Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 71

يُطَافُ عَلَيۡهِم بِصِحَافٖ مِّن ذَهَبٖ وَأَكۡوَابٖۖ وَفِيهَا مَا تَشۡتَهِيهِ ٱلۡأَنفُسُ وَتَلَذُّ ٱلۡأَعۡيُنُۖ وَأَنتُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Ana zagayawa tsakaninsu da akusa na zinari da kofuna; a cikinta kuma akwai (duk) abin da rayuka suke sha’awa, idanuwa kuma suke jin daxin (ganinsu); ku kuma a cikinta madawwama ne



Capítulo: Suratul Jasiya

Verso : 22

وَخَلَقَ ٱللَّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّ وَلِتُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ وَهُمۡ لَا يُظۡلَمُونَ

Allah kuma Ya halicci sammai da qasa da gaskiya, don kuma a saka wa kowane rai irin abin da ya aikata, alhali kuma su ba za a zalunce su ba



Capítulo: Suratu Qaf 

Verso : 21

وَجَآءَتۡ كُلُّ نَفۡسٖ مَّعَهَا سَآئِقٞ وَشَهِيدٞ

Kuma kowane rai ya zo a tare da shi akwai mai kora da mai shaida[1]


1- Watau mala’iku biyu tare da kowane mutum, xaya yana kora shi; xaya kuma mai ba da shaida game da shi.


Capítulo: Suratu Qaf 

Verso : 22

لَّقَدۡ كُنتَ فِي غَفۡلَةٖ مِّنۡ هَٰذَا فَكَشَفۡنَا عَنكَ غِطَآءَكَ فَبَصَرُكَ ٱلۡيَوۡمَ حَدِيدٞ

Haqiqa ka kasance a cikin gafala game da wannan, sai Muka yaye maka yanarka, to ganinka a yau tangaran yake



Capítulo: Suratux Xur

Verso : 21

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَٱتَّبَعَتۡهُمۡ ذُرِّيَّتُهُم بِإِيمَٰنٍ أَلۡحَقۡنَا بِهِمۡ ذُرِّيَّتَهُمۡ وَمَآ أَلَتۡنَٰهُم مِّنۡ عَمَلِهِم مِّن شَيۡءٖۚ كُلُّ ٱمۡرِيِٕۭ بِمَا كَسَبَ رَهِينٞ

Waxanda kuwa suka yi imani, zuriyarsu kuma suka bi su a imani, za Mu haxa su da zuriyarsu[1], ba kuma za Mu tauye musu komai ba na aikinsu. Kowane mutum jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[2]


1- Watau sai Allah ya xaukaka darajar ‘ya’yansu don su haxu wuri guda a Aljanna, ko da kuwa ayyukan ‘ya’yan ba su kai na iyayen ba.


2- Watau ana tsare shi don abin da ya aikata kaxai, ba za a kama shi ne da laifin wani ba.


Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 38

كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ رَهِينَةٌ

Kowane rai jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[1]


1- Watau jingina ne ga ayyukansu, ko dai su hallakar da shi ko su kuvutar da shi, su ‘yanta shi.


Capítulo: Suratut Takwir

Verso : 14

عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّآ أَحۡضَرَتۡ

To kowane rai ya san abin da ya halarto (da shi na ayyuka)



Capítulo: Suratul Infixar

Verso : 5

عَلِمَتۡ نَفۡسٞ مَّا قَدَّمَتۡ وَأَخَّرَتۡ

Kowane rai ya san abin da ya gabatar da wanda ya jirkintar



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa