Sourate: Suratul Fil

Verset : 1

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِأَصۡحَٰبِ ٱلۡفِيلِ

Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya yi wa ma’abota giwa[1] ba?


1- Watau runduna ce ta mayaqa daga qasar Yaman qarqashin jagorancin Abrahata, suka nufo Makka da niyyar rushe Xakin Ka’aba. A tare da su akwai wata babbar giwa. Allah ya hallaka su baki xaya..


Sourate: Suratul Fil

Verset : 2

أَلَمۡ يَجۡعَلۡ كَيۡدَهُمۡ فِي تَضۡلِيلٖ

Ashe bai mayar da makircinsu cikin watsewa ba?



Sourate: Suratul Fil

Verset : 3

وَأَرۡسَلَ عَلَيۡهِمۡ طَيۡرًا أَبَابِيلَ

Ya kuma aiko musu da tsuntsaye dodo-dodo?



Sourate: Suratul Fil

Verset : 4

تَرۡمِيهِم بِحِجَارَةٖ مِّن سِجِّيلٖ

Suna jifan su da duwatsu na qonanniyar laka?



Sourate: Suratul Fil

Verset : 5

فَجَعَلَهُمۡ كَعَصۡفٖ مَّأۡكُولِۭ

Sai da Ya mayar da su kamar karmami da aka cinye[1]?


1- Wannan babban abu ya auku ne a shekara ta 571 bayan haihuwar Annabi Isa (). A shekarar ne aka haifi Manzon Allah ().


Sourate: Suratu Quraish

Verset : 1

لِإِيلَٰفِ قُرَيۡشٍ

Domin sabon da Quraishawa suka yi



Sourate: Suratu Quraish

Verset : 2

إِۦلَٰفِهِمۡ رِحۡلَةَ ٱلشِّتَآءِ وَٱلصَّيۡفِ

Sabonsu na yin safara a lokacin xari (zuwa qasar Yaman) da lokacin bazara (zuwan qasar Sham)[1]


1- A cikin aminci ba tare da tsoron komai ba.


Sourate: Suratu Quraish

Verset : 3

فَلۡيَعۡبُدُواْ رَبَّ هَٰذَا ٱلۡبَيۡتِ

To sai su bauta wa Ubangijin wannan Xakin[1]


1- Watau Xakin Ka’aba mai alfarma.


Sourate: Suratu Quraish

Verset : 4

ٱلَّذِيٓ أَطۡعَمَهُم مِّن جُوعٖ وَءَامَنَهُم مِّنۡ خَوۡفِۭ

Wanda Ya ciyar da su daga yunwa, Ya kuma amintar da su daga tsoro



Sourate: Ma’un

Verset : 1

أَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي يُكَذِّبُ بِٱلدِّينِ

Shin ka ga wanda yake qaryata ranar sakamako?



Sourate: Ma’un

Verset : 2

فَذَٰلِكَ ٱلَّذِي يَدُعُّ ٱلۡيَتِيمَ

To shi ne wanda yake ingije maraya (daga haqqinsa)



Sourate: Ma’un

Verset : 3

وَلَا يَحُضُّ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ

Ba kuma ya kwaxaitarwa wajen ciyar da miskini



Sourate: Ma’un

Verset : 4

فَوَيۡلٞ لِّلۡمُصَلِّينَ

To tsananin azaba ya tabbata ga masallata



Sourate: Ma’un

Verset : 5

ٱلَّذِينَ هُمۡ عَن صَلَاتِهِمۡ سَاهُونَ

Waxanda suke masu rafkana su bar sallarsu[1]


1- Watau ba sa yin ta a kan lokaci, ko ma su bar sallar a wasu lokuta ba tare da sun yi ta ba.


