Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 73

نَحۡنُ جَعَلۡنَٰهَا تَذۡكِرَةٗ وَمَتَٰعٗا لِّلۡمُقۡوِينَ

Mu ne Muka sanya ta wa’azi da kuma abin amfani ga matafiya



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 74

فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ

Saboda haka sai ka tsarkake Sunan Ubangijinka Mai girma



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 75

۞فَلَآ أُقۡسِمُ بِمَوَٰقِعِ ٱلنُّجُومِ

To ina yin rantsuwa da mafaxar taurari



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 76

وَإِنَّهُۥ لَقَسَمٞ لَّوۡ تَعۡلَمُونَ عَظِيمٌ

Lalle ita kuwa rantsuwa ce mai girma, da kuna ganewa.[1]


1- Domin taurari da tafiyarsu a sararin sama abu ne mai cike da ayoyi da darussa masu ximbin yawa.


Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 77

إِنَّهُۥ لَقُرۡءَانٞ كَرِيمٞ

Lalle shi Alqur’ani ne mai girma



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 78

فِي كِتَٰبٖ مَّكۡنُونٖ

A cikin littafi abin kiyayewa (daga wani sauyi).[1]


1- Shi ne Lauhul Mahfuz.


Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 79

لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلۡمُطَهَّرُونَ

Babu mai tava shi sai tsarkakakku



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 80

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Saukakke ne daga Ubangijin talikai



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 81

أَفَبِهَٰذَا ٱلۡحَدِيثِ أَنتُم مُّدۡهِنُونَ

Yanzu wannan zance kuke qaryatawa?



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 82

وَتَجۡعَلُونَ رِزۡقَكُمۡ أَنَّكُمۡ تُكَذِّبُونَ

Kuke kuma sanya (godiyar) arzikinku shi ne ku riqa qaryatawa?



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 83

فَلَوۡلَآ إِذَا بَلَغَتِ ٱلۡحُلۡقُومَ

Me ya hana idan (rai) ya isa maqogwaro



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 84

وَأَنتُمۡ حِينَئِذٖ تَنظُرُونَ

Ku kuma a lokacin kuna kallo



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 85

وَنَحۡنُ أَقۡرَبُ إِلَيۡهِ مِنكُمۡ وَلَٰكِن لَّا تُبۡصِرُونَ

Mu ne kuwa Muka fi ku kusanci da shi, sai dai kuma ba kwa gani



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 86

فَلَوۡلَآ إِن كُنتُمۡ غَيۡرَ مَدِينِينَ

Me ya hana idan da kun zamanto ba waxanda za a tasa ba ne



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 87

تَرۡجِعُونَهَآ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Ku dawo da shi (ran) mana idan kun kasance masu gaskiya



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 88

فَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلۡمُقَرَّبِينَ

Amma kuma idan (mai mutuwar) ya kasance daga makusanta



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 89

فَرَوۡحٞ وَرَيۡحَانٞ وَجَنَّتُ نَعِيمٖ

To (sakamakonsa) hutu ne da arziki mai daxi, da kuma Aljannar ni’ima



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 90

وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنۡ أَصۡحَٰبِ ٱلۡيَمِينِ

Idan kuma ya kasance daga ma’abota hannun dama ne



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 91

فَسَلَٰمٞ لَّكَ مِنۡ أَصۡحَٰبِ ٱلۡيَمِينِ

To aminci ya tabbata a gare ka don zamanka na hannun dama



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 92

وَأَمَّآ إِن كَانَ مِنَ ٱلۡمُكَذِّبِينَ ٱلضَّآلِّينَ

Idan kuwa ya kasance daga masu qaryatawa ne vatattu



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 93

فَنُزُلٞ مِّنۡ حَمِيمٖ

To kavaki ne na tafasasshen ruwa (sakamakonsa)



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 94

وَتَصۡلِيَةُ جَحِيمٍ

Da kuma shiga wutar Jahannama



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 95

إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ حَقُّ ٱلۡيَقِينِ

Lalle wannan (bayani na cikin wannan Surar) shi ne haqiqanin gaskiya



Sourate: Suratul Waqi’a

Verset : 96

فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ

To ka yi tasbihi da tsarkake sunan Ubangijinka mai girma



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 1

سَبَّحَ لِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Abin da yake cikin sammai da qasa ya yi tasbihi ga Allah; Shi ne kuma Mabuwayi, Mai hikima



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 2

لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ يُحۡيِۦ وَيُمِيتُۖ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Mulkin sammai da qasa nasa ne; Yana rayawa, Yana kuma kashewa; kuma Shi Mai iko ne a kan komai



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 3

هُوَ ٱلۡأَوَّلُ وَٱلۡأٓخِرُ وَٱلظَّـٰهِرُ وَٱلۡبَاطِنُۖ وَهُوَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٌ

Shi ne Na farko kuma Na qarshe, kuma Bayyananne kuma Voyayye[1]; Shi kuma Masanin komai ne


1- Na farko, watau babu wani abu gabaninsa. Na qarshe, watau babu wani abu bayansa. Bayyananne, watau babu wani abu sama da shi. Voyayye, watau babu wani abu da ya fi shi vuya.


Sourate: Suratul Hadid

Verset : 4

هُوَ ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ ثُمَّ ٱسۡتَوَىٰ عَلَى ٱلۡعَرۡشِۖ يَعۡلَمُ مَا يَلِجُ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا يَخۡرُجُ مِنۡهَا وَمَا يَنزِلُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ وَمَا يَعۡرُجُ فِيهَاۖ وَهُوَ مَعَكُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡۚ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

Shi ne wanda Ya halicci sammai da qasa cikin kwana shida, sannan Ya daidaitu a kan Al’arshi. Yana sane da abin da yake shiga cikin qasa da abin da yake fitowa daga cikinta, da kuma abin da yake saukowa daga sama da abin da yake hawa cikinta; kuma Shi Yana tare da ku a duk inda kuka kasance[1]. Allah kuwa Mai ganin duk abin da kuke aikatawa ne


1- Watau da iliminsa. Babu wani abu da yake vuya a gare shi, yana kuma ganin duk abin da suke aikatawa.


Sourate: Suratul Hadid

Verset : 5

لَّهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَإِلَى ٱللَّهِ تُرۡجَعُ ٱلۡأُمُورُ

Mulkin sammai da qasa nasa ne. Kuma ga Allah ake mayar da al’amura



Sourate: Suratul Hadid

Verset : 6

يُولِجُ ٱلَّيۡلَ فِي ٱلنَّهَارِ وَيُولِجُ ٱلنَّهَارَ فِي ٱلَّيۡلِۚ وَهُوَ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Yana shigar da dare cikin rana, Yana kuma shigar da rana cikin dare. Kuma Shi Masanin abubuwan da suke cikin qiraza ne