Sourate: Suratul Qamar

Verset : 40

وَلَقَدۡ يَسَّرۡنَا ٱلۡقُرۡءَانَ لِلذِّكۡرِ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun sauqaqe Alqur’ani don tunatarwa, to ko akwai mai wa’azantuwa?



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 41

وَلَقَدۡ جَآءَ ءَالَ فِرۡعَوۡنَ ٱلنُّذُرُ

Kuma haqiqa gargaxi ya zo wa mutanen Fir’auna



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 42

كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا كُلِّهَا فَأَخَذۡنَٰهُمۡ أَخۡذَ عَزِيزٖ مُّقۡتَدِرٍ

Suka qaryata ayoyinmu dukkaninsu, sai Muka kama su irin kamu na Mabuwayi, Mai iko



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 43

أَكُفَّارُكُمۡ خَيۡرٞ مِّنۡ أُوْلَـٰٓئِكُمۡ أَمۡ لَكُم بَرَآءَةٞ فِي ٱلزُّبُرِ

Yanzu kafiranku (ku mutanen Makka) su ne suka fi waxancan alheri, ko kuwa kuna da wata hanya ta kuvuta ne a cikin littattafan da aka saukar?



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 44

أَمۡ يَقُولُونَ نَحۡنُ جَمِيعٞ مُّنتَصِرٞ

A’a, suna dai cewa ne: “Mu jama’a ce wadda za ta ci nasara.”



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 45

سَيُهۡزَمُ ٱلۡجَمۡعُ وَيُوَلُّونَ ٱلدُّبُرَ

To ba da daxewa ba za a karya jama’ar tasu[1], su kuma su ba da baya


1- Haka kuwa ya faru a yaqin Badar lokacin da aka karya lagon kafiran Makka, aka kashe manyansu da dama.


Sourate: Suratul Qamar

Verset : 46

بَلِ ٱلسَّاعَةُ مَوۡعِدُهُمۡ وَٱلسَّاعَةُ أَدۡهَىٰ وَأَمَرُّ

A’a, alqiyama ita ce lokacin yi musu azaba, alqiyama kuwa ita ta fi bala’i, ta kuma fi xaci



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 47

إِنَّ ٱلۡمُجۡرِمِينَ فِي ضَلَٰلٖ وَسُعُرٖ

Lalle masu manyan laifuka suna cikin vata da azabar wuta



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 48

يَوۡمَ يُسۡحَبُونَ فِي ٱلنَّارِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ ذُوقُواْ مَسَّ سَقَرَ

Ranar da za a ja su cikin wuta a kan fuskokinsu (a ce da su): “Ku xanxani azabar wutar Saqara.”



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 49

إِنَّا كُلَّ شَيۡءٍ خَلَقۡنَٰهُ بِقَدَرٖ

Lalle Mu, kowane abu Mun halitta shi da qaddara



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 50

وَمَآ أَمۡرُنَآ إِلَّا وَٰحِدَةٞ كَلَمۡحِۭ بِٱلۡبَصَرِ

Kuma al’amarinmu bai zamanto ba face kalma xaya kamar qiftawar ido



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 51

وَلَقَدۡ أَهۡلَكۡنَآ أَشۡيَاعَكُمۡ فَهَلۡ مِن مُّدَّكِرٖ

Haqiqa kuma Mun hallakar da ire-irenku[1], to ko akwai mai wa’azantuwa?


1- Watau kafirai irinsu masu taurin kai.


Sourate: Suratul Qamar

Verset : 52

وَكُلُّ شَيۡءٖ فَعَلُوهُ فِي ٱلزُّبُرِ

Kuma kowane abu da suka aikata yana cikin littattafai



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 53

وَكُلُّ صَغِيرٖ وَكَبِيرٖ مُّسۡتَطَرٌ

Kowane qaramin abu da babba kuma suna nan a rubuce



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 54

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَنَهَرٖ

Lalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da qoramu



Sourate: Suratul Qamar

Verset : 55

فِي مَقۡعَدِ صِدۡقٍ عِندَ مَلِيكٖ مُّقۡتَدِرِۭ

A mazauni na gaskiya a wurin Mai mulki, Mai iko



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 1

ٱلرَّحۡمَٰنُ

(Allah) Mai rahama



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 2

عَلَّمَ ٱلۡقُرۡءَانَ

Shi Ya koyar da Alqur’ani



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 3

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ

Ya halicci mutum



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 4

عَلَّمَهُ ٱلۡبَيَانَ

Ya koyar da shi bayani



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 5

ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ بِحُسۡبَانٖ

Rana da wata (suna tafiya) a tsare



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 6

وَٱلنَّجۡمُ وَٱلشَّجَرُ يَسۡجُدَانِ

Tsirrai da bishiyoyi suna yin sujjada[1]


1- Watau tsirrai waxanda ba sa tashi tsaye da bishiyoyi masu tsayawa a kan sandunansu.


Sourate: Suratur Rahman

Verset : 7

وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلۡمِيزَانَ

Sama kuma Ya xaga ta, Ya kuma kafa adalci



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 8

أَلَّا تَطۡغَوۡاْ فِي ٱلۡمِيزَانِ

Don kada ku yi zalunci a abin awo



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 9

وَأَقِيمُواْ ٱلۡوَزۡنَ بِٱلۡقِسۡطِ وَلَا تُخۡسِرُواْ ٱلۡمِيزَانَ

Kuma ku tabbatar da awo da adalci kada kuma ku tauye abin awo



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 10

وَٱلۡأَرۡضَ وَضَعَهَا لِلۡأَنَامِ

Qasa kuma Ya yi ta saboda talikai



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 11

فِيهَا فَٰكِهَةٞ وَٱلنَّخۡلُ ذَاتُ ٱلۡأَكۡمَامِ

A cikinta akwai abin marmari da dabinai ma’abota kwasfa



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 12

وَٱلۡحَبُّ ذُو ٱلۡعَصۡفِ وَٱلرَّيۡحَانُ

Da qwayoyi ma’abota qaiqayi da kuma ganyaye masu qanshi



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 13

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

To da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Sourate: Suratur Rahman

Verset : 14

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِن صَلۡصَٰلٖ كَٱلۡفَخَّارِ

Ya halicci mutum daga busasshen tavo kamar kasko