Sourate: Suratut Tin

Verset : 1

وَٱلتِّينِ وَٱلزَّيۡتُونِ

Na rantse da vaure da zaitun[1]


1- Watau wuraren tsirowarsu, watau Sham, ko kuma su kansu waxanan bishiyoyin.


Sourate: Suratut Tin

Verset : 2

وَطُورِ سِينِينَ

Da (dutsen) Xuri Sinina



Sourate: Suratut Tin

Verset : 3

وَهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ ٱلۡأَمِينِ

Da wannan garin amintacce (watau Makka)



Sourate: Suratut Tin

Verset : 4

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِيٓ أَحۡسَنِ تَقۡوِيمٖ

Haqiqa Mun halicci mutum a kan mafi kyan diri



Sourate: Suratut Tin

Verset : 5

ثُمَّ رَدَدۡنَٰهُ أَسۡفَلَ سَٰفِلِينَ

Sannan Muka mayar da shi mafi qasqancin qasqantattu[1]


1- Watau ya mayar da shi tsoho tukuf a duniya, ko kuma a lahira ya zamanto xan wuta.


Sourate: Suratut Tin

Verset : 6

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَلَهُمۡ أَجۡرٌ غَيۡرُ مَمۡنُونٖ

Sai fa waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, to su kam suna da lada ba mai yankewa ba



Sourate: Suratut Tin

Verset : 7

فَمَا يُكَذِّبُكَ بَعۡدُ بِٱلدِّينِ

To (kai kafiri) me ya sa kake qaryata ranar sakamako bayan haka?



Sourate: Suratut Tin

Verset : 8

أَلَيۡسَ ٱللَّهُ بِأَحۡكَمِ ٱلۡحَٰكِمِينَ

Ashe Allah ba Shi ne Mafi iya hukuncin masu hukunci ba?



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 1

ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 2

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ

Ya halicci mutum daga gudan jini[1]


1- Watau bayan yana xigon maniyyi.


Sourate: Suratul Alaq

Verset : 3

ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ

Ka yi karatu alhali Ubangijinka Shi ne mafi karamci



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 4

ٱلَّذِي عَلَّمَ بِٱلۡقَلَمِ

Wanda Ya koyar ta (hanyar) alqalami



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 5

عَلَّمَ ٱلۡإِنسَٰنَ مَا لَمۡ يَعۡلَمۡ

Ya koyar da mutum abin da bai sani ba



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 6

كَلَّآ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَيَطۡغَىٰٓ

Tabbas! Lalle (jinsin) mutum haqiqa yana yin xagawa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 7

أَن رَّءَاهُ ٱسۡتَغۡنَىٰٓ

Don ya ga kansa yana cikin wadata



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 8

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰٓ

Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makomar (taka) take



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 9

أَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي يَنۡهَىٰ

Ka ba ni labarin wanda yake hana



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 10

عَبۡدًا إِذَا صَلَّىٰٓ

Bawa yayin da ya yi salla



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 11

أَرَءَيۡتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلۡهُدَىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi Bawan) ya kasance a kan shiriya



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 12

أَوۡ أَمَرَ بِٱلتَّقۡوَىٰٓ

Ko kuma ya yi umarni da taqawa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 13

أَرَءَيۡتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi mai hanawar) ya qaryata ya kuma ba da baya



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 14

أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 15

كَلَّا لَئِن لَّمۡ يَنتَهِ لَنَسۡفَعَۢا بِٱلنَّاصِيَةِ

A’aha! Tabbas idan bai hanu ba to za Mu ja shi ta makwarkwaxar kai



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 16

نَاصِيَةٖ كَٰذِبَةٍ خَاطِئَةٖ

Makwarkwaxar kai mai qaryatawa, mai aikata laifi



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 17

فَلۡيَدۡعُ نَادِيَهُۥ

To ya kirawo majalisar tasa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 18

سَنَدۡعُ ٱلزَّبَانِيَةَ

Mu kuma lalle za Mu kirawo (mala’iku) zabaniyawa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 19

كَلَّا لَا تُطِعۡهُ وَٱسۡجُدۡۤ وَٱقۡتَرِب۩

Faufau! Kada ka bi shi, ka kuma yi salla, ka kusanta (ga Allah)



Sourate: Qadar

Verset : 1

إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ فِي لَيۡلَةِ ٱلۡقَدۡرِ

Lalle Mu Muka saukar da shi (Alqur’ani) a daren Lailatul-Qadari[1] (dare mai daraja)


1- Watau lokacin da aka fara saukar da jumullarsa a sama ta kusa, kamar yadda a cikin watan Ramadana ne ake fara saukar da shi ga Manzon Allah () a kogon Hira.


Sourate: Qadar

Verset : 2

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا لَيۡلَةُ ٱلۡقَدۡرِ

Mene ne ya sanar da kai mece ce Lailatul-Qadari?



Sourate: Qadar

Verset : 3

لَيۡلَةُ ٱلۡقَدۡرِ خَيۡرٞ مِّنۡ أَلۡفِ شَهۡرٖ

(Daren) Lailatul-Qadari ya fi wata dubu alheri