Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 17

سَأُرۡهِقُهُۥ صَعُودًا

Ba da daxewa ba zan xora masa (azaba) mai matsananciyar wahala



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 18

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ

Lalle shi ya yi tunani, ya kuma auna (a ransa)



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 19

فَقُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sai aka la’ane shi, yaya ya yi irin wannan awon?



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 20

ثُمَّ قُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sannan aka kuma la’antar sa, yaya ya yi wannan awon?



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 21

ثُمَّ نَظَرَ

Sannan ya yi nazari



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 22

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ

Sannan ya xaure fuska, ya kuma murtuke



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 23

ثُمَّ أَدۡبَرَ وَٱسۡتَكۡبَرَ

Sannan ya ba da baya (daga imani) ya kuma yi girman kai



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 24

فَقَالَ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ يُؤۡثَرُ

Sai ya ce: “Wannan (Alqur’ani) ba komai ba ne sai sihiri da aka samo (daga wasu)



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 25

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا قَوۡلُ ٱلۡبَشَرِ

“Wannan ba komai ba ne sai magana irin ta mutane.”



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 26

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ

(Allah ya ce): Da sannu zan shigar da shi (wutar) Saqara



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 27

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Me ya sanar da kai abin da ake ce wa Saqara?



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 28

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ

Ba ta ragewa kuma ba ta barin (komai)



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 29

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ

Mai xaxxaye fata ce



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 30

عَلَيۡهَا تِسۡعَةَ عَشَرَ

Akwai (mala’iku) goma sha tara suna tsaron ta



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 31

وَمَا جَعَلۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلنَّارِ إِلَّا مَلَـٰٓئِكَةٗۖ وَمَا جَعَلۡنَا عِدَّتَهُمۡ إِلَّا فِتۡنَةٗ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ لِيَسۡتَيۡقِنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَيَزۡدَادَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِيمَٰنٗا وَلَا يَرۡتَابَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ وَٱلۡمُؤۡمِنُونَ وَلِيَقُولَ ٱلَّذِينَ فِي قُلُوبِهِم مَّرَضٞ وَٱلۡكَٰفِرُونَ مَاذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِهَٰذَا مَثَلٗاۚ كَذَٰلِكَ يُضِلُّ ٱللَّهُ مَن يَشَآءُ وَيَهۡدِي مَن يَشَآءُۚ وَمَا يَعۡلَمُ جُنُودَ رَبِّكَ إِلَّا هُوَۚ وَمَا هِيَ إِلَّا ذِكۡرَىٰ لِلۡبَشَرِ

Ba Mu kuwa sanya masu tsaron wutar ba sai mala’iku, ba Mu kuma sanya adadinsu ba sai don fitina ga waxanda suka kafirta, don kuma waxanda aka bai wa littafi su sami yaqini, waxanda kuma suka yi imani su qara imani, waxanda aka bai wa littafi da muminai kuma kada su yi tababa, don kuma waxanda suke da raunin imani a zukatansu da kuma kafirai su ce: “Me Allah Yake nufi da yin misali da wannan (adadin)?” Kamar haka Allah Yake vatar da wanda Ya ga dama, Yake kuma shiryar da wanda Ya ga dama. Ba kuma wanda ya san (yawan) rundunar Ubangijinka sai Shi. Ita (Saqara) kuma ba wata abu ba ce face wa’azi ga mutane



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 32

كَلَّا وَٱلۡقَمَرِ

A’a. Na rantse da wata



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 33

وَٱلَّيۡلِ إِذۡ أَدۡبَرَ

Da kuma dare idan ya ba da baya



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 34

وَٱلصُّبۡحِ إِذَآ أَسۡفَرَ

Da kuma asuba idan ta bayyana (da haskenta)



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 35

إِنَّهَا لَإِحۡدَى ٱلۡكُبَرِ

Lalle ita (Saqara) tana xaya daga manya-manyan (bala’o’i)



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 36

نَذِيرٗا لِّلۡبَشَرِ

Gargaxi ce ga mutane



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 37

لِمَن شَآءَ مِنكُمۡ أَن يَتَقَدَّمَ أَوۡ يَتَأَخَّرَ

Ga wanda ya ga dama daga cikinku, ya ci gaba ko ya ci baya



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 38

كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا كَسَبَتۡ رَهِينَةٌ

Kowane rai jingina ne ga abin da ya tsuwurwurta[1]


1- Watau jingina ne ga ayyukansu, ko dai su hallakar da shi ko su kuvutar da shi, su ‘yanta shi.


Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 39

إِلَّآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡيَمِينِ

Sai dai ga ma’abota dama[1]


1- Watau waxanda za su karvi littattafan ayyukansu ta hannayensu na dama.


Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 40

فِي جَنَّـٰتٖ يَتَسَآءَلُونَ

(Su kam suna) cikin gidajen Aljanna suna tambayar juna



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 41

عَنِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Game da manyan masu laifuka



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 42

مَا سَلَكَكُمۡ فِي سَقَرَ

(Suna cewa): “Me ya shigar da ku cikin Saqara?”



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 43

قَالُواْ لَمۡ نَكُ مِنَ ٱلۡمُصَلِّينَ

Suka ce: “Ba mu zama daga cikin masallata ba



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 44

وَلَمۡ نَكُ نُطۡعِمُ ٱلۡمِسۡكِينَ

“Kuma ba mu kasance muna ciyar da miskini ba



Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 45

وَكُنَّا نَخُوضُ مَعَ ٱلۡخَآئِضِينَ

“Mun kuma kasance muna kutsawa (cikin varna)[1] tare da masu kutsawa


1- Watau suna faxar qarerayi game da Annabi () da Alqur’ani.


Sourate: Suratul Muddassir

Verset : 46

وَكُنَّا نُكَذِّبُ بِيَوۡمِ ٱلدِّينِ

“Kuma mun kasance muna qaryata ranar sakamako