Capítulo: Suratul An’am

Verso : 31

قَدۡ خَسِرَ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِلِقَآءِ ٱللَّهِۖ حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَتۡهُمُ ٱلسَّاعَةُ بَغۡتَةٗ قَالُواْ يَٰحَسۡرَتَنَا عَلَىٰ مَا فَرَّطۡنَا فِيهَا وَهُمۡ يَحۡمِلُونَ أَوۡزَارَهُمۡ عَلَىٰ ظُهُورِهِمۡۚ أَلَا سَآءَ مَا يَزِرُونَ

Haqiqa waxanda suka qaryata haxuwa da Allah sun yi hasara; har sai lokacin da alqiyama ta zo musu ba zato ba tsammani, sai su ce: “Kaiconmu kan irin sakacin da muka yi a cikinta (duniya),” alhalin kuwa suna xauke da kayan laifukansu a bayansu. Ku saurara, abin da suka xauka na laifi ya munana matuqa



Capítulo: Suratul An’am

Verso : 40

قُلۡ أَرَءَيۡتَكُمۡ إِنۡ أَتَىٰكُمۡ عَذَابُ ٱللَّهِ أَوۡ أَتَتۡكُمُ ٱلسَّاعَةُ أَغَيۡرَ ٱللَّهِ تَدۡعُونَ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Ka ce; “Ku ba ni labari, idan da a ce azabar Allah za ta zo muku ko alqiyama ta zo muku, shin wanin Allah za ku kira, in har kun kasance masu gaskiya?”



Capítulo: Suratul A’araf

Verso : 187

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَاۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ رَبِّيۖ لَا يُجَلِّيهَا لِوَقۡتِهَآ إِلَّا هُوَۚ ثَقُلَتۡ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ لَا تَأۡتِيكُمۡ إِلَّا بَغۡتَةٗۗ يَسۡـَٔلُونَكَ كَأَنَّكَ حَفِيٌّ عَنۡهَاۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ ٱللَّهِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Suna tambayar ka game da tashin alqiyama yaushe ne matabbatarta take? Ka ce: “Sanin lokacinta yana wajen Ubangijina; ba mai bayyanar da lokacinta sai Shi. Ta yi nauyi a cikin sammai da qasa. Ba za ta zo muku ba sai katsahan.” Suna tambayar ka kamar ka nace a kanta, ka ce: “Iliminta yana wajen Allah kaxai”, sai dai da yawa daga cikin mutane ba su sani ba



Capítulo: Suratu Yusuf 

Verso : 107

أَفَأَمِنُوٓاْ أَن تَأۡتِيَهُمۡ غَٰشِيَةٞ مِّنۡ عَذَابِ ٱللَّهِ أَوۡ تَأۡتِيَهُمُ ٱلسَّاعَةُ بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Yanzu sun amince ne wata azabar Allah mai lulluvewa ta zo musu, ko kuwa alqiyama ta zo musu ba zato ba tsammani, alhalin su ba su sani ba?



Capítulo: Suratun Nahl

Verso : 77

وَلِلَّهِ غَيۡبُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَمَآ أَمۡرُ ٱلسَّاعَةِ إِلَّا كَلَمۡحِ ٱلۡبَصَرِ أَوۡ هُوَ أَقۡرَبُۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ

Kuma Allah ne Masanin gaibu na sammai da qasa. Al’amarin alqiyama kuma ba komai ba ne face kamar qiftawar ido ko kuma ya fi haka kusa. Lalle Allah Mai iko ne a kan komai



Capítulo: Suratu Xa Ha

Verso : 15

إِنَّ ٱلسَّاعَةَ ءَاتِيَةٌ أَكَادُ أُخۡفِيهَا لِتُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا تَسۡعَىٰ

“Lalle alqiyama za ta zo, ina nufin voye ta ne don a saka wa kowanne rai da irin abin da yake aikatawa



