مَآ أَصَابَ مِن مُّصِيبَةٍ إِلَّا بِإِذۡنِ ٱللَّهِۗ وَمَن يُؤۡمِنۢ بِٱللَّهِ يَهۡدِ قَلۡبَهُۥۚ وَٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ
Ba wata musiba da ta samu sai da izinin Allah. Duk kuwa wanda ya yi imani da Allah zai shiryi zuciyarsa. Allah kuma Masanin komai ne
Compartir :
وَأَنَّا مِنَّا ٱلۡمُسۡلِمُونَ وَمِنَّا ٱلۡقَٰسِطُونَۖ فَمَنۡ أَسۡلَمَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ تَحَرَّوۡاْ رَشَدٗا
“Kuma lalle mu a cikinmu akwai Musulmi, a cikinmu kuma akwai karkatattu; saboda haka duk wanda ya musulunta, to waxannan sun nufi hanyar shiriya
إِنَّا هَدَيۡنَٰهُ ٱلسَّبِيلَ إِمَّا شَاكِرٗا وَإِمَّا كَفُورًا
Lalle Mun bayyana masa hanya, ko dai (ya zama) mai godewa ko kuma mai butulcewa
إِنَّ عَلَيۡنَا لَلۡهُدَىٰ
Lalle bayyana hanyar shiriya a kanmu yake
وَإِنَّ لَنَا لَلۡأٓخِرَةَ وَٱلۡأُولَىٰ
Kuma lalle lahira da duniya namu ne