أَوۡ تَكُونَ لَكَ جَنَّةٞ مِّن نَّخِيلٖ وَعِنَبٖ فَتُفَجِّرَ ٱلۡأَنۡهَٰرَ خِلَٰلَهَا تَفۡجِيرًا
“Ko kuma ya zamana kana da wata gona ta dabinai da inabi, sai kuma ka vuvvugo da qoramu ta tsakiyarta su kwarara sosai
أَوۡ تُسۡقِطَ ٱلسَّمَآءَ كَمَا زَعَمۡتَ عَلَيۡنَا كِسَفًا أَوۡ تَأۡتِيَ بِٱللَّهِ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ قَبِيلًا
“Ko kuma ka rufto da sama a kanmu, kamar yadda ka riya, ta faxo yanki-yanki, ko kuma ka zo da Allah da kuma mala’iku (mu gan su) ido-da-ido!
أَوۡ يَكُونَ لَكَ بَيۡتٞ مِّن زُخۡرُفٍ أَوۡ تَرۡقَىٰ فِي ٱلسَّمَآءِ وَلَن نُّؤۡمِنَ لِرُقِيِّكَ حَتَّىٰ تُنَزِّلَ عَلَيۡنَا كِتَٰبٗا نَّقۡرَؤُهُۥۗ قُلۡ سُبۡحَانَ رَبِّي هَلۡ كُنتُ إِلَّا بَشَرٗا رَّسُولٗا
“Ko kuma ya zamana kana da wani gida na zinari, ko kuma ka hau sama, ba kuwa za mu amince da hawan naka ba har sai ka saukar mana da wani littafi da za mu karanta shi.” Ka ce (da su): “Tsarki ya tabbata ga Ubangijina, ni ba kowa ba ne face mutum Manzo.”
وَمَا مَنَعَ ٱلنَّاسَ أَن يُؤۡمِنُوٓاْ إِذۡ جَآءَهُمُ ٱلۡهُدَىٰٓ إِلَّآ أَن قَالُوٓاْ أَبَعَثَ ٱللَّهُ بَشَرٗا رَّسُولٗا
Kuma babu abin da ya hana kafirai su yi imani lokacin da shiriya ta zo musu, sai cewar da suka yi: “Yanzu Allah ne zai aiko mutum a matsayin manzo?”
قُل لَّوۡ كَانَ فِي ٱلۡأَرۡضِ مَلَـٰٓئِكَةٞ يَمۡشُونَ مُطۡمَئِنِّينَ لَنَزَّلۡنَا عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ مَلَكٗا رَّسُولٗا
Ka ce: “Da mala’iku ne suke tafiya a natse a bayan qasa, to da lalle Mun aiko musu mala’ika daga sama a matsayin manzo.”
قُلۡ كَفَىٰ بِٱللَّهِ شَهِيدَۢا بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡۚ إِنَّهُۥ كَانَ بِعِبَادِهِۦ خَبِيرَۢا بَصِيرٗا
Ka ce: “Allah Ya isa shaida tsakanina da ku: Lalle Shi ya zamanto Masani ne ga bayinsa, kuma Mai ganin (abin da suke aikatawa) ne.”
وَمَن يَهۡدِ ٱللَّهُ فَهُوَ ٱلۡمُهۡتَدِۖ وَمَن يُضۡلِلۡ فَلَن تَجِدَ لَهُمۡ أَوۡلِيَآءَ مِن دُونِهِۦۖ وَنَحۡشُرُهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ عَلَىٰ وُجُوهِهِمۡ عُمۡيٗا وَبُكۡمٗا وَصُمّٗاۖ مَّأۡوَىٰهُمۡ جَهَنَّمُۖ كُلَّمَا خَبَتۡ زِدۡنَٰهُمۡ سَعِيرٗا
Wanda kuwa Allah Ya shiryar to shi ne shiryayye; wanda kuwa Ya vatar to ba za ka sami wani mai taimakon su ba in ban da Shi; za kuma Mu tashe su ranar alqiyama a kan fuskokinsu suna makafi, kurame, bebaye; makomarsu Jahannama; duk sanda ta lafa sai Mu qara musu qunarta
ذَٰلِكَ جَزَآؤُهُم بِأَنَّهُمۡ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا وَقَالُوٓاْ أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمٗا وَرُفَٰتًا أَءِنَّا لَمَبۡعُوثُونَ خَلۡقٗا جَدِيدًا
Wannan ne sakamakonsu saboda lalle sun kafirce wa ayoyinmu, suka kuma ce: “Yanzu idan muka zama qasusuwa kuma rududdugaggu, anya kuwa za a tashe mu a sabuwar halitta?”
