Sourate: Suratul Hijr

Verset : 91

ٱلَّذِينَ جَعَلُواْ ٱلۡقُرۡءَانَ عِضِينَ

(Su ne) waxanda suka mai da Alqur’ani kashi-kashi[1]


1- Watau suka yi imani da wani vangare suka kafirce wa wani vangare.


Sourate: Suratul Hijr

Verset : 92

فَوَرَبِّكَ لَنَسۡـَٔلَنَّهُمۡ أَجۡمَعِينَ

(Na rantse) da Ubangijinka tabbas za Mu tambaye su gaba xaya



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 93

عَمَّا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

Game da abin da suka kasance suna aikatawa



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 94

فَٱصۡدَعۡ بِمَا تُؤۡمَرُ وَأَعۡرِضۡ عَنِ ٱلۡمُشۡرِكِينَ

To ka tsage gaskiyar abin da aka umarce ka da shi, ka kuma kawar da kanka daga mushirikai



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 95

إِنَّا كَفَيۡنَٰكَ ٱلۡمُسۡتَهۡزِءِينَ

Lalle Mu Mun isar maka (sharrin) masu izgili



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 96

ٱلَّذِينَ يَجۡعَلُونَ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَۚ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ

(Su ne) waxanda suke sanya wani abin bauta tare da Allah. Ba ko da daxewa ba za su sani



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 97

وَلَقَدۡ نَعۡلَمُ أَنَّكَ يَضِيقُ صَدۡرُكَ بِمَا يَقُولُونَ

Haqiqa kuma Muna sane da cewa qirjinka yana qunci game da abin da suke faxa



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 98

فَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ وَكُن مِّنَ ٱلسَّـٰجِدِينَ

To sai ka yi tasbihi tare da godiyar Ubangijinka, ka kuma zamo cikin masu sujjada



Sourate: Suratul Hijr

Verset : 99

وَٱعۡبُدۡ رَبَّكَ حَتَّىٰ يَأۡتِيَكَ ٱلۡيَقِينُ

Ka kuma bauta wa Ubangijinka har yaqini ya zo maka (wato mutuwa)



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 1

أَتَىٰٓ أَمۡرُ ٱللَّهِ فَلَا تَسۡتَعۡجِلُوهُۚ سُبۡحَٰنَهُۥ وَتَعَٰلَىٰ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Al’amarin Allah ya zo, don haka kada ku nemi gaggauto shi (watau ranar alqiyama). Tsarki ya tabbata a gare Shi, Ya kuma xaukaka daga abin da suke tara (Shi da shi)



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 2

يُنَزِّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ بِٱلرُّوحِ مِنۡ أَمۡرِهِۦ عَلَىٰ مَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦٓ أَنۡ أَنذِرُوٓاْ أَنَّهُۥ لَآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱتَّقُونِ

Yana saukar da mala’iku da wahayi na umarninsa ga waxanda Ya ga dama daga bayinsa da cewa,: “Ku yi gargaxi cewa,, lalle ba wani abin bauta sai Ni, to sai ku kiyaye dokokina.”



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 3

خَلَقَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ بِٱلۡحَقِّۚ تَعَٰلَىٰ عَمَّا يُشۡرِكُونَ

Ya halicci sammai da qasa da gaskiya. Ya xaukaka daga abin da suke tara (Shi da shi)



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 4

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِن نُّطۡفَةٖ فَإِذَا هُوَ خَصِيمٞ مُّبِينٞ

Ya halicci mutum daga maniyyi, sai ga shi mai jayayya a fili



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 5

وَٱلۡأَنۡعَٰمَ خَلَقَهَاۖ لَكُمۡ فِيهَا دِفۡءٞ وَمَنَٰفِعُ وَمِنۡهَا تَأۡكُلُونَ

Ya kuma halicci dabbobin ni’ima. Kuna da (abin) xumama jiki tattare da su, da kuma sauran abubuwan amfani; daga gare su ne kuma kuke ci



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 6

وَلَكُمۡ فِيهَا جَمَالٌ حِينَ تُرِيحُونَ وَحِينَ تَسۡرَحُونَ

Kuma kuna da abubuwan ado a tattare da su, lokacin da kuke dawowa (daga kiwo) da kuma lokacin da kuke fita (da safe)



