Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 107

لَّا تَرَىٰ فِيهَا عِوَجٗا وَلَآ أَمۡتٗا

“Ba za ka ga wani kwari ko tudu a kanta ba.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 108

يَوۡمَئِذٖ يَتَّبِعُونَ ٱلدَّاعِيَ لَا عِوَجَ لَهُۥۖ وَخَشَعَتِ ٱلۡأَصۡوَاتُ لِلرَّحۡمَٰنِ فَلَا تَسۡمَعُ إِلَّا هَمۡسٗا

A wannan rana ne za su bi mai kira (zuwa matattara), ba mai bauxe masa; kuma (duk) muryoyi su yi qasa-qasa saboda (girman Allah) Mai rahama, sannan ba za ka ji (komai) ba sai raxa



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 109

يَوۡمَئِذٖ لَّا تَنفَعُ ٱلشَّفَٰعَةُ إِلَّا مَنۡ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَرَضِيَ لَهُۥ قَوۡلٗا

A wannan ranar ceto ba ya amfani sai ga wanda (Allah) Mai rahama Ya yi wa izini, kuma Ya yarda da maganarsa



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 110

يَعۡلَمُ مَا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُمۡ وَلَا يُحِيطُونَ بِهِۦ عِلۡمٗا

(Allah) Yana sane da abin da yake gaba gare su (na ranar alqiyama) da kuma abin da yake bayansu (na ayyukan da suka yi a duniya), su kuwa ba za su kewaye da saninsa ba



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 111

۞وَعَنَتِ ٱلۡوُجُوهُ لِلۡحَيِّ ٱلۡقَيُّومِۖ وَقَدۡ خَابَ مَنۡ حَمَلَ ظُلۡمٗا

Kuma dukkanin fuskoki suka qasqanta ga (Allah) Rayayye, Tsayayye (da Zatinsa). Haqiqa kuma duk wanda ya yo dakon zalunci ya tave



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 112

وَمَن يَعۡمَلۡ مِنَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَلَا يَخَافُ ظُلۡمٗا وَلَا هَضۡمٗا

Duk kuma wanda yake yin aiki na gari alhali kuwa shi mumini ne, to ba zai ji tsoron zalunci ba ko kuma qwauro



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 113

وَكَذَٰلِكَ أَنزَلۡنَٰهُ قُرۡءَانًا عَرَبِيّٗا وَصَرَّفۡنَا فِيهِ مِنَ ٱلۡوَعِيدِ لَعَلَّهُمۡ يَتَّقُونَ أَوۡ يُحۡدِثُ لَهُمۡ ذِكۡرٗا

Kuma kamar haka Muka saukar da shi (Alqur’ani) Balarabe (watau da harshen Larabci), Muka kuma sarrafa ayoyin gargaxi a cikinsa don su kiyaye dokokin (Allah) ko kuma ya sa su su wa’azantu



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 114

فَتَعَٰلَى ٱللَّهُ ٱلۡمَلِكُ ٱلۡحَقُّۗ وَلَا تَعۡجَلۡ بِٱلۡقُرۡءَانِ مِن قَبۡلِ أَن يُقۡضَىٰٓ إِلَيۡكَ وَحۡيُهُۥۖ وَقُل رَّبِّ زِدۡنِي عِلۡمٗا

Kuma fa Allah Sarki na gaskiya Ya xaukaka (daga maganganun kafirai). Kada kuma ka yi garaje da (karatun) Alqur’ani tun kafin a gama yi maka wahayinsa, kuma ka ce: “Ubangiji Ka qara min ilimi.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 115

وَلَقَدۡ عَهِدۡنَآ إِلَىٰٓ ءَادَمَ مِن قَبۡلُ فَنَسِيَ وَلَمۡ نَجِدۡ لَهُۥ عَزۡمٗا

Kuma haqiqa Mun yi alqawari da Adamu tun da farko (cewa kada ya ci itaciyar da aka hana shi), sai ya manta, sai ba Mu same shi da qarfin quduri ba



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 116

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ أَبَىٰ

Kuma (ka tuna) lokacin da Muka ce da mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu” sai suka yi sujjadar sai Iblis ne kawai ya qi



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 117

فَقُلۡنَا يَـٰٓـَٔادَمُ إِنَّ هَٰذَا عَدُوّٞ لَّكَ وَلِزَوۡجِكَ فَلَا يُخۡرِجَنَّكُمَا مِنَ ٱلۡجَنَّةِ فَتَشۡقَىٰٓ

Sannan Muka ce: “Ya Adamu, lalle wannan maqiyinka ne kai da matarka, to kada (ku yarda) ya fitar da ku daga Aljanna, sai ka wahala



