حَتَّىٰٓ أَتَىٰنَا ٱلۡيَقِينُ
“Har mutuwa ta zo mana.”
Partager :
فَمَا تَنفَعُهُمۡ شَفَٰعَةُ ٱلشَّـٰفِعِينَ
Saboda haka ceton masu ceto ba zai amfane su ba
فَمَا لَهُمۡ عَنِ ٱلتَّذۡكِرَةِ مُعۡرِضِينَ
To me ya same su ne suke bijire wa wa’azi?
كَأَنَّهُمۡ حُمُرٞ مُّسۡتَنفِرَةٞ
Kai ka ce su jakunan jeji ne da aka firgitar
فَرَّتۡ مِن قَسۡوَرَةِۭ
Da suka guje wa zaki
بَلۡ يُرِيدُ كُلُّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ أَن يُؤۡتَىٰ صُحُفٗا مُّنَشَّرَةٗ
A’a, kowane mutum daga cikinsu yana so ne a ba shi takardu buxaxxu[1] (kafin su bi Annabi)
1- Watau a ba shi buxaxxen littafi wanda zai ba shi labari cewa Annabi Muhammadu () Manzon Allah ne.
كَلَّاۖ بَل لَّا يَخَافُونَ ٱلۡأٓخِرَةَ
Faufau! A’a, su dai ba sa tsoron ranar lahira ne
كَلَّآ إِنَّهُۥ تَذۡكِرَةٞ
Tabbas, lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne
فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ
To duk wanda ya ga dama sai ya wa’azantu
وَمَا يَذۡكُرُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ هُوَ أَهۡلُ ٱلتَّقۡوَىٰ وَأَهۡلُ ٱلۡمَغۡفِرَةِ
Ba sa kuma wa’azantuwa sai idan Allah Ya ga dama. Shi ne Ya cancanci taqawa, kuma Shi ne Ya cancanci yin gafara
لَآ أُقۡسِمُ بِيَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ
Ina rantsuwa da ranar alqiyama
وَلَآ أُقۡسِمُ بِٱلنَّفۡسِ ٱللَّوَّامَةِ
Ina kuma rantsuwa da rai mai yawan zargin (kansa)[1]
1- Watau a kan gazawarsa wajen ayyukan alheri ko a kan aikata laifuka.
أَيَحۡسَبُ ٱلۡإِنسَٰنُ أَلَّن نَّجۡمَعَ عِظَامَهُۥ
Yanzu mutum yana tsammanin ba za Mu tattara qasusuwansa ba?
بَلَىٰ قَٰدِرِينَ عَلَىٰٓ أَن نُّسَوِّيَ بَنَانَهُۥ
E, (Mu) Masu iko ne a kan Mu daidaita gavovin yatsunsa
بَلۡ يُرِيدُ ٱلۡإِنسَٰنُ لِيَفۡجُرَ أَمَامَهُۥ
Ba haka ba ne, mutum yana nufi ne kawai ya gurvata gabansa (da savon Allah)
يَسۡـَٔلُ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلۡقِيَٰمَةِ
Yana tambaya yaushe ne ranar alqiyamar?
فَإِذَا بَرِقَ ٱلۡبَصَرُ
To lokacin da gani ya ruxe
وَخَسَفَ ٱلۡقَمَرُ
Wata kuma ya yi duhu
وَجُمِعَ ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ
Aka kuma haxe rana da wata (a mafitarsu)
يَقُولُ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذٍ أَيۡنَ ٱلۡمَفَرُّ
A wannan rana ne mutum zai ce: “Ina wurin gudu?”
كَلَّا لَا وَزَرَ
Faufau, babu mafaka
إِلَىٰ رَبِّكَ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡمُسۡتَقَرُّ
Zuwa ga Ubangijinka ne kawai matabbata take a wannan rana
يُنَبَّؤُاْ ٱلۡإِنسَٰنُ يَوۡمَئِذِۭ بِمَا قَدَّمَ وَأَخَّرَ
Za a bai wa mutum labari a wannan rana na abin da ya gabatar da kuma (abin da) ya jinkirtar (na ayyukansa)
بَلِ ٱلۡإِنسَٰنُ عَلَىٰ نَفۡسِهِۦ بَصِيرَةٞ
A’a, shi dai mutum mai shaida ne a kan kansa
وَلَوۡ أَلۡقَىٰ مَعَاذِيرَهُۥ
Ko da kuwa ya kawo uzururrukansa
لَا تُحَرِّكۡ بِهِۦ لِسَانَكَ لِتَعۡجَلَ بِهِۦٓ
(Allah ya ce da Annabinsa): Kada ka motsa harshenka da shi (Alqur’ani) don gaggauta (karanta) shi
إِنَّ عَلَيۡنَا جَمۡعَهُۥ وَقُرۡءَانَهُۥ
Lalle tattara shi (a zuciyarka) da karanta shi yana kanmu
فَإِذَا قَرَأۡنَٰهُ فَٱتَّبِعۡ قُرۡءَانَهُۥ
Saboda haka idan Muka karanta (maka) shi sai ka bi karatunsa
ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا بَيَانَهُۥ
Sannan kuma bayaninsa yana kanmu
كَلَّا بَلۡ تُحِبُّونَ ٱلۡعَاجِلَةَ
Haba, ku dai kawai kuna son duniya ne