Sourate: Suratul An’am

Verset : 52

وَلَا تَطۡرُدِ ٱلَّذِينَ يَدۡعُونَ رَبَّهُم بِٱلۡغَدَوٰةِ وَٱلۡعَشِيِّ يُرِيدُونَ وَجۡهَهُۥۖ مَا عَلَيۡكَ مِنۡ حِسَابِهِم مِّن شَيۡءٖ وَمَا مِنۡ حِسَابِكَ عَلَيۡهِم مِّن شَيۡءٖ فَتَطۡرُدَهُمۡ فَتَكُونَ مِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma kada ka kori waxannan da suke bauta wa Ubangijinsu safe da yamma, suna nufin Fuskarsa (watau suna yi don Shi kaxai); ba wani abu na haqqinsu a kanka, kuma babu wani abu na haqqinka a kansu, balle ka kore su, sai ka kasance cikin azzalumai.[1]


1- Daga nan zuwa aya ta 54 suna magana ne game da mushirikan Larabawa da suka nuna wa Manzon Allah () cewa za su musulunta amma da sharaxin zai kori Musulmi talakawa daga majalisarsa don kada su riqa yi musu rashin kunya. Sai Allah () ya hana shi aikata hakan.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 53

وَكَذَٰلِكَ فَتَنَّا بَعۡضَهُم بِبَعۡضٖ لِّيَقُولُوٓاْ أَهَـٰٓؤُلَآءِ مَنَّ ٱللَّهُ عَلَيۡهِم مِّنۢ بَيۡنِنَآۗ أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَعۡلَمَ بِٱلشَّـٰكِرِينَ

Kuma kamar haka ne Muka jarrabi sashinsu da sashi, domin su ce: “Yanzu waxannan su ne Allah Ya yi wa baiwa daga cikinmu?” Ashe Allah ba Shi ne Mafi sanin masu godiya (gare Shi) ba?



Sourate: Suratul An’am

Verset : 54

وَإِذَا جَآءَكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِـَٔايَٰتِنَا فَقُلۡ سَلَٰمٌ عَلَيۡكُمۡۖ كَتَبَ رَبُّكُمۡ عَلَىٰ نَفۡسِهِ ٱلرَّحۡمَةَ أَنَّهُۥ مَنۡ عَمِلَ مِنكُمۡ سُوٓءَۢا بِجَهَٰلَةٖ ثُمَّ تَابَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَصۡلَحَ فَأَنَّهُۥ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Kuma idan waxanda suke yin imani da ayoyinmu sun zo wurinka, to ka ce: “Sallama a gare ku;” Ubangijinku Ya wajabta wa kansa yin rahama cewa, lalle cikinku duk wanda ya aikata wani mummunan aiki bisa ga jahilci, sannan daga baya ya tuba kuma ya kyautata aiki, to Shi Mai gafara ne, Mai jin qai.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 55

وَكَذَٰلِكَ نُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ وَلِتَسۡتَبِينَ سَبِيلُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Kuma kamar haka ne Muke rarrabe ayoyi domin tafarkin masu laifuka ya bayyana



Sourate: Suratul An’am

Verset : 56

قُلۡ إِنِّي نُهِيتُ أَنۡ أَعۡبُدَ ٱلَّذِينَ تَدۡعُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِۚ قُل لَّآ أَتَّبِعُ أَهۡوَآءَكُمۡ قَدۡ ضَلَلۡتُ إِذٗا وَمَآ أَنَا۠ مِنَ ٱلۡمُهۡتَدِينَ

Ka ce: “Lalle ni an hana ni in bauta wa abubuwan da kuke bauta wa ba Allah ba.” Ka ce: “Ba zan bi soye-soyen zukatanku ba, (idan har zan bi son zuciyarku), to haqiqa na vata, kuma da ban zama cikin shiryayyu ba kenan”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 57

قُلۡ إِنِّي عَلَىٰ بَيِّنَةٖ مِّن رَّبِّي وَكَذَّبۡتُم بِهِۦۚ مَا عِندِي مَا تَسۡتَعۡجِلُونَ بِهِۦٓۚ إِنِ ٱلۡحُكۡمُ إِلَّا لِلَّهِۖ يَقُصُّ ٱلۡحَقَّۖ وَهُوَ خَيۡرُ ٱلۡفَٰصِلِينَ

