ٱلَّذِيٓ أَنقَضَ ظَهۡرَكَ
Wanda ya nauyayi bayanka?
Partager :
وَرَفَعۡنَا لَكَ ذِكۡرَكَ
Muka kuma xaukaka maka ambatonka[1]?
1- Watau kamar ambatonsa a cikin kiran salla da iqama da tahiya da sauransu.
فَإِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرًا
To lalle tsanani yana tare da sauqi
إِنَّ مَعَ ٱلۡعُسۡرِ يُسۡرٗا
Lalle tsananin yana tare da sauqi
فَإِذَا فَرَغۡتَ فَٱنصَبۡ
Saboda haka idan ka gama (harkokinka) sai ka kafu (wajen bautar Allah)
وَإِلَىٰ رَبِّكَ فَٱرۡغَب
Sannan kuma ka yi kwaxayi wajen Ubangijinka kawai
وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيۡتُونِ
Na rantse da vaure da zaitun[1]
1- Watau wuraren tsirowarsu, watau Sham, ko kuma su kansu waxanan bishiyoyin.
وَطُورِ سِينِينَ
Da (dutsen) Xuri Sinina
وَهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِينِ
Da wannan garin amintacce (watau Makka)
لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ
Haqiqa Mun halicci mutum a kan mafi kyan diri
ثُمَّ رَدَدۡنَٰهُ أَسۡفَلَ سَٰفِلِينَ
Sannan Muka mayar da shi mafi qasqancin qasqantattu[1]
1- Watau ya mayar da shi tsoho tukuf a duniya, ko kuma a lahira ya zamanto xan wuta.
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ
Sai fa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, to su kam suna da lada ba mai yankewa ba
فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّينِ
To (kai kafiri) me ya sa kake qaryata ranar sakamako bayan haka?
أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَحۡكَمِ ٱلۡحَٰكِمِينَ
Ashe Allah ba Shi ne Mafi iya hukuncin masu hukunci ba?
ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta
خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ
Ya halicci mutum daga gudan jini[1]
1- Watau bayan yana xigon maniyyi.
ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ
Ka yi karatu alhali Ubangijinka Shi ne mafi karamci
ٱلَّذِي عَلَّمَ بِٱلۡقَلَمِ
Wanda Ya koyar ta (hanyar) alqalami
عَلَّمَ ٱلۡإِنسَٰنَ مَا لَمۡ يَعۡلَمۡ
Ya koyar da mutum abin da bai sani ba
كَلَّآ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَيَطۡغَىٰٓ
Tabbas! Lalle (jinsin) mutum haqiqa yana yin xagawa
أَن رَّءَاهُ ٱسۡتَغۡنَىٰٓ
Don ya ga kansa yana cikin wadata
إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰٓ
Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makomar (taka) take
أَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي يَنۡهَىٰ
Ka ba ni labarin wanda yake hana
عَبۡدًا إِذَا صَلَّىٰٓ
Bawa yayin da ya yi salla
أَرَءَيۡتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلۡهُدَىٰٓ
Ka ba ni labari idan (shi Bawan) ya kasance a kan shiriya
أَوۡ أَمَرَ بِٱلتَّقۡوَىٰٓ
Ko kuma ya yi umarni da taqawa
أَرَءَيۡتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ
Ka ba ni labari idan (shi mai hanawar) ya qaryata ya kuma ba da baya
أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ
Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?
كَلَّا لَئِن لَّمۡ يَنتَهِ لَنَسۡفَعَۢا بِٱلنَّاصِيَةِ
A’aha! Tabbas idan bai hanu ba to za Mu ja shi ta makwarkwaxar kai
نَاصِيَةٖ كَٰذِبَةٍ خَاطِئَةٖ
Makwarkwaxar kai mai qaryatawa, mai aikata laifi