۞أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ أَنَّ ٱللَّهَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ قَادِرٌ عَلَىٰٓ أَن يَخۡلُقَ مِثۡلَهُمۡ وَجَعَلَ لَهُمۡ أَجَلٗا لَّا رَيۡبَ فِيهِ فَأَبَى ٱلظَّـٰلِمُونَ إِلَّا كُفُورٗا
Yanzu ba sa gani cewa Allah wanda Ya halicci sammai da qasa Mai iko ne a kan Ya halicci irinsu? Ya kuma sanya musu wani lokaci wanda ba kokwanto a cikinsa, sai azzalumai suka qi (yin imani) sai kafircewa
قُل لَّوۡ أَنتُمۡ تَمۡلِكُونَ خَزَآئِنَ رَحۡمَةِ رَبِّيٓ إِذٗا لَّأَمۡسَكۡتُمۡ خَشۡيَةَ ٱلۡإِنفَاقِۚ وَكَانَ ٱلۡإِنسَٰنُ قَتُورٗا
Ka ce da su: “Idan da ku ne kuka mallaki taskokin rahamar Ubangijina to lalle da kun riqe su qam-qam don tsoron ciyarwa. Mutum kuwa ya tabbata mai tsananin rowa ne
وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَىٰ تِسۡعَ ءَايَٰتِۭ بَيِّنَٰتٖۖ فَسۡـَٔلۡ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ إِذۡ جَآءَهُمۡ فَقَالَ لَهُۥ فِرۡعَوۡنُ إِنِّي لَأَظُنُّكَ يَٰمُوسَىٰ مَسۡحُورٗا
Kuma haqiqa Mun bai wa Musa ayoyi tara bayyanannu; to ka tambayi Banu Isra’ila lokacin da ya zo musu, sai Fir’auna ya ce da shi: “Lalle ni fa ina tsammanin kai Musa sihirtacce ne!”
قَالَ لَقَدۡ عَلِمۡتَ مَآ أَنزَلَ هَـٰٓؤُلَآءِ إِلَّا رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ بَصَآئِرَ وَإِنِّي لَأَظُنُّكَ يَٰفِرۡعَوۡنُ مَثۡبُورٗا
(Musa) ya ce: “Haqiqa ka sani ba wanda ya saukar da waxannan (ayoyin) sai Ubangijin sammai da qasa don su zama hujjoji, kuma lalle ina tsammanin kai Fir’auna halakakke ne.”
فَأَرَادَ أَن يَسۡتَفِزَّهُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ فَأَغۡرَقۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ جَمِيعٗا
Sai ya yi nufin ya girgiza su a qasar (ta Masar don ya fitar da su daga ciki), to sai Muka nutsar da shi da duk wanda yake tare da shi gaba xaya
وَقُلۡنَا مِنۢ بَعۡدِهِۦ لِبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱسۡكُنُواْ ٱلۡأَرۡضَ فَإِذَا جَآءَ وَعۡدُ ٱلۡأٓخِرَةِ جِئۡنَا بِكُمۡ لَفِيفٗا
Muka kuma ce da Banu Isra’ila: “Ku zauna a qasar (ta Falasxinu), to idan lokacin alqiyama ya zo za Mu tattaro ku gaba xaya
وَبِٱلۡحَقِّ أَنزَلۡنَٰهُ وَبِٱلۡحَقِّ نَزَلَۗ وَمَآ أَرۡسَلۡنَٰكَ إِلَّا مُبَشِّرٗا وَنَذِيرٗا
Kuma da gaskiya Muka saukar da shi (Alqur’ani), kuma da gaskiya ya sauko. Ba Mu kuma aiko ka ba sai mai yin albishir, mai kuma gargaxi
وَقُرۡءَانٗا فَرَقۡنَٰهُ لِتَقۡرَأَهُۥ عَلَى ٱلنَّاسِ عَلَىٰ مُكۡثٖ وَنَزَّلۡنَٰهُ تَنزِيلٗا
Kuma Mun saukar da Qur’ani, Mun bayyana shi don ka karanta wa mutane shi a sannu a hankali, Mun kuma saukar da shi daki-daki
قُلۡ ءَامِنُواْ بِهِۦٓ أَوۡ لَا تُؤۡمِنُوٓاْۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَ مِن قَبۡلِهِۦٓ إِذَا يُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ يَخِرُّونَۤ لِلۡأَذۡقَانِۤ سُجَّدٗاۤ
Ka ce da su: “Ko ku yi imani da shi ko kada ku yi imani da shi (duk xaya ne).” Lalle waxanda aka bai wa ilimi gabaninsa (Yahudu da Nasara)[1] idan ana karanta musu shi suna faxuwa da fuskokinsu suna masu sujjada
1- Watau mutanen kirki daga cikinsu.
وَيَقُولُونَ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِن كَانَ وَعۡدُ رَبِّنَا لَمَفۡعُولٗا
Suna kuma cewa: “Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu, lalle alqawarin Ubangijinmu tabbas ya zamanto abin aikatawa ne.”
