Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 21

وَتَذَرُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ

Kuna kuma barin lahira



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 22

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ نَّاضِرَةٌ

Wasu fuskokin a wannan rana a ni’imce suke



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 23

إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٞ

Suna masu kallon Ubangijinsu



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 24

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذِۭ بَاسِرَةٞ

Wasu fuskokin kuma a wannan rana a xaxxaure suke



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 25

تَظُنُّ أَن يُفۡعَلَ بِهَا فَاقِرَةٞ

Suna tabbatar da cewa, za a saukar musu da wani bala’i



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 26

كَلَّآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلتَّرَاقِيَ

Ku saurara, yayin da rai ya iso a karankarama[1]


1- Watau ya zo qasusuwan qirji a lokacin gargarar mutuwa.


Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 27

وَقِيلَ مَنۡۜ رَاقٖ

Aka kuma ce: “Wane ne mai tawaida[1]?”


1- Watau masu jinya su riqa tambayar junansu cewa, wane ne zai yi masa ruqya ko zai zamu sauqi?


Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 28

وَظَنَّ أَنَّهُ ٱلۡفِرَاقُ

Ya kuma tabbata cewar (wannan) shi ne rabuwarsa (da duniya)



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 29

وَٱلۡتَفَّتِ ٱلسَّاقُ بِٱلسَّاقِ

Kuma tsananin bala’i ya haxu



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 30

إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمَسَاقُ

To zuwa Ubangijinka ne (za a) kora ka a wannan ranar



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 31

فَلَا صَدَّقَ وَلَا صَلَّىٰ

To bai ba da gaskiya ba bai kuma yi salla ba



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 32

وَلَٰكِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ

Sai dai ya qaryata ya kuma ba da baya



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 33

ثُمَّ ذَهَبَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ يَتَمَطَّىٰٓ

Sannan ya tafi zuwa ga iyalinsa yana taqama



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 34

أَوۡلَىٰ لَكَ فَأَوۡلَىٰ

(Azaba) ta doso ka, ta fa doso ka!



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 35

ثُمَّ أَوۡلَىٰ لَكَ فَأَوۡلَىٰٓ

Sannan ta doso ka, ta fa doso ka!



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 36

أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَن يُتۡرَكَ سُدًى

Yanzu mutum yana tsammanin za a bar shi haka sasaka[1]?


1- Watau za a qyale shi ya yi abin da ya ga dama ba tare da umarni ko hani ba?


Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 37

أَلَمۡ يَكُ نُطۡفَةٗ مِّن مَّنِيّٖ يُمۡنَىٰ

Shin bai kasance wani xigo na maniyyi da ake zuba shi (a mahaifa) ba?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 38

ثُمَّ كَانَ عَلَقَةٗ فَخَلَقَ فَسَوَّىٰ

Sannan ya zama gudan jini sannan (Allah) Ya halicce (shi) sai Ya daidaita (shi)?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 39

فَجَعَلَ مِنۡهُ ٱلزَّوۡجَيۡنِ ٱلذَّكَرَ وَٱلۡأُنثَىٰٓ

Sannan Ya halicci dangi biyu daga gare shi, namiji da mace?



Sourate: Suratul Qiyama

Verset : 40

أَلَيۡسَ ذَٰلِكَ بِقَٰدِرٍ عَلَىٰٓ أَن يُحۡـِۧيَ ٱلۡمَوۡتَىٰ

Yanzu wannan bai zama Mai iko a kan ya raya matattu ba?



Sourate: Suratul Insan

Verset : 1

هَلۡ أَتَىٰ عَلَى ٱلۡإِنسَٰنِ حِينٞ مِّنَ ٱلدَّهۡرِ لَمۡ يَكُن شَيۡـٔٗا مَّذۡكُورًا

Haqiqa wani yanki na zamani ya zo wa mutum yayin da bai zama wani abin ambato ba[1]


1- Watau babu shi gaba xaya, babu kuma wanda ya san shi.


Sourate: Suratul Insan

Verset : 2

إِنَّا خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِن نُّطۡفَةٍ أَمۡشَاجٖ نَّبۡتَلِيهِ فَجَعَلۡنَٰهُ سَمِيعَۢا بَصِيرًا

Lalle Mun halicci mutum daga maniyyi gamin-gambiza[1] don Mu jarrabe shi, sai Muka sanya shi mai ji mai gani


1- Watau tsakanin na namiji da na mace.


Sourate: Suratul Insan

Verset : 3

إِنَّا هَدَيۡنَٰهُ ٱلسَّبِيلَ إِمَّا شَاكِرٗا وَإِمَّا كَفُورًا

Lalle Mun bayyana masa hanya, ko dai (ya zama) mai godewa ko kuma mai butulcewa



Sourate: Suratul Insan

Verset : 4

إِنَّآ أَعۡتَدۡنَا لِلۡكَٰفِرِينَ سَلَٰسِلَاْ وَأَغۡلَٰلٗا وَسَعِيرًا

Lalle Mun tanadar wa kafirai sarqoqi da ququmai da wutar Sa’ira



Sourate: Suratul Insan

Verset : 5

إِنَّ ٱلۡأَبۡرَارَ يَشۡرَبُونَ مِن كَأۡسٖ كَانَ مِزَاجُهَا كَافُورًا

Lalle mutane nagari suna sha daga wani kofin (giya) da mahaxinta ya kasance kafur ne[1]


1- Watau mai daxin qamshi.


Sourate: Suratul Insan

Verset : 6

عَيۡنٗا يَشۡرَبُ بِهَا عِبَادُ ٱللَّهِ يُفَجِّرُونَهَا تَفۡجِيرٗا

Wani marmaro ne da bayin Allah suke sha daga gare shi suna vuvvugo shi vuvvugowa ta haqiqa



Sourate: Suratul Insan

Verset : 7

يُوفُونَ بِٱلنَّذۡرِ وَيَخَافُونَ يَوۡمٗا كَانَ شَرُّهُۥ مُسۡتَطِيرٗا

Suna cika alqawari na bakance suna kuma tsoron ranar da sharrinta ya kasance mai bazuwa ne



Sourate: Suratul Insan

Verset : 8

وَيُطۡعِمُونَ ٱلطَّعَامَ عَلَىٰ حُبِّهِۦ مِسۡكِينٗا وَيَتِيمٗا وَأَسِيرًا

Suna kuma ciyar da abinci tare da suna son sa ga miskini da maraya da kuma ribataccen yaqi



Sourate: Suratul Insan

Verset : 9

إِنَّمَا نُطۡعِمُكُمۡ لِوَجۡهِ ٱللَّهِ لَا نُرِيدُ مِنكُمۡ جَزَآءٗ وَلَا شُكُورًا

(Suna cewa): “Mu kawai muna ciyar da ku ne saboda Allah, ba ma nufin sakamako ko godiya daga wurinka



Sourate: Suratul Insan

Verset : 10

إِنَّا نَخَافُ مِن رَّبِّنَا يَوۡمًا عَبُوسٗا قَمۡطَرِيرٗا

“Lalle mu muna jin tsoron rana mai sa xaure fuska, matsananciya daga Ubangijinmu