Sourate: Suratut Tauba

Verset : 86

وَإِذَآ أُنزِلَتۡ سُورَةٌ أَنۡ ءَامِنُواْ بِٱللَّهِ وَجَٰهِدُواْ مَعَ رَسُولِهِ ٱسۡتَـٔۡذَنَكَ أُوْلُواْ ٱلطَّوۡلِ مِنۡهُمۡ وَقَالُواْ ذَرۡنَا نَكُن مَّعَ ٱلۡقَٰعِدِينَ

Idan kuma aka saukar da wata sura mai cewa: “Ku yi imani da Allah kuma ku yi yaqi tare da Manzonsa,” sai masu wadata daga cikinsu su nemi izininka su ce: “Qyale mu mu kasance tare da masu zama (a gida, wato mata da yara).”



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 87

رَضُواْ بِأَن يَكُونُواْ مَعَ ٱلۡخَوَالِفِ وَطُبِعَ عَلَىٰ قُلُوبِهِمۡ فَهُمۡ لَا يَفۡقَهُونَ

Sun yarda da su kasance tare da mata masu zaman gida, an kuma doxe zukatansu, saboda haka ba sa ganewa



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 88

لَٰكِنِ ٱلرَّسُولُ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ جَٰهَدُواْ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡۚ وَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمُ ٱلۡخَيۡرَٰتُۖ وَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

Sai dai shi Manzo da waxanda suka yi imani tare da shi sun yi yaqi da dukiyoyinsu da kuma kawunansu. Waxannan kuwa suna da alherai; kuma waxannan su ne marabauta



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 89

أَعَدَّ ٱللَّهُ لَهُمۡ جَنَّـٰتٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

Allah Ya tanadar musu da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dawwama a cikinsu. Wannan shi ne rabo mai girma



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 90

وَجَآءَ ٱلۡمُعَذِّرُونَ مِنَ ٱلۡأَعۡرَابِ لِيُؤۡذَنَ لَهُمۡ وَقَعَدَ ٱلَّذِينَ كَذَبُواْ ٱللَّهَ وَرَسُولَهُۥۚ سَيُصِيبُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Masu kawo uzurin qarya daga mutanen qauye kuma suka zo don a yi musu izini, sai kuma waxanda suka yi wa Allah da Manzonsa qarya suka yi zamansu (ba tare da kawo hanzari ba). To azaba mai raxaxi za ta samu waxanda suka kafirta daga cikinsu



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 91

لَّيۡسَ عَلَى ٱلضُّعَفَآءِ وَلَا عَلَى ٱلۡمَرۡضَىٰ وَلَا عَلَى ٱلَّذِينَ لَا يَجِدُونَ مَا يُنفِقُونَ حَرَجٌ إِذَا نَصَحُواْ لِلَّهِ وَرَسُولِهِۦۚ مَا عَلَى ٱلۡمُحۡسِنِينَ مِن سَبِيلٖۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Babu wani laifi a kan raunana ko marasa lafiya ko kuma waxanda ba su samu abin da za su ciyar ba (don talauci), matuqar dai sun tsarkake zuciyarsu ga Allah da Manzonsa. Babu wata hanya (ta xora laifi) ga masu kyautatawa. Allah kuwa Mai gafara ne, Mai jin qai



Sourate: Suratut Tauba

Verset : 92

وَلَا عَلَى ٱلَّذِينَ إِذَا مَآ أَتَوۡكَ لِتَحۡمِلَهُمۡ قُلۡتَ لَآ أَجِدُ مَآ أَحۡمِلُكُمۡ عَلَيۡهِ تَوَلَّواْ وَّأَعۡيُنُهُمۡ تَفِيضُ مِنَ ٱلدَّمۡعِ حَزَنًا أَلَّا يَجِدُواْ مَا يُنفِقُونَ

Haka kuma babu (laifi) a kan waxanda idan sun zo maka don ka ba su abin hawa sai ka ce: “Ba ni da abin hawan da zan ba ku,” sai suka juya idanuwansu suna kwararar da hawaye don baqin cikin ba su sami abin da za su ciyar ba