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 7

وَتَحۡمِلُ أَثۡقَالَكُمۡ إِلَىٰ بَلَدٖ لَّمۡ تَكُونُواْ بَٰلِغِيهِ إِلَّا بِشِقِّ ٱلۡأَنفُسِۚ إِنَّ رَبَّكُمۡ لَرَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Suna kuma xaukar kayayyakinku masu nauyi zuwa garin da ba za ku iya isar sa ba sai da qyar. Lalle Ubangijinku tabbas Mai tausayi ne, Mai rahama



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 8

وَٱلۡخَيۡلَ وَٱلۡبِغَالَ وَٱلۡحَمِيرَ لِتَرۡكَبُوهَا وَزِينَةٗۚ وَيَخۡلُقُ مَا لَا تَعۡلَمُونَ

Dawakai da kuma alfadarai da jakai (Ya halitta muku su) don ku hau su kuma su zama ado. Zai kuma hallici abin da ma ba ku sani ba



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 9

وَعَلَى ٱللَّهِ قَصۡدُ ٱلسَّبِيلِ وَمِنۡهَا جَآئِرٞۚ وَلَوۡ شَآءَ لَهَدَىٰكُمۡ أَجۡمَعِينَ

Kuma bayanin hanya madaidaiciya haqqi ne a kan Allah, daga kuma (hanyar) akwai karkatacciya. Da kuma Ya ga dama lalle da Ya shirye ku gaba xaya



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 10

هُوَ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗۖ لَّكُم مِّنۡهُ شَرَابٞ وَمِنۡهُ شَجَرٞ فِيهِ تُسِيمُونَ

Shi ne wanda Ya saukar da ruwa daga sama; daga gare shi ne kuke sha, daga gare shi ne kuma bishiyoyi suke (sha) wanda da su ne kuke kiwon (dabbobinku)



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 11

يُنۢبِتُ لَكُم بِهِ ٱلزَّرۡعَ وَٱلزَّيۡتُونَ وَٱلنَّخِيلَ وَٱلۡأَعۡنَٰبَ وَمِن كُلِّ ٱلثَّمَرَٰتِۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّقَوۡمٖ يَتَفَكَّرُونَ

Da shi (ruwan) Yake tsiro muku da shuke-shuke da zaitun da dabinai da inabai da kuma kowanne irin ‘ya’yan itace. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga mutanen da suke tunani



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 12

وَسَخَّرَ لَكُمُ ٱلَّيۡلَ وَٱلنَّهَارَ وَٱلشَّمۡسَ وَٱلۡقَمَرَۖ وَٱلنُّجُومُ مُسَخَّرَٰتُۢ بِأَمۡرِهِۦٓۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يَعۡقِلُونَ

Ya kuma hore muku dare da rana da kuma wata; taurari ma ababen horewa ne da umarninsa. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutane masu hankali



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 13

وَمَا ذَرَأَ لَكُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُخۡتَلِفًا أَلۡوَٰنُهُۥٓۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّقَوۡمٖ يَذَّكَّرُونَ

Da kuma abubuwan da Ya halitta muku a qasa masu launi iri daban-daban. Lalle a game da wannan tabbas akwai aya ga mutanen da suke wa’azantuwa



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 14

وَهُوَ ٱلَّذِي سَخَّرَ ٱلۡبَحۡرَ لِتَأۡكُلُواْ مِنۡهُ لَحۡمٗا طَرِيّٗا وَتَسۡتَخۡرِجُواْ مِنۡهُ حِلۡيَةٗ تَلۡبَسُونَهَاۖ وَتَرَى ٱلۡفُلۡكَ مَوَاخِرَ فِيهِ وَلِتَبۡتَغُواْ مِن فَضۡلِهِۦ وَلَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Shi ne kuma wanda Ya hore muku kogi don ku ci daddaxan nama mai taushi daga gare shi, ku kuma riqa fito da kayan ado daga cikinsa waxanda kuke xaurawa, kuