Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 39

وَمَا لَا تُبۡصِرُونَ

Da kuma abin da ba kwa gani



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 40

إِنَّهُۥ لَقَوۡلُ رَسُولٖ كَرِيمٖ

Lalle shi (Alqur’ani) tabbas zance ne na wani manzo mai girma



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 41

وَمَا هُوَ بِقَوۡلِ شَاعِرٖۚ قَلِيلٗا مَّا تُؤۡمِنُونَ

Shi kuwa ba zancen mawaqi ba ne. Kaxan ne qwarai kuke yin imani



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 42

وَلَا بِقَوۡلِ كَاهِنٖۚ قَلِيلٗا مَّا تَذَكَّرُونَ

Ba kuma zance ne na boka ba. Kaxan ne qwarai kuke wa’azantuwa



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 43

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Shi saukakke ne daga Ubangijin halittu



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 44

وَلَوۡ تَقَوَّلَ عَلَيۡنَا بَعۡضَ ٱلۡأَقَاوِيلِ

Kuma da ya qaga Mana wasu maganganu



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 45

لَأَخَذۡنَا مِنۡهُ بِٱلۡيَمِينِ

Tabbas da Mun kama shi da qarfi



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 46

ثُمَّ لَقَطَعۡنَا مِنۡهُ ٱلۡوَتِينَ

Sannan da Mun yanke masa jijiyar zuciyarsa



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 47

فَمَا مِنكُم مِّنۡ أَحَدٍ عَنۡهُ حَٰجِزِينَ

Sannan kuma ba wani xaya daga cikinku da zai kare shi



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 48

وَإِنَّهُۥ لَتَذۡكِرَةٞ لِّلۡمُتَّقِينَ

Lalle shi (Alqur’ani) wa’azi ne ga masu kiyaye dokokin Allah



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 49

وَإِنَّا لَنَعۡلَمُ أَنَّ مِنكُم مُّكَذِّبِينَ

Lalle kuma Mu Muna sane da cewa a cikinku akwai masu qaryatawa



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 50

وَإِنَّهُۥ لَحَسۡرَةٌ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma lalle shi tabbas nadama ce ga kafirai



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 51

وَإِنَّهُۥ لَحَقُّ ٱلۡيَقِينِ

Kuma lalle shi tabbas gaskiya ce ta sakankancewa



Sourate: Suratul Haqqa

Verset : 52

فَسَبِّحۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلۡعَظِيمِ

Saboda haka ka yi tasbihi da sunan Ubangijinka Mai girma



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 1

سَأَلَ سَآئِلُۢ بِعَذَابٖ وَاقِعٖ

Mai tambaya ya yi tambaya game da wata azaba mai aukuwa[1]


1- Watau wadda Annabi () yake musu kashedi da ita idan sun qi imani. Duba Suratul Anfal, aya ta 32. Mai tambayar kuwa shi ne Nadhru xan Haris.


Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 2

لِّلۡكَٰفِرِينَ لَيۡسَ لَهُۥ دَافِعٞ

Ga kafirai (wadda) ba ta da wani mai kaxe ta



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 3

مِّنَ ٱللَّهِ ذِي ٱلۡمَعَارِجِ

Daga Allah Mai matattakalai



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 4

تَعۡرُجُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيۡهِ فِي يَوۡمٖ كَانَ مِقۡدَارُهُۥ خَمۡسِينَ أَلۡفَ سَنَةٖ

Mala’iku tare da Jibrilu suna hawa zuwa gare Shi a cikin wata rana (wadda) gwargwadonta yake daidai da shekara dubu hamsin



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 5

فَٱصۡبِرۡ صَبۡرٗا جَمِيلًا

Sai ka yi haquri kyakkyawan haquri



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 6

إِنَّهُمۡ يَرَوۡنَهُۥ بَعِيدٗا

Lalle su suna ganin ta mai nisa ce



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 7

وَنَرَىٰهُ قَرِيبٗا

Mu kuma Muna ganin ta kusa-kusa



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 8

يَوۡمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلۡمُهۡلِ

A ranar da sama za ta kasance kamar narkakkiyar dalma



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 9

وَتَكُونُ ٱلۡجِبَالُ كَٱلۡعِهۡنِ

Duwatsu kuma su zama kamar kaxaxxiyar auduga (ta gashin tumaki)



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 10

وَلَا يَسۡـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمٗا

Kuma aboki ba ya tambayar aboki



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 11

يُبَصَّرُونَهُمۡۚ يَوَدُّ ٱلۡمُجۡرِمُ لَوۡ يَفۡتَدِي مِنۡ عَذَابِ يَوۡمِئِذِۭ بِبَنِيهِ

(Alhali kuma) ana nuna musu junansu. Mai laifi ya riqa burin ina ma zai fanshi kansa daga azabar wannan rana da ‘ya’yansa



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 12

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

Da matarsa da xan’uwansa



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 13

وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِي تُـٔۡوِيهِ

Da danginsa waxanda suke kare shi



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 14

وَمَن فِي ٱلۡأَرۡضِ جَمِيعٗا ثُمَّ يُنجِيهِ

Da ma duk wanda yake a bayan qasa baki xaya, sannan (fansar) ta tserar da shi



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 15

كَلَّآۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

Faufau! Lalle ita (wutar) Laza ce



Sourate: Suratul Ma’arij

Verset : 16

نَزَّاعَةٗ لِّلشَّوَىٰ

Mai xaxxaye fatar kai