Capítulo: Suratul Hajji

Verso : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلنَّاسُ ٱتَّقُواْ رَبَّكُمۡۚ إِنَّ زَلۡزَلَةَ ٱلسَّاعَةِ شَيۡءٌ عَظِيمٞ

Ya ku mutane, ku kiyaye dokokin Ubangijinku. Lalle girgizar (ranar) alqiyama abu ne mai girma



Capítulo: Suratur Rum

Verso : 12

وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ يُبۡلِسُ ٱلۡمُجۡرِمُونَ

Kuma ranar da alqiyama za ta tashi, a wannan ranar ne masu manyan laifuka (kafirai) za su yanke qauna daga rahama



Capítulo: Suratur Rum

Verso : 14

وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ يَوۡمَئِذٖ يَتَفَرَّقُونَ

Kuma ranar da alqiyama za ta tashi, a wannan ranar ne (mutane) za su rarrabu[1]


1- Watau qungiya biyu, qungiyar muminai masu shiga Aljanna da ta kafirai masu shiga wuta.


Capítulo: Suratul Ahzab

Verso : 63

يَسۡـَٔلُكَ ٱلنَّاسُ عَنِ ٱلسَّاعَةِۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ ٱللَّهِۚ وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّ ٱلسَّاعَةَ تَكُونُ قَرِيبًا

Mutane suna tambayar ka game da (ranar) alqiyama; ka ce (da su): “Saninta a wajen Allah kawai yake.” Ba ka sani ba ko watakila alqiyamar za ta kasance kusa



Capítulo: Suratu Saba’i

Verso : 3

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَا تَأۡتِينَا ٱلسَّاعَةُۖ قُلۡ بَلَىٰ وَرَبِّي لَتَأۡتِيَنَّكُمۡ عَٰلِمِ ٱلۡغَيۡبِۖ لَا يَعۡزُبُ عَنۡهُ مِثۡقَالُ ذَرَّةٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَلَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَآ أَصۡغَرُ مِن ذَٰلِكَ وَلَآ أَكۡبَرُ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٖ

Kuma waxanda suka kafirta suka ce: “Ranar alqiyama ba za ta zo mana ba.” Ka ce: “A’a, na rantse da Ubangijina, tabbas za ta zo muku, (Allah) Shi ne Masanin gaibu; ba abin da yake voye a gare Shi; daidai da qwayar zarra a cikin sammai ko a qasa, ko wanda ya fi wannan qanqanta ko ya fi girma, face yana nan (a rubuce) a cikin Lauhul-Mahafuzu



Capítulo: Suratu Ghafir

Verso : 59

إِنَّ ٱلسَّاعَةَ لَأٓتِيَةٞ لَّا رَيۡبَ فِيهَا وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يُؤۡمِنُونَ

Lalle alqiyama tabbas za ta zo babu kokwanto a cikinta, sai dai kuma yawancin mutane ba sa yin imani



Capítulo: Suratu Fussilat

Verso : 47

۞إِلَيۡهِ يُرَدُّ عِلۡمُ ٱلسَّاعَةِۚ وَمَا تَخۡرُجُ مِن ثَمَرَٰتٖ مِّنۡ أَكۡمَامِهَا وَمَا تَحۡمِلُ مِنۡ أُنثَىٰ وَلَا تَضَعُ إِلَّا بِعِلۡمِهِۦۚ وَيَوۡمَ يُنَادِيهِمۡ أَيۡنَ شُرَكَآءِي قَالُوٓاْ ءَاذَنَّـٰكَ مَامِنَّا مِن شَهِيدٖ

Gare shi ne ake mayar da sanin lokacin alqiyama. Kuma babu wasu ‘ya’yan itatuwa da suke fitowa daga kwansonsu, babu kuma wata mace da take xaukan ciki ko take haifewa sai da saninsa. Kuma a ranar da zai yi kiran su cewa: “Ina abokan tarayyar tawa?” Za su ce: “Mun sanar da Kai (a yau) babu wani mai yin shaida daga cikinmu[1].”


1- Watau babu wani da zai ba da shaidar cewa, Allah yana da abokan tarayya.