Ka ce: “Lalle ni ina kan hujja mai qarfi daga Ubangijina, ku kuma kun qaryata ta. Abin da kuke so in gaggauto muku da shi, ba a hannuna yake ba. Hukunci yana hannun Allah ne Shi kaxai; Shi ne Yake bayar da labarin gaskiya, kuma Shi ne Fiyayyen masu rarrabewa (tsakanin qarya da gaskiya)”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 58

قُل لَّوۡ أَنَّ عِندِي مَا تَسۡتَعۡجِلُونَ بِهِۦ لَقُضِيَ ٱلۡأَمۡرُ بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡۗ وَٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِٱلظَّـٰلِمِينَ

Ka ce: “Da a ce abin da kuke nema a gaggauto muku da shi a wurina yake, to tabbas da ta faru ta qare tsakanina da ku. Kuma Allah Shi ne Mafi sanin su wane ne azzalumai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 59

۞وَعِندَهُۥ مَفَاتِحُ ٱلۡغَيۡبِ لَا يَعۡلَمُهَآ إِلَّا هُوَۚ وَيَعۡلَمُ مَا فِي ٱلۡبَرِّ وَٱلۡبَحۡرِۚ وَمَا تَسۡقُطُ مِن وَرَقَةٍ إِلَّا يَعۡلَمُهَا وَلَا حَبَّةٖ فِي ظُلُمَٰتِ ٱلۡأَرۡضِ وَلَا رَطۡبٖ وَلَا يَابِسٍ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٖ

“Kuma mabuxan gaibu a wurinsa suke Shi kaxai[1], babu wanda ya san su sai Shi. Kuma Ya san qididdigar abin da yake kan tudu da na ruwa. Kuma babu wani ganyen itace da zai faxo, face sai Ya san da shi, kuma ba wata qwaya da take cikin duhun qasa, kuma ba wani xanyen abu ko busasshe, face (bayaninsa) yana cikin Littafi mabayyani


1- Mabuxan gaibu biyar ne babu wanda ya san su sai Allah. Su ne suka zo a qarshen Suratu Luqman aya ta 34.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 60

وَهُوَ ٱلَّذِي يَتَوَفَّىٰكُم بِٱلَّيۡلِ وَيَعۡلَمُ مَا جَرَحۡتُم بِٱلنَّهَارِ ثُمَّ يَبۡعَثُكُمۡ فِيهِ لِيُقۡضَىٰٓ أَجَلٞ مُّسَمّٗىۖ ثُمَّ إِلَيۡهِ مَرۡجِعُكُمۡ ثُمَّ يُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

“Kuma Shi ne Yake karvar rayukanku da daddare[1], kuma Ya san abin da kuka aikata da rana, sannan Ya tayar da ku a cikinta (ranar), har zuwa lokacin da zai zartar da wani ajali sananne, sannan zuwa gare Shi ne makomarku take, sannan zai ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa


1- Watau lokacin barcinku; ya riqe ran da ya hukunta masa mutuwa, ya sako wanda lokacin mutuwarsa bai zo ba. duba Suratuz Zumar aya ta 42.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 61

وَهُوَ ٱلۡقَاهِرُ فَوۡقَ عِبَادِهِۦۖ وَيُرۡسِلُ عَلَيۡكُمۡ حَفَظَةً حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَ أَحَدَكُمُ ٱلۡمَوۡتُ تَوَفَّتۡهُ رُسُلُنَا وَهُمۡ لَا يُفَرِّطُونَ

“Kuma Shi ne wanda Yake da iko a kan bayinsa, kuma Yana aiko muku masu tsaro, har zuwa lokacin da mutuwa za ta zo wa xayanku, sai manzanninmu su karvi ransa, kuma su ba sa yin sakaci



Sourate: Suratul An’am

Verset : 62

ثُمَّ رُدُّوٓاْ إِلَى ٱللَّهِ مَوۡلَىٰهُمُ ٱلۡحَقِّۚ أَلَا لَهُ ٱلۡحُكۡمُ وَهُوَ أَسۡرَعُ ٱلۡحَٰسِبِينَ

“Sannan sai a mayar da su zuwa ga Allah Majivincin lamarinsu na gaskiya. Ku saurara, dukkan hukunci nasa ne, kuma Shi ne Mafi gaggawar masu hisabi.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 63

قُلۡ مَن يُنَجِّيكُم مِّن ظُلُمَٰتِ ٱلۡبَرِّ وَٱلۡبَحۡرِ تَدۡعُونَهُۥ تَضَرُّعٗا وَخُفۡيَةٗ لَّئِنۡ أَنجَىٰنَا مِنۡ هَٰذِهِۦ لَنَكُونَنَّ مِنَ ٱلشَّـٰكِرِينَ

