Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 16

ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَبۡلَ ذَٰلِكَ مُحۡسِنِينَ

Suna masu kwasar abin da Ubangijinsu Ya ba su. Lalle su sun zamanto kafin wannan (ranar) masu kyautata ayyuka ne



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 17

كَانُواْ قَلِيلٗا مِّنَ ٱلَّيۡلِ مَا يَهۡجَعُونَ

Sun kasance kaxan ne na dare suke bacci[1]


1- Watau sun kasance masu yawaita sallar dare.


Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 18

وَبِٱلۡأَسۡحَارِ هُمۡ يَسۡتَغۡفِرُونَ

A gefin asuba kuma su suna neman gafara



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 19

وَفِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

A cikin dukiyoyinsu kuma akwai wani haqqi na mai bara da mai kamewa daga yin ta



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 20

وَفِي ٱلۡأَرۡضِ ءَايَٰتٞ لِّلۡمُوقِنِينَ

A cikin qasa kuma akwai ayoyi ga masu sakankancewa



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 21

وَفِيٓ أَنفُسِكُمۡۚ أَفَلَا تُبۡصِرُونَ

Da kuma cikin kawunanku. Yanzu ba kwa lura ba?



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 22

وَفِي ٱلسَّمَآءِ رِزۡقُكُمۡ وَمَا تُوعَدُونَ

A cikin sammai kuma akwai arzikinku da kuma abin da aka yi muku alkawarinsa



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 23

فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ إِنَّهُۥ لَحَقّٞ مِّثۡلَ مَآ أَنَّكُمۡ تَنطِقُونَ

To na rantse da Ubangijin sammai da qasa, lalle shi (abin da ake yi muku gargaxinsa) tabbas gaskiya ne kamar dai yadda kuke yin magana



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 24

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلۡمُكۡرَمِينَ

Shin labarin baqin Ibrahimu masu girma[1] ya zo maka?


1- Su ne mala’iku da Allah ya aiko.


Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 25

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ

Lokacin da suka shiga wurinsa sai suka ce: “Muna maka sallama;” ya ce: “Aminci ya tabbata gare ku, (ku) mutane ne da ba sanannu ba.”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 26

فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجۡلٖ سَمِينٖ

Sai ya saxaxa da sauri zuwa ga iyalinsa, sai ya zo da wani xan maraqi mai mai



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 27

فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيۡهِمۡ قَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ

Sai ya kusanta shi gare su, ya ce: “Yanzu ba za ku ci ba?”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 28

فَأَوۡجَسَ مِنۡهُمۡ خِيفَةٗۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ

(Da suka qi ci) sai ya tsorata da su, suka ce: “Kada ka tsorata;” suka kuma yi masa albishir da samun yaro mai ilimi[1]


1- Watau Annabi Ishaq ().


Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 29

فَأَقۡبَلَتِ ٱمۡرَأَتُهُۥ فِي صَرَّةٖ فَصَكَّتۡ وَجۡهَهَا وَقَالَتۡ عَجُوزٌ عَقِيمٞ

Sannan sai matarsa ta gabato su cikin wata qara, sai ta mari fuskarta ta ce: “Yanzu tsohuwa bakarara (ita ce za ta haihu?)”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 30

قَالُواْ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ

Suka ce, “Kamar haka Ubangijinki Ya ce, lalle Shi Mai hikima ne, Masani.”