



Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 58

وَرَبُّكَ ٱلۡغَفُورُ ذُو ٱلرَّحۡمَةِۖ لَوۡ يُؤَاخِذُهُم بِمَا كَسَبُواْ لَعَجَّلَ لَهُمُ ٱلۡعَذَابَۚ بَل لَّهُم مَّوۡعِدٞ لَّن يَجِدُواْ مِن دُونِهِۦ مَوۡئِلٗا

Ubangijinka kuwa Mai yawan gafara ne Ma’abocin rahama; da Yana kama su da abin da suka aikata, to da Ya gaggauta musu azaba. A’a, (ba Ya yin haka), sai dai suna da qayyadajjen lokaci wanda ba za su sami wata makauta ba daga gare shi



Capítulo: Suratu Xa Ha

Verso : 82

وَإِنِّي لَغَفَّارٞ لِّمَن تَابَ وَءَامَنَ وَعَمِلَ صَٰلِحٗا ثُمَّ ٱهۡتَدَىٰ

Lalle Ni kuma Mai yawan gafara ne ga wanda ya tuba kuma ya yi aiki na gari sannan ya (tabbata bisa) shiriya



Capítulo: Suratun Nur

Verso : 22

وَلَا يَأۡتَلِ أُوْلُواْ ٱلۡفَضۡلِ مِنكُمۡ وَٱلسَّعَةِ أَن يُؤۡتُوٓاْ أُوْلِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينَ وَٱلۡمُهَٰجِرِينَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ وَلۡيَعۡفُواْ وَلۡيَصۡفَحُوٓاْۗ أَلَا تُحِبُّونَ أَن يَغۡفِرَ ٱللَّهُ لَكُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٌ

Kuma kada masu hali da wadata daga cikinku su rantse a kan qin ba da (abin hannunsu) ga makusanta da miskinai da masu hijira saboda Allah. Su kuma yi afuwa su yafe. Shin ku ba kwa so ne Allah Ya gafarta muku? Allah kuwa Mai gafara ne, Mai jin qai[1]


1- Ayar tana magana ne a kan Abubakar () lokacin da ya yi rantsuwa ba zai ci gaba da taimaka wa xan innarsa Misxahu xan Usasa ba domin ya zama cikin masu kwaza qagen da aka yi wa Nana A’isha (RAH)..


Capítulo: Suratun Nur

Verso : 33

وَلۡيَسۡتَعۡفِفِ ٱلَّذِينَ لَا يَجِدُونَ نِكَاحًا حَتَّىٰ يُغۡنِيَهُمُ ٱللَّهُ مِن فَضۡلِهِۦۗ وَٱلَّذِينَ يَبۡتَغُونَ ٱلۡكِتَٰبَ مِمَّا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُكُمۡ فَكَاتِبُوهُمۡ إِنۡ عَلِمۡتُمۡ فِيهِمۡ خَيۡرٗاۖ وَءَاتُوهُم مِّن مَّالِ ٱللَّهِ ٱلَّذِيٓ ءَاتَىٰكُمۡۚ وَلَا تُكۡرِهُواْ فَتَيَٰتِكُمۡ عَلَى ٱلۡبِغَآءِ إِنۡ أَرَدۡنَ تَحَصُّنٗا لِّتَبۡتَغُواْ عَرَضَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۚ وَمَن يُكۡرِههُّنَّ فَإِنَّ ٱللَّهَ مِنۢ بَعۡدِ إِكۡرَٰهِهِنَّ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Waxanda kuma ba su sami wadatar yin aure ba su kame kansu har Allah Ya wadata su daga falalarsa. Waxanda kuwa suke neman fansar kansu daga bayinku[1], sai ku ba su damar fansar kansu, idan kun san suna da halin iya biya; kuma ku ba su wani abu daga dukiyar Allah da Ya ba ku. Kada kuma ku tilasta wa kuyanginku ‘yan mata a kan yin zina idan sun nemi kame kai, don ku nemi amfanin rayuwar duniya. Wanda duk kuwa ya tilasta su, to lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai bayan tilastawar da aka yi musu


1- Watau ta hanyar biyan wani kuxi da za a yanka musu idan sun biya sun zama ‘yantattun ‘ya’ya.


Capítulo: Suratul Furqan

Verso : 70

إِلَّا مَن تَابَ وَءَامَنَ وَعَمِلَ عَمَلٗا صَٰلِحٗا فَأُوْلَـٰٓئِكَ يُبَدِّلُ ٱللَّهُ سَيِّـَٔاتِهِمۡ حَسَنَٰتٖۗ وَكَانَ ٱللَّهُ غَفُورٗا رَّحِيمٗا

Sai dai wanda ya tuba ya kuma yi imani, kuma ya yi aiki na gari, to waxannan Allah zai musanya munanan ayyukansu da kyawawa. Allah kuwa ya kasance Mai gafara ne, Mai jin qai



Capítulo: Suratul Qasas

Verso : 46

وَمَا كُنتَ بِجَانِبِ ٱلطُّورِ إِذۡ نَادَيۡنَا وَلَٰكِن رَّحۡمَةٗ مِّن رَّبِّكَ لِتُنذِرَ قَوۡمٗا مَّآ أَتَىٰهُم مِّن نَّذِيرٖ مِّن قَبۡلِكَ لَعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ

Kuma ba ka kasance a gefen (dutsen) Xuri ba, lokacin da Muka kirawo (Musa), sai dai wata rahama daga Ubangijinka, don ka gargaxi wasu mutane da mai gargaxi bai zo musu ba gabaninka ko sa wa’azantu