Ka ce: “Wane ne yake tserar da ku daga cikin duffai na tudu da na kogi, kuna roqon sa a fili da a voye (cewa): “Tabbas, in da zai tserar da mu daga wannan, to lalle za mu kasance cikin masu godiya.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 64

قُلِ ٱللَّهُ يُنَجِّيكُم مِّنۡهَا وَمِن كُلِّ كَرۡبٖ ثُمَّ أَنتُمۡ تُشۡرِكُونَ

Ka ce: “Allah ne zai tserar da ku daga cikinsa (tsoron), da ma duk wani baqin ciki, sannan sai ga ku kuna yin shirka.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 65

قُلۡ هُوَ ٱلۡقَادِرُ عَلَىٰٓ أَن يَبۡعَثَ عَلَيۡكُمۡ عَذَابٗا مِّن فَوۡقِكُمۡ أَوۡ مِن تَحۡتِ أَرۡجُلِكُمۡ أَوۡ يَلۡبِسَكُمۡ شِيَعٗا وَيُذِيقَ بَعۡضَكُم بَأۡسَ بَعۡضٍۗ ٱنظُرۡ كَيۡفَ نُصَرِّفُ ٱلۡأٓيَٰتِ لَعَلَّهُمۡ يَفۡقَهُونَ

Ka ce: “Shi ne Mai cikakken ikon Ya aiko muku da azaba ta samanku ko ta qarqashin qafafuwanku ko Ya mayar da ku qungiyoyi daban-daban, kuma Ya xanxana wa sashinku azabar sashi.” Duba ka ga yadda Muke bayyana ayoyi, don su fahimta



Sourate: Suratul An’am

Verset : 66

وَكَذَّبَ بِهِۦ قَوۡمُكَ وَهُوَ ٱلۡحَقُّۚ قُل لَّسۡتُ عَلَيۡكُم بِوَكِيلٖ

Kuma mutanenka sun qaryata shi (Alqur’ani) alhali shi ne gaskiya. Ka ce: “Ni ba wakili ne a kanku ba



Sourate: Suratul An’am

Verset : 67

لِّكُلِّ نَبَإٖ مُّسۡتَقَرّٞۚ وَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَ

“Kowane labari yana da lokaci ne na musamman. Kuma da sannu za ku sani.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 68

وَإِذَا رَأَيۡتَ ٱلَّذِينَ يَخُوضُونَ فِيٓ ءَايَٰتِنَا فَأَعۡرِضۡ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ يَخُوضُواْ فِي حَدِيثٍ غَيۡرِهِۦۚ وَإِمَّا يُنسِيَنَّكَ ٱلشَّيۡطَٰنُ فَلَا تَقۡعُدۡ بَعۡدَ ٱلذِّكۡرَىٰ مَعَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Kuma idan ka ga waxanda suke kutsawa cikin ayoyinmu (suna izgili), to ka rabu da su, har sai sun canja wani zancen da ba wancan ba. Amma in da Shaixan zai mantar da kai kuwa, to bayan ka tuna kar ka sake zama tare da azzalumai



Sourate: Suratul An’am

Verset : 69

وَمَا عَلَى ٱلَّذِينَ يَتَّقُونَ مِنۡ حِسَابِهِم مِّن شَيۡءٖ وَلَٰكِن ذِكۡرَىٰ لَعَلَّهُمۡ يَتَّقُونَ

Kuma babu wani laifi a kan waxanda suke tsoron haxuwarsu da Allah (don sun zauna da su), sai dai kuma (dole su yi) musu wa’azi don su tsorata



Sourate: Suratul An’am

Verset : 70

وَذَرِ ٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ دِينَهُمۡ لَعِبٗا وَلَهۡوٗا وَغَرَّتۡهُمُ ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَاۚ وَذَكِّرۡ بِهِۦٓ أَن تُبۡسَلَ نَفۡسُۢ بِمَا كَسَبَتۡ لَيۡسَ لَهَا مِن دُونِ ٱللَّهِ وَلِيّٞ وَلَا شَفِيعٞ وَإِن تَعۡدِلۡ كُلَّ عَدۡلٖ لَّا يُؤۡخَذۡ مِنۡهَآۗ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ أُبۡسِلُواْ بِمَا كَسَبُواْۖ لَهُمۡ شَرَابٞ مِّنۡ حَمِيمٖ وَعَذَابٌ أَلِيمُۢ بِمَا كَانُواْ يَكۡفُرُونَ

