Sourate: Suratul Balad

Verset : 10

وَهَدَيۡنَٰهُ ٱلنَّجۡدَيۡنِ

Muka kuma bayyana masa hanyoyi biyu[1]?


1- Watau hanyar alheri da hanyar sharri.


Sourate: Suratul Balad

Verset : 11

فَلَا ٱقۡتَحَمَ ٱلۡعَقَبَةَ

Sai bai qetare hanya mai wahala[1] ba?


1- Watau hanyar da ta raba tsakaninsa da gidan Aljanna.


Sourate: Suratul Balad

Verset : 12

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡعَقَبَةُ

Me kuma ya sanar da kai mece ce hanya mai wahala?



Sourate: Suratul Balad

Verset : 13

فَكُّ رَقَبَةٍ

(Watau) ‘yanta wuyaye (bawa ko baiwa)



Sourate: Suratul Balad

Verset : 14

أَوۡ إِطۡعَٰمٞ فِي يَوۡمٖ ذِي مَسۡغَبَةٖ

Ko kuma ciyarwa a wata rana ta yunwa



Sourate: Suratul Balad

Verset : 15

يَتِيمٗا ذَا مَقۡرَبَةٍ

Ga maraya ma’abocin kusanci



Sourate: Suratul Balad

Verset : 16

أَوۡ مِسۡكِينٗا ذَا مَتۡرَبَةٖ

Ko miskini ma’abocin talauci



Sourate: Suratul Balad

Verset : 17

ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ

Sannan kuma ya zama daga waxanda suka yi imani, suka yi wa junansu wasiyya da yin haquri kuma suka yi wa juna wasiyya da tausayawa



Sourate: Suratul Balad

Verset : 18

أُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ

Waxannan su ne ma’abota dama[1]


1- Watau ‘yan Aljanna.


Sourate: Suratul Balad

Verset : 19

وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ

Waxanda kuwa suka kafirce wa ayoyinmu, su ne ma’abota hagu[1]


1- Watau ‘yan wuta.


Sourate: Suratul Balad

Verset : 20

عَلَيۡهِمۡ نَارٞ مُّؤۡصَدَةُۢ

A kansu akwai wuta abar kullewa



Sourate: Suratus Shams

Verset : 1

وَٱلشَّمۡسِ وَضُحَىٰهَا

Na rantse da rana da walaharta



Sourate: Suratus Shams

Verset : 2

وَٱلۡقَمَرِ إِذَا تَلَىٰهَا

Da kuma wata idan ya bi ta (wato ranar)[1]


1- Watau ya biyo bayan faxuwar rana.


Sourate: Suratus Shams

Verset : 3

وَٱلنَّهَارِ إِذَا جَلَّىٰهَا

Da kuma wuni idan ya bayyana ta



Sourate: Suratus Shams

Verset : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰهَا

Da kuma dare idan ya lulluve ta



Sourate: Suratus Shams

Verset : 5

وَٱلسَّمَآءِ وَمَا بَنَىٰهَا

Da kuma sama da gininta



Sourate: Suratus Shams

Verset : 6

وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا طَحَىٰهَا

Da kuma qasa da shimfixarta



Sourate: Suratus Shams

Verset : 7

وَنَفۡسٖ وَمَا سَوَّىٰهَا

Da kuma rai da daidaitarsa



Sourate: Suratus Shams

Verset : 8

فَأَلۡهَمَهَا فُجُورَهَا وَتَقۡوَىٰهَا

Sai Ya kimsa masa (gane) lalacewarsa da taqawarsa



Sourate: Suratus Shams

Verset : 9

قَدۡ أَفۡلَحَ مَن زَكَّىٰهَا

Haqiqa wanda ya tsarkake shi (ran) ya rabauta



Sourate: Suratus Shams

Verset : 10

وَقَدۡ خَابَ مَن دَسَّىٰهَا

Haqiqa kuma wanda ya binne shi da savo ya tave



Sourate: Suratus Shams

Verset : 11

كَذَّبَتۡ ثَمُودُ بِطَغۡوَىٰهَآ

Samudawa sun qaryata saboda xagawarsu



Sourate: Suratus Shams

Verset : 12

إِذِ ٱنۢبَعَثَ أَشۡقَىٰهَا

Yayin da mafi tsagerancinsu ya zabura



Sourate: Suratus Shams

Verset : 13

فَقَالَ لَهُمۡ رَسُولُ ٱللَّهِ نَاقَةَ ٱللَّهِ وَسُقۡيَٰهَا

Sai Manzon Allah[1] ya ce da su: “Ku bar taguwar Allah da (ranar) shanta.”


1- Watau Annabi Salihu ().


Sourate: Suratus Shams

Verset : 14

فَكَذَّبُوهُ فَعَقَرُوهَا فَدَمۡدَمَ عَلَيۡهِمۡ رَبُّهُم بِذَنۢبِهِمۡ فَسَوَّىٰهَا

Sai suka qaryata shi sannan suka soke ta, sai Ubangijinsu Ya kama su da azaba saboda zunubinsu, sai Ya daidaita ta (watau qabilar wajen azaba)



Sourate: Suratus Shams

Verset : 15

وَلَا يَخَافُ عُقۡبَٰهَا

Kuma ba Ya tsoron abin da zai biyo bayanta[1]


1- Watau ba ya jin tsoron wani abu da hallaka su za ta haifar nan gaba.


Sourate: Suratul Lail

Verset : 1

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَغۡشَىٰ

Na rantse da dare idan ya lulluve (da duhunsa)



Sourate: Suratul Lail

Verset : 2

وَٱلنَّهَارِ إِذَا تَجَلَّىٰ

Da kuma wuni idan ya bayyana



Sourate: Suratul Lail

Verset : 3

وَمَا خَلَقَ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ

Da kuma halittar namiji da mace



Sourate: Suratul Lail

Verset : 4

إِنَّ سَعۡيَكُمۡ لَشَتَّىٰ

Lalle aikinku ya sha bamban