Sourate: Ma’un

Verset : 6

ٱلَّذِينَ هُمۡ يُرَآءُونَ

Waxanda su ne suke yin riya



Sourate: Ma’un

Verset : 7

وَيَمۡنَعُونَ ٱلۡمَاعُونَ

Suke kuma hana kayan taimako[1]


1- Watau ba sa bayar da zakkar dukiyoyinsu, ba sa taimaka wa masu buqata, ko kayan aro ba sa bayarwa.


Sourate: Suratul Kausar

Verset : 1

إِنَّآ أَعۡطَيۡنَٰكَ ٱلۡكَوۡثَرَ

Lalle Mu Mun ba ka alheri mai yawa[1]


1- Watau qoramar Alkausara ta gidan Aljanna.


Sourate: Suratul Kausar

Verset : 2

فَصَلِّ لِرَبِّكَ وَٱنۡحَرۡ

To sai ka yi salla don Ubangijinka, ka kuma soke (abin hadayarka)



Sourate: Suratul Kausar

Verset : 3

إِنَّ شَانِئَكَ هُوَ ٱلۡأَبۡتَرُ

Lalle mai qin ka shi ne mai yankakken alheri[1]


1- Watau wanda a duk sanda aka tuna da shi za a yi tir da shi.


Sourate: Suratul Kafirun

Verset : 1

قُلۡ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡكَٰفِرُونَ

Ka ce: “Ya ku waxannan kafirai



Sourate: Suratul Kafirun

Verset : 2

لَآ أَعۡبُدُ مَا تَعۡبُدُونَ

“Ba zan bauta wa abin da kuke bauta wa ba



Sourate: Suratul Kafirun

Verset : 3

وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ

“Ku kuma ba masu bautar abin da nake bauta wa ba ne



Sourate: Suratul Kafirun

Verset : 4

وَلَآ أَنَا۠ عَابِدٞ مَّا عَبَدتُّمۡ

“Ni kuma ba mai bauta wa abin da kuka bauta wa ba ne



Sourate: Suratul Kafirun

Verset : 5

وَلَآ أَنتُمۡ عَٰبِدُونَ مَآ أَعۡبُدُ

“Ku ma ba za ku bauta wa abin da nake bauta wa ba



Sourate: Suratul Kafirun

Verset : 6

لَكُمۡ دِينُكُمۡ وَلِيَ دِينِ

“Addininku na gare ku, ni ma kuma addinina na gare ni[1].”


1- Annabi () ya ga wani yana karanta wannan Surar sai ya ce: “Amma dai wannan haqiqa ya kuvuta daga shirka”.


Sourate: Suratun Nasr

Verset : 1

إِذَا جَآءَ نَصۡرُ ٱللَّهِ وَٱلۡفَتۡحُ

Idan nasarar Allah ta zo da kuma buxe (Makka)



Sourate: Suratun Nasr

Verset : 2

وَرَأَيۡتَ ٱلنَّاسَ يَدۡخُلُونَ فِي دِينِ ٱللَّهِ أَفۡوَاجٗا

Ka kuma ga mutane suna shiga addinin Allah qungiya-qungiya



Sourate: Suratun Nasr

Verset : 3

فَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ وَٱسۡتَغۡفِرۡهُۚ إِنَّهُۥ كَانَ تَوَّابَۢا

To ka yi tasbihi da yabon Ubangijinka, ka kuma nemi gafararsa. Lalle Shi Ya kasance Mai karvar tuba ne



Sourate: Suratul Masad

Verset : 1

تَبَّتۡ يَدَآ أَبِي لَهَبٖ وَتَبَّ

Hannayen Abu Lahabi[1] sun halaka, shi ma kuma ya halaka


1- Abu Lahab, xaya ne daga baffannin Manzon Allah wanda ya nuna wa Annabi () qiyayya ya mutu yana kafiri.


Sourate: Suratul Masad

Verset : 2

مَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُ مَالُهُۥ وَمَا كَسَبَ

Dukiyarsa da abin da ya tsuwurwurta ba su amfana masa komai ba