Ka rabu da waxanda suka xauki addininsu wasa da sharholiya, rayuwarsu ta duniya kuma ta ruxe su. Ka kuma yi gargaxi da shi (Alqur’ani), saboda kada a jarrabi rai da abin da ya aikata wanda ba ya da wani mataimaki ko mai ceto ban da Allah, ko da kuwa (ran) ya ba da kowace irin fansa ba za a karva ba daga gare shi. Waxancan su ne waxanda aka kange (don yi musu azaba) saboda abin da suka aikata; suna da abin sha na tafasasshen ruwa da kuma azaba mai raxaxi saboda abin da suka zamanto suna kafircewa (da shi)



Sourate: Suratul An’am

Verset : 71

قُلۡ أَنَدۡعُواْ مِن دُونِ ٱللَّهِ مَا لَا يَنفَعُنَا وَلَا يَضُرُّنَا وَنُرَدُّ عَلَىٰٓ أَعۡقَابِنَا بَعۡدَ إِذۡ هَدَىٰنَا ٱللَّهُ كَٱلَّذِي ٱسۡتَهۡوَتۡهُ ٱلشَّيَٰطِينُ فِي ٱلۡأَرۡضِ حَيۡرَانَ لَهُۥٓ أَصۡحَٰبٞ يَدۡعُونَهُۥٓ إِلَى ٱلۡهُدَى ٱئۡتِنَاۗ قُلۡ إِنَّ هُدَى ٱللَّهِ هُوَ ٱلۡهُدَىٰۖ وَأُمِرۡنَا لِنُسۡلِمَ لِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ka ce: “Shin yanzu ma riqa bauta wa wani wanda ba Allah ba, abin da ba zai amfane mu ba, kuma ba zai cutar da mu ba, mu koma gidan jiya (kafirai) bayan kuwa Allah Ya shiryar da mu, (mu koma) kamar wanda shaixanu suka vatar da shi yana ta ximuwa a bayan qasa, ga shi da wasu abokai suna kiran sa zuwa ga shiriya, (suna cewa): “Ka zo (mu bi tafarkin shiriya)[1].” Ka ce: “Lalle shiriyar Allah fa ita kaxai ce shiriya; kuma mu an umarce mu da mu miqa wuya ne kaxai ga Ubangijin talikai


1- Misali ne na wanda ya saki Musulunci ya kama shirka ko vata, ya zama kamar mutumin da aljanu suka xauke shi suka tafi da shi suka jefar da shi a qurgurmin daji. Don haka ya yi nisan da ba zai ji kira ba, balle ya gane hanyar dawowa.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 72

وَأَنۡ أَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَٱتَّقُوهُۚ وَهُوَ ٱلَّذِيٓ إِلَيۡهِ تُحۡشَرُونَ

“Kuma ku tsayar da salla kuma ku kiyaye dokokinsa. Kuma Shi ne Wanda za a tara ku zuwa gare Shi



Sourate: Suratul An’am

Verset : 73

وَهُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۖ وَيَوۡمَ يَقُولُ كُن فَيَكُونُۚ قَوۡلُهُ ٱلۡحَقُّۚ وَلَهُ ٱلۡمُلۡكُ يَوۡمَ يُنفَخُ فِي ٱلصُّورِۚ عَٰلِمُ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِۚ وَهُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡخَبِيرُ

“Kuma Shi ne Wanda ya halicci sammai da qasa da gaskiya; kuma (ku tuna) ranar da zai ce da abu: ‘Kasance!’ Nan take sai ya kasance. Maganarsa gaskiya ce. Kuma Shi ne Yake da cikakken mulki a ranar da za a busa qaho Masanin gaibu da sarari, kuma Shi ne Mai hikima, Mai cikakken sani.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 74

۞وَإِذۡ قَالَ إِبۡرَٰهِيمُ لِأَبِيهِ ءَازَرَ أَتَتَّخِذُ أَصۡنَامًا ءَالِهَةً إِنِّيٓ أَرَىٰكَ وَقَوۡمَكَ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Kuma (ka tuna) lokacin da Ibrahimu ya ce da babansa Azaru: “Yanzu ka riqi gumaka a matsayin alloli? Lalle ni ina ganin ka kai da mutanenka, kuna cikin vata mabayyani.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 75

وَكَذَٰلِكَ نُرِيٓ إِبۡرَٰهِيمَ مَلَكُوتَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَلِيَكُونَ مِنَ ٱلۡمُوقِنِينَ

Kuma kamar haka ne Muke nuna wa Ibrahimu halittun sammai da qasa, domin ya kasance cikin masu sakankancewa



Sourate: Suratul An’am

Verset : 76

فَلَمَّا جَنَّ عَلَيۡهِ ٱلَّيۡلُ رَءَا كَوۡكَبٗاۖ قَالَ هَٰذَا رَبِّيۖ فَلَمَّآ أَفَلَ قَالَ لَآ أُحِبُّ ٱلۡأٓفِلِينَ

To yayin da dare ya lulluve shi, ya ga tauraro, sai ya ce; “Wannan shi ne ubangijina;”[1] sannan yayin da ya vace, sai ya ce: “Ni fa ba na son abubuwa masu gushewa.”


