Capítulo: Suratu Qaf 

Verso : 30

يَوۡمَ نَقُولُ لِجَهَنَّمَ هَلِ ٱمۡتَلَأۡتِ وَتَقُولُ هَلۡ مِن مَّزِيدٖ

A ranar da za Mu ce da Jahannama: “Shin kin cika?” (Ita) kuma ta ce: “Shin akwai wani qari?”



Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 42

فِي سَمُومٖ وَحَمِيمٖ

Suna cikin iska mai tsananin zafi da kuma tafasasshen ruwa



Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 43

وَظِلّٖ مِّن يَحۡمُومٖ

Da kuma inuwa ta turnuqun hayaqi



Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 44

لَّا بَارِدٖ وَلَا كَرِيمٍ

Ba mai sanyi ba, kuma ba mai daraja ba



Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 51

ثُمَّ إِنَّكُمۡ أَيُّهَا ٱلضَّآلُّونَ ٱلۡمُكَذِّبُونَ

“Sannan lalle ku kuma waxannan vatattu masu qaryatawa



Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 52

لَأٓكِلُونَ مِن شَجَرٖ مِّن زَقُّومٖ

“Tabbas za ku ci daga bishiyar Zaqqumu[1]


1- Watau wata bishiya ce mafi muni da sharri a wutar jahannama.


Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 53

فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ

“Sannan za ku cika cikunanku da ita



Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 54

فَشَٰرِبُونَ عَلَيۡهِ مِنَ ٱلۡحَمِيمِ

“Sannan za ku sha tafasasshen ruwa a kanta



Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 55

فَشَٰرِبُونَ شُرۡبَ ٱلۡهِيمِ

“Sannan za ku sha irin shan raquma masu jin qishirwa.”



Capítulo: Suratul Waqi’a

Verso : 56

هَٰذَا نُزُلُهُمۡ يَوۡمَ ٱلدِّينِ

Wannan ita ce gararsu a ranar sakamako



Capítulo: Suratut Tahrim

Verso : 6

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ قُوٓاْ أَنفُسَكُمۡ وَأَهۡلِيكُمۡ نَارٗا وَقُودُهَا ٱلنَّاسُ وَٱلۡحِجَارَةُ عَلَيۡهَا مَلَـٰٓئِكَةٌ غِلَاظٞ شِدَادٞ لَّا يَعۡصُونَ ٱللَّهَ مَآ أَمَرَهُمۡ وَيَفۡعَلُونَ مَا يُؤۡمَرُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kare kawunanku da iyalanku daga wuta (wadda) makamashinta mutane ne da duwatsu, masu kula da ita mala’iku ne masu kaushin hali, masu tsananin gaske, ba sa sava wa Allah abin da Ya umarce su, suna kuma aikata abin da ake umartar su



Capítulo: Suratul Mulk

Verso : 6

وَلِلَّذِينَ كَفَرُواْ بِرَبِّهِمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Waxanda kuma suka kafirce wa Ubangijinsu suna da azabar Jahannama; makoma kuwa ta munana



Capítulo: Suratul Mulk

Verso : 7

إِذَآ أُلۡقُواْ فِيهَا سَمِعُواْ لَهَا شَهِيقٗا وَهِيَ تَفُورُ

Idan aka jefa su a cikinta sai su ji kururuwarta, tana tafarfasa



Capítulo: Suratul Mulk

Verso : 8

تَكَادُ تَمَيَّزُ مِنَ ٱلۡغَيۡظِۖ كُلَّمَآ أُلۡقِيَ فِيهَا فَوۡجٞ سَأَلَهُمۡ خَزَنَتُهَآ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ نَذِيرٞ

Tana kusa da ta kekkece saboda tsananin fushi; duk sanda aka jefa wata tawaga a cikinta sai masu tsaron ta su tambaye su: “Shin mai gargaxi bai zo muku ba?”



Capítulo: Suratul Haqqa

Verso : 31

ثُمَّ ٱلۡجَحِيمَ صَلُّوهُ

Sannan ku shigar da shi (wutar) Jahimu



Capítulo: Suratul Haqqa

Verso : 32

ثُمَّ فِي سِلۡسِلَةٖ ذَرۡعُهَا سَبۡعُونَ ذِرَاعٗا فَٱسۡلُكُوهُ

Sannan ku sa shi cikin sarqa mai tsawo kamu saba’in



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 17

تَدۡعُواْ مَنۡ أَدۡبَرَ وَتَوَلَّىٰ

Tana kiran wanda ya juya ya ba da baya



Capítulo: Suratul Ma’arij

Verso : 18

وَجَمَعَ فَأَوۡعَىٰٓ

Ya kuma tara (dukiya) sai ya voye (ta)



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 26

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ

(Allah ya ce): Da sannu zan shigar da shi (wutar) Saqara



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 27

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Me ya sanar da kai abin da ake ce wa Saqara?



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 28

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ

Ba ta ragewa kuma ba ta barin (komai)



Capítulo: Suratul Muddassir

Verso : 29

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ

Mai xaxxaye fata ce



Capítulo: Suratul Insan

Verso : 4

إِنَّآ أَعۡتَدۡنَا لِلۡكَٰفِرِينَ سَلَٰسِلَاْ وَأَغۡلَٰلٗا وَسَعِيرًا

Lalle Mun tanadar wa kafirai sarqoqi da ququmai da wutar Sa’ira



Capítulo: Suratul Mursalat

Verso : 30

ٱنطَلِقُوٓاْ إِلَىٰ ظِلّٖ ذِي ثَلَٰثِ شُعَبٖ

Ku tafi zuwa wata inuwa mai rassa uku



Capítulo: Suratul Mursalat

Verso : 31

لَّا ظَلِيلٖ وَلَا يُغۡنِي مِنَ ٱللَّهَبِ

Ba mai ba da inuwa ba kuma ba mai karewa daga harshen wuta ba



Capítulo: Suratul Mursalat

Verso : 32

إِنَّهَا تَرۡمِي بِشَرَرٖ كَٱلۡقَصۡرِ

Haqiqa ita tana jefa tartsatsi kamar qaton gini



Capítulo: Suratul Mursalat

Verso : 33

كَأَنَّهُۥ جِمَٰلَتٞ صُفۡرٞ

Kai ka ce su raquma ne baqaqe



Capítulo: Suratun Naba’i

Verso : 21

إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتۡ مِرۡصَادٗا

Lalle Jahannama ta kasance madakata ce