وَيَخِرُّونَ لِلۡأَذۡقَانِ يَبۡكُونَ وَيَزِيدُهُمۡ خُشُوعٗا۩
Suna kuma faxuwa da fuskokinsu suna kuka, Yana kuma qara musu qasqantar da kai
قُلِ ٱدۡعُواْ ٱللَّهَ أَوِ ٱدۡعُواْ ٱلرَّحۡمَٰنَۖ أَيّٗا مَّا تَدۡعُواْ فَلَهُ ٱلۡأَسۡمَآءُ ٱلۡحُسۡنَىٰۚ وَلَا تَجۡهَرۡ بِصَلَاتِكَ وَلَا تُخَافِتۡ بِهَا وَٱبۡتَغِ بَيۡنَ ذَٰلِكَ سَبِيلٗا
Ka ce: “Ku kira (sunan) Allah ko ku kira (sunan) Arrahaman; kowanne kuka kira to shi Yana da sunaye ne mafiya kyau.” Kada kuma ka xaga muryarka da (karatun) sallarka, kada kuma ka yi shi a voye, ka nemi tsaka-tsakin wannan
وَقُلِ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي لَمۡ يَتَّخِذۡ وَلَدٗا وَلَمۡ يَكُن لَّهُۥ شَرِيكٞ فِي ٱلۡمُلۡكِ وَلَمۡ يَكُن لَّهُۥ وَلِيّٞ مِّنَ ٱلذُّلِّۖ وَكَبِّرۡهُ تَكۡبِيرَۢا
Kuma ka ce, “Yabo da godiya sun tabbata ga Allah wanda bai riqi xa ba, kuma ba Shi da wani abokin tarayya a cikin mulki, kuma ba Shi da wani mataimaki don kare masa qasqanci.” Kuma ka girmama shi girmamawa ta sosai
ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ عَلَىٰ عَبۡدِهِ ٱلۡكِتَٰبَ وَلَمۡ يَجۡعَل لَّهُۥ عِوَجَاۜ
Dukkan yabo ya tabbata ga Allah wanda Ya saukar wa da Bawansa Littafi, bai kuma sanya masa wata karkata ba
قَيِّمٗا لِّيُنذِرَ بَأۡسٗا شَدِيدٗا مِّن لَّدُنۡهُ وَيُبَشِّرَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ ٱلَّذِينَ يَعۡمَلُونَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أَنَّ لَهُمۡ أَجۡرًا حَسَنٗا
Daidaitacce ne, don ya yi gargaxi game da azaba mai tsanani daga gare Shi (wato Allah), ya kuma yi wa muminai waxanda suke aiki nagari albishir cewa suna da lada kyakkyawa
مَّـٰكِثِينَ فِيهِ أَبَدٗا
Madawwama a cikinsa har abada
وَيُنذِرَ ٱلَّذِينَ قَالُواْ ٱتَّخَذَ ٱللَّهُ وَلَدٗا
Ya kuma gargaxi waxanda suka ce Allah Yana da xa
مَّا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٖ وَلَا لِأٓبَآئِهِمۡۚ كَبُرَتۡ كَلِمَةٗ تَخۡرُجُ مِنۡ أَفۡوَٰهِهِمۡۚ إِن يَقُولُونَ إِلَّا كَذِبٗا
Ba su da wani ilimi game da shi (wannan zance) kuma iyayensu ma ba su da (ilimi game da shi). Kalmar da take fitowa daga bakunansu ta yi girma. Ba abin da suke faxa sai qarya
فَلَعَلَّكَ بَٰخِعٞ نَّفۡسَكَ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمۡ إِن لَّمۡ يُؤۡمِنُواْ بِهَٰذَا ٱلۡحَدِيثِ أَسَفًا
To ko mai yiwuwa ne za ka kashe kanka da baqin ciki, in ba su yi imani da wannan zancen ba (watau Alqur’ani)
إِنَّا جَعَلۡنَا مَا عَلَى ٱلۡأَرۡضِ زِينَةٗ لَّهَا لِنَبۡلُوَهُمۡ أَيُّهُمۡ أَحۡسَنُ عَمَلٗا
Lalle Mu Mun sanya abin da yake bayan qasa ya zama ado a gare ta, don (kuma) Mu jarraba su, wane ne daga cikinsu ya fi kyakkyawan aiki?
وَإِنَّا لَجَٰعِلُونَ مَا عَلَيۡهَا صَعِيدٗا جُرُزًا
Lalle kuma Mu za Mu mai da abin da yake kanta (ya zama) turvaya qeqasasshiya
أَمۡ حَسِبۡتَ أَنَّ أَصۡحَٰبَ ٱلۡكَهۡفِ وَٱلرَّقِيمِ كَانُواْ مِنۡ ءَايَٰتِنَا عَجَبًا
Shin ka yi tsammanin cewa lalle Mutanen Kogo da Raqimu[1] sun kasance daga ayoyinmu masu ban mamaki?
1- An yi savani wajen fassara ma’anar arraqimu. Wasu sun ce sunan dutsen da suka kasance a cikinsa ne; wasu kuma sun ce sunan allon da aka rubuta sunayensu a ciki; wasu kuma sun ce mutanen nan uku ne da suka shiga kogo dutse ya rufe da su.