1- Daga wannan ayar zuwa aya ta 79 Allah () ya koya wa Annabi Ibrahim () hanyar da zai yi wa mutanensa wa’azi cikin hikima da laluma don jan hankalinsu su fahimci abubuwan da suke bauta wa ba ababen bauta ne na gaskiya ba.


Sourate: Suratul An’am

Verset : 77

فَلَمَّا رَءَا ٱلۡقَمَرَ بَازِغٗا قَالَ هَٰذَا رَبِّيۖ فَلَمَّآ أَفَلَ قَالَ لَئِن لَّمۡ يَهۡدِنِي رَبِّي لَأَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلضَّآلِّينَ

Sa’annan yayin da ya ga wata ya fito, sai ya ce; “Wannan shi ne ubangijina;” sannan yayin da ya gushe, sai ya ce: “Lalle idan Ubangijina bai shiryar da ni ba, haqiqa zan kasance daga cikin mutane vatattu.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 78

فَلَمَّا رَءَا ٱلشَّمۡسَ بَازِغَةٗ قَالَ هَٰذَا رَبِّي هَٰذَآ أَكۡبَرُۖ فَلَمَّآ أَفَلَتۡ قَالَ يَٰقَوۡمِ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تُشۡرِكُونَ

Sannan yayin da ya ga rana ta hudo, sai ya ce: “Wannan shi ne ubangijina, wannan shi ya fi girma;” sannan yayin da ta vace, sai ya ce: “Ya ku mutanena, haqiqa ni ba ruwana da abin da kuke haxa Allah da shi



Sourate: Suratul An’am

Verset : 79

إِنِّي وَجَّهۡتُ وَجۡهِيَ لِلَّذِي فَطَرَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ حَنِيفٗاۖ وَمَآ أَنَا۠ مِنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

“Lalle ni kam na juyar da fuskata ga Wanda Ya halicci sammai da qasa, ina mai kauce wa varna kuma ni ba na cikin masu yin shirka.”



Sourate: Suratul An’am

Verset : 80

وَحَآجَّهُۥ قَوۡمُهُۥۚ قَالَ أَتُحَـٰٓجُّوٓنِّي فِي ٱللَّهِ وَقَدۡ هَدَىٰنِۚ وَلَآ أَخَافُ مَا تُشۡرِكُونَ بِهِۦٓ إِلَّآ أَن يَشَآءَ رَبِّي شَيۡـٔٗاۚ وَسِعَ رَبِّي كُلَّ شَيۡءٍ عِلۡمًاۚ أَفَلَا تَتَذَكَّرُونَ

Kuma mutanensa sun yi jayayya da shi; (sai) ya ce: “Shin yanzu kwa riqa jayayya da ni game da (kaxaitakar) Allah, alhalin kuwa Ya shiryar da ni? Kuma ba na jin tsoron abin da kuke sanya wa Allah kishiya da shi, sai abin da Ubangijina Ya ga dama. Kuma ilimin Ubangijina ya yalwaci komai. Shin ba za ku wa’azantu ba?



Sourate: Suratul An’am

Verset : 81

وَكَيۡفَ أَخَافُ مَآ أَشۡرَكۡتُمۡ وَلَا تَخَافُونَ أَنَّكُمۡ أَشۡرَكۡتُم بِٱللَّهِ مَا لَمۡ يُنَزِّلۡ بِهِۦ عَلَيۡكُمۡ سُلۡطَٰنٗاۚ فَأَيُّ ٱلۡفَرِيقَيۡنِ أَحَقُّ بِٱلۡأَمۡنِۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

“To ta qaqa kuwa zan ji tsoron abin da kuka tara da (Allah), alhali ku kuma ba kwa jin tsoron kun sanya wa Allah kishiya, abin da kuwa bai saukar muku da wata hujja a kai ba? To wane vangare ne cikin vangarori biyu, ya fi dacewa da samun aminci; in har kun kasance kun sani?