Sourate: Suratul Alaq

Verset : 17

فَلۡيَدۡعُ نَادِيَهُۥ

To ya kirawo majalisar tasa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 18

سَنَدۡعُ ٱلزَّبَانِيَةَ

Mu kuma lalle za Mu kirawo (mala’iku) zabaniyawa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 19

كَلَّا لَا تُطِعۡهُ وَٱسۡجُدۡۤ وَٱقۡتَرِب۩

Faufau! Kada ka bi shi, ka kuma yi salla, ka kusanta (ga Allah)



Sourate: Qadar

Verset : 1

إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ فِي لَيۡلَةِ ٱلۡقَدۡرِ

Lalle Mu Muka saukar da shi (Alqur’ani) a daren Lailatul-Qadari[1] (dare mai daraja)


1- Watau lokacin da aka fara saukar da jumullarsa a sama ta kusa, kamar yadda a cikin watan Ramadana ne ake fara saukar da shi ga Manzon Allah () a kogon Hira.


Sourate: Qadar

Verset : 2

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا لَيۡلَةُ ٱلۡقَدۡرِ

Mene ne ya sanar da kai mece ce Lailatul-Qadari?



Sourate: Qadar

Verset : 3

لَيۡلَةُ ٱلۡقَدۡرِ خَيۡرٞ مِّنۡ أَلۡفِ شَهۡرٖ

(Daren) Lailatul-Qadari ya fi wata dubu alheri



Sourate: Qadar

Verset : 4

تَنَزَّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ فِيهَا بِإِذۡنِ رَبِّهِم مِّن كُلِّ أَمۡرٖ

Mala’iku da Jibrilu suna ta saukowa da dukkanin al’amura a cikinsa da izinin Ubangijinsu



Sourate: Qadar

Verset : 5

سَلَٰمٌ هِيَ حَتَّىٰ مَطۡلَعِ ٱلۡفَجۡرِ

Aminci ne shi (daren dukkansa) har zuwa hudowar alfijir



Sourate: Suratul Bayyina

Verset : 1

لَمۡ يَكُنِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ مُنفَكِّينَ حَتَّىٰ تَأۡتِيَهُمُ ٱلۡبَيِّنَةُ

Waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushirikai ba su zamanto masu barin abin da suke kai (na kafirci) ba har sai hujja bayyananniya ta zo musu



Sourate: Suratul Bayyina

Verset : 2

رَسُولٞ مِّنَ ٱللَّهِ يَتۡلُواْ صُحُفٗا مُّطَهَّرَةٗ

(Watau) Manzo daga Allah da zai riqa karanta (musu) takardu masu tsarki



Sourate: Suratul Bayyina

Verset : 3

فِيهَا كُتُبٞ قَيِّمَةٞ

(Waxanda) a cikinsu akwai hukunce-hukunce masu qima



Sourate: Suratul Bayyina

Verset : 4

وَمَا تَفَرَّقَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ مَا جَآءَتۡهُمُ ٱلۡبَيِّنَةُ

Waxanda kuma aka bai wa littafi ba su rarraba ba[1] sai bayan da hujja bayyananniya ta zo musu


1- Watau Yahudawa da Nasara ba su rarrabu ba suka zama qungiya-qungiya wasu suka yi imani da Manzo Allah (), wasu kuma suka kafirce.


Sourate: Suratul Bayyina

Verset : 5

وَمَآ أُمِرُوٓاْ إِلَّا لِيَعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مُخۡلِصِينَ لَهُ ٱلدِّينَ حُنَفَآءَ وَيُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُؤۡتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَذَٰلِكَ دِينُ ٱلۡقَيِّمَةِ

Ba a kuma umarce su ba sai don su bauta wa Allah suna masu tsantsanta addini gare Shi, suna masu kauce wa varna, suna kuma tsayar da salla, kuma suna ba da zakka. Wannan kuwa shi ne addinin miqaqqiyar hanya



Sourate: Suratul Bayyina

Verset : 6

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَٱلۡمُشۡرِكِينَ فِي نَارِ جَهَنَّمَ خَٰلِدِينَ فِيهَآۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ شَرُّ ٱلۡبَرِيَّةِ

Lalle waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushirikai suna cikin wutar Jahannama suna madawwama a cikinta. Waxannan su ne mafiya sharrin halitta



Sourate: Suratul Bayyina

Verset : 7

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمۡ خَيۡرُ ٱلۡبَرِيَّةِ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, waxannan su ne mafiya alherin halitta



Sourate: Suratul Bayyina

Verset : 8

جَزَآؤُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَآ أَبَدٗاۖ رَّضِيَ ٱللَّهُ عَنۡهُمۡ وَرَضُواْ عَنۡهُۚ ذَٰلِكَ لِمَنۡ خَشِيَ رَبَّهُۥ

Sakamakonsu a wajen Ubangijinsu gidajen Aljanna ne na dawwama waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu suna madawwama a cikinsu har abada; Allah Ya yarda da su, su ma sun yarda da Shi. Wannan kuma (sakamako ne) ga wanda ya ji tsoron Ubangijinsa



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 1

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 2

وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا

Qasar kuma ta fitar da nauyaye-nauyayenta[1]


1- Watau ta fitar da mutanen da ke cikinta da sauran ma’adanan qarqashinta.


Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 3

وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا

Mutum kuma ya ce: “Me ya same ta?”



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 4

يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا

A wannan ranar ne za ta ba da labaranta[1]


1- Watau ayyukan da aka yi a kanta masu kyau da munana.


Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 5

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا

Don Ubangijinka Ya umarce ta (da yin haka)



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 6

يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ

A wannan ranar mutane za su fito a warwatse, don a nuna musu ayyukansu



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 7

فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ

To duk wanda ya yi aikin alheri daidai da zarra zai gan shi



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 8

وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ

Wanda kuma duk ya yi aikin sharri daidai da zarra zai gan shi



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 1

وَٱلۡعَٰدِيَٰتِ ضَبۡحٗا

Na rantse da (dawaki) masu sukuwa suna kukan ciki



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 2

فَٱلۡمُورِيَٰتِ قَدۡحٗا

Sannan masu bugun qyastu da kofatai[1]


1- Watau suna qyasta wuta da kofatansu idan suka daki duwatsu da su.


Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 3

فَٱلۡمُغِيرَٰتِ صُبۡحٗا

Sannan masu kai hari da asuba



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 4

فَأَثَرۡنَ بِهِۦ نَقۡعٗا

Sai suka tayar da qura da ita (sukawar tasu)



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 5

فَوَسَطۡنَ بِهِۦ جَمۡعًا

Sai kuma suka shiga tsakiyar taro (da mahayansu)



Sourate: Suratul Adiyat

Verset : 6

إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لِرَبِّهِۦ لَكَنُودٞ

Lalle mutum tabbas mai yawan butulci ne ga Ubangijinsa