Capítulo: Suratuz Zukhruf 

Verso : 66

هَلۡ يَنظُرُونَ إِلَّا ٱلسَّاعَةَ أَن تَأۡتِيَهُم بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ

Ba abin da suke jira sai alqiyama kawai ta zo musu kwatsam, alhali ba tare da sun sani ba



Capítulo: Suratul Jasiya

Verso : 32

وَإِذَا قِيلَ إِنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞ وَٱلسَّاعَةُ لَا رَيۡبَ فِيهَا قُلۡتُم مَّا نَدۡرِي مَا ٱلسَّاعَةُ إِن نَّظُنُّ إِلَّا ظَنّٗا وَمَا نَحۡنُ بِمُسۡتَيۡقِنِينَ

Idan kuma aka ce, lalle alqawarin Allah gaskiya ne, alqiyama kuma babu kokwanto a game da ita kukan ce: “Mu ba mu da sanin mece ce ma alqiyama, mu ba abin da muke tsammani (game da ita) sai zato, mu kuma ba mu da tabbas.”



Capítulo: Suratuz Zariyat

Verso : 5

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٞ

Lalle abin da ake yi muku alqawarinsa tabbas gaskiya ne



Capítulo: Suratuz Zariyat

Verso : 6

وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٞ

Kuma lalle sakamako tabbas mai afkuwa ne



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 1

ٱقۡتَرَبَتِ ٱلسَّاعَةُ وَٱنشَقَّ ٱلۡقَمَرُ

Alqiyama ta kusanto, wata kuma ya tsage[1]


1- Watau a zamanin Manzon Allah () wanda mushirikan Quraishawa suka gani da idonsu, bayan sun nemi ya nuna musu mu’ujiza.


Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 2

وَإِن يَرَوۡاْ ءَايَةٗ يُعۡرِضُواْ وَيَقُولُواْ سِحۡرٞ مُّسۡتَمِرّٞ

Idan kuma suka ga wata aya sai su kau da kai kuma su ce: “Wannan sihiri ne qaqqarfa.”



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 3

وَكَذَّبُواْ وَٱتَّبَعُوٓاْ أَهۡوَآءَهُمۡۚ وَكُلُّ أَمۡرٖ مُّسۡتَقِرّٞ

Suka kuma qaryata, suka bi soye-soyen zukatansu. Kowane al’amari kuwa (na alheri ko na sharri) mai tabbata ne



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 4

وَلَقَدۡ جَآءَهُم مِّنَ ٱلۡأَنۢبَآءِ مَا فِيهِ مُزۡدَجَرٌ

Haqiqa kuma wasu labarai waxanda tsawatarwa take cikinsu sun zo musu



Capítulo: Suratul Qamar

Verso : 5

حِكۡمَةُۢ بَٰلِغَةٞۖ فَمَا تُغۡنِ ٱلنُّذُرُ

Hikima ce mai kaiwa matuqa, sai dai kuma gargaxin ba ya amfanarwa



Capítulo: Suratul Mulk

Verso : 25

وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا ٱلۡوَعۡدُ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Suna kuma cewa: “Yaushe ne wannan alqawarin, idan kun kasance masu gaskiya?”



Capítulo: Suratul Mulk

Verso : 26

قُلۡ إِنَّمَا ٱلۡعِلۡمُ عِندَ ٱللَّهِ وَإِنَّمَآ أَنَا۠ نَذِيرٞ مُّبِينٞ

Ka ce: “Saninsa yana wurin Allah kawai, kuma ni kawai mai gargaxi ne mai bayyana (gargaxin).”



Capítulo: Suratul Mulk

Verso : 27

فَلَمَّا رَأَوۡهُ زُلۡفَةٗ سِيٓـَٔتۡ وُجُوهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَقِيلَ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَدَّعُونَ

To lokacin da za su gan shi a kurkusa, sai fuskokin waxanda suka kafirce suka yi baqi, aka kuma ce: “Wannan ne abin da kuka kasance kuna neman zuwansa.”