Capítulo: Suratut Taghabun

Verso : 11

مَآ أَصَابَ مِن مُّصِيبَةٍ إِلَّا بِإِذۡنِ ٱللَّهِۗ وَمَن يُؤۡمِنۢ بِٱللَّهِ يَهۡدِ قَلۡبَهُۥۚ وَٱللَّهُ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٞ

Ba wata musiba da ta samu sai da izinin Allah. Duk kuwa wanda ya yi imani da Allah zai shiryi zuciyarsa. Allah kuma Masanin komai ne



Capítulo: Suratul Jinn

Verso : 14

وَأَنَّا مِنَّا ٱلۡمُسۡلِمُونَ وَمِنَّا ٱلۡقَٰسِطُونَۖ فَمَنۡ أَسۡلَمَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ تَحَرَّوۡاْ رَشَدٗا

“Kuma lalle mu a cikinmu akwai Musulmi, a cikinmu kuma akwai karkatattu; saboda haka duk wanda ya musulunta, to waxannan sun nufi hanyar shiriya



Capítulo: Suratul Insan

Verso : 3

إِنَّا هَدَيۡنَٰهُ ٱلسَّبِيلَ إِمَّا شَاكِرٗا وَإِمَّا كَفُورًا

Lalle Mun bayyana masa hanya, ko dai (ya zama) mai godewa ko kuma mai butulcewa



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 12

إِنَّ عَلَيۡنَا لَلۡهُدَىٰ

Lalle bayyana hanyar shiriya a kanmu yake



Capítulo: Suratul Lail

Verso : 13

وَإِنَّ لَنَا لَلۡأٓخِرَةَ وَٱلۡأُولَىٰ

Kuma lalle lahira da duniya namu ne