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 118

إِنَّ لَكَ أَلَّا تَجُوعَ فِيهَا وَلَا تَعۡرَىٰ

“Lalle (Allah) Ya yi maka alqawarin ba za ka ji yunwa ba a cikinta, kuma ba za ka yi tsiraici ba



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 119

وَأَنَّكَ لَا تَظۡمَؤُاْ فِيهَا وَلَا تَضۡحَىٰ

“Kuma lalle kai ba za ka ji qishi ba a cikinta, kuma ba za ka ji zafin rana ba.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 120

فَوَسۡوَسَ إِلَيۡهِ ٱلشَّيۡطَٰنُ قَالَ يَـٰٓـَٔادَمُ هَلۡ أَدُلُّكَ عَلَىٰ شَجَرَةِ ٱلۡخُلۡدِ وَمُلۡكٖ لَّا يَبۡلَىٰ

Sai Shaixan ya yi masa waswasi ya ce: “Ya Adamu, yanzu ba na nuna maka wata bishiya ta dawwama da kuma mulki wanda ba zai qare ba?”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 121

فَأَكَلَا مِنۡهَا فَبَدَتۡ لَهُمَا سَوۡءَٰتُهُمَا وَطَفِقَا يَخۡصِفَانِ عَلَيۡهِمَا مِن وَرَقِ ٱلۡجَنَّةِۚ وَعَصَىٰٓ ءَادَمُ رَبَّهُۥ فَغَوَىٰ

Sai suka ci wani abu daga gare ta, sai ga tsiraicinsu ya bayyana gare su, sai suka riqa lulluve (jikinsu) da ganyen Aljanna. Kuma Adamu ya sava wa Ubangijinsa ya bar shiriya



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 122

ثُمَّ ٱجۡتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَتَابَ عَلَيۡهِ وَهَدَىٰ

Sannan Ubangijinsa Ya zave shi, sai Ya yafe masa Ya kuma shirye (shi)



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 123

قَالَ ٱهۡبِطَا مِنۡهَا جَمِيعَۢاۖ بَعۡضُكُمۡ لِبَعۡضٍ عَدُوّٞۖ فَإِمَّا يَأۡتِيَنَّكُم مِّنِّي هُدٗى فَمَنِ ٱتَّبَعَ هُدَايَ فَلَا يَضِلُّ وَلَا يَشۡقَىٰ

(Allah) Ya ce (da Adamu da Hauwa’u): “Ku sauka daga gare ta (Aljannar) gaba xayanku, sashinku ya dinga gaba da sashi; sannan idan shiriya ta zo muku daga gare Ni, to duk wanda ya bi shiriyata ba zai tave ba, kuma ba zai wahala ba



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 124

وَمَنۡ أَعۡرَضَ عَن ذِكۡرِي فَإِنَّ لَهُۥ مَعِيشَةٗ ضَنكٗا وَنَحۡشُرُهُۥ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ أَعۡمَىٰ

“Wanda kuma ya bijire wa Alqur’ani to lalle zai yi rayuwa mai qunci, kuma Mu tashe shi makaho ranar alqiyama.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 125

قَالَ رَبِّ لِمَ حَشَرۡتَنِيٓ أَعۡمَىٰ وَقَدۡ كُنتُ بَصِيرٗا

Zai ce: “Ubangijina me ya sa Ka tashe ni makaho, alhali kuwa na kasance mai gani?”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 126

قَالَ كَذَٰلِكَ أَتَتۡكَ ءَايَٰتُنَا فَنَسِيتَهَاۖ وَكَذَٰلِكَ ٱلۡيَوۡمَ تُنسَىٰ

(Allah) Ya ce: “Kamar haka ne ayoyinmu suka zo maka sai ka manta su, to kamar haka kuwa (kai ma) za a manta da kai a yau.”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 127

وَكَذَٰلِكَ نَجۡزِي مَنۡ أَسۡرَفَ وَلَمۡ يُؤۡمِنۢ بِـَٔايَٰتِ رَبِّهِۦۚ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَشَدُّ وَأَبۡقَىٰٓ

Kamar haka Muke saka wa (duk) wanda ya yi varna kuma bai yi imani da ayoyin Ubangijinsa ba. Kuma azabar lahira tabbas ta fi tsanani ta kuma fi dawwama



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 128

أَفَلَمۡ يَهۡدِ لَهُمۡ كَمۡ أَهۡلَكۡنَا قَبۡلَهُم مِّنَ ٱلۡقُرُونِ يَمۡشُونَ فِي مَسَٰكِنِهِمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّأُوْلِي ٱلنُّهَىٰ

Yanzu (mutanen Makka) ba su gane cewa al’ummu nawa muka hallaka a gabaninsu ba waxanda suna wucewa ta gidajensu? Lalle a game da wannan akwai ayoyi ga ma’abota hankali



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 129

وَلَوۡلَا كَلِمَةٞ سَبَقَتۡ مِن رَّبِّكَ لَكَانَ لِزَامٗا وَأَجَلٞ مُّسَمّٗى

Ba don kuwa wata kalma da ta rigaya daga Ubangijinka ba[1], da kuma wani wa’adi qayyadajje[2], to da (azaba) ta zama dole (a kansu tun a duniya)


1- Watau alqawari na cewa ba zai hallakar da kowa ba har sai ya tsayar masa da hujja.


2- Watau ajali na rayuwa da ya riga ya qayyade wa kowa a duniya.


Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 130

فَٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَا يَقُولُونَ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ قَبۡلَ طُلُوعِ ٱلشَّمۡسِ وَقَبۡلَ غُرُوبِهَاۖ وَمِنۡ ءَانَآيِٕ ٱلَّيۡلِ فَسَبِّحۡ وَأَطۡرَافَ ٱلنَّهَارِ لَعَلَّكَ تَرۡضَىٰ

Sai ka yi haquri a kan abin da suke faxa, kuma ka yi tasbihi da godiyar Ubangijinka kafin hudowar rana, da kuma gabanin faxuwarta; a (wasu) lokatai na dare kuma ka yi tasbihi, da kuma gefukan wuni don (a saka maka da abin da) za ka yarda



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 131

وَلَا تَمُدَّنَّ عَيۡنَيۡكَ إِلَىٰ مَا مَتَّعۡنَا بِهِۦٓ أَزۡوَٰجٗا مِّنۡهُمۡ زَهۡرَةَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا لِنَفۡتِنَهُمۡ فِيهِۚ وَرِزۡقُ رَبِّكَ خَيۡرٞ وَأَبۡقَىٰ

Kada kuma ka zura idanuwanka a kan dangogin daxin da Muka jiyar da wasu daga cikinsu, na adon rayuwar duniya ne don Mu jarrabe su da shi. Arzikin Ubangijinka kuwa (shi) ya fi alheri ya kuma fi dawwama



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 132

وَأۡمُرۡ أَهۡلَكَ بِٱلصَّلَوٰةِ وَٱصۡطَبِرۡ عَلَيۡهَاۖ لَا نَسۡـَٔلُكَ رِزۡقٗاۖ نَّحۡنُ نَرۡزُقُكَۗ وَٱلۡعَٰقِبَةُ لِلتَّقۡوَىٰ

Ka kuma umarci iyalinka da (tsai da) salla, kuma ka dawwama a kanta; ba Ma neman ka arzuta (kanka da iyalinka); Mu ne za Mu arzuta ka. Kyakkyawan qarshe kuwa yana ga masu taqawa



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 133

وَقَالُواْ لَوۡلَا يَأۡتِينَا بِـَٔايَةٖ مِّن رَّبِّهِۦٓۚ أَوَلَمۡ تَأۡتِهِم بَيِّنَةُ مَا فِي ٱلصُّحُفِ ٱلۡأُولَىٰ

Suka kuma ce: “Me ya sa bai zo mana da wata aya daga Ubangijinsa ba?” Yanzu hujjar abin da yake cikin littattafan farko ba ta zo musu ba (wato Alqur’ani)?



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 134

وَلَوۡ أَنَّآ أَهۡلَكۡنَٰهُم بِعَذَابٖ مِّن قَبۡلِهِۦ لَقَالُواْ رَبَّنَا لَوۡلَآ أَرۡسَلۡتَ إِلَيۡنَا رَسُولٗا فَنَتَّبِعَ ءَايَٰتِكَ مِن قَبۡلِ أَن نَّذِلَّ وَنَخۡزَىٰ

In da a ce Mun hallaka su ne da azaba tun gabaninsa (wato Annabi Muhammadu), to da sun ce: “Ubangijinmu, me ya sa ba Ka aiko mana da wani manzo ba sai mu bi ayoyinka tun kafin mu qasqanta mu kuma wulaqanta?”



Sourate: Suratu Xa Ha

Verset : 135

قُلۡ كُلّٞ مُّتَرَبِّصٞ فَتَرَبَّصُواْۖ فَسَتَعۡلَمُونَ مَنۡ أَصۡحَٰبُ ٱلصِّرَٰطِ ٱلسَّوِيِّ وَمَنِ ٱهۡتَدَىٰ

Ka ce (da su): “Kowanne (ni da ku) mai sauraro ne, sai ku saurara; to ba da daxewa ba za ku san su wane ne ma’abota hanya madaidaiciya, kuma su wane ne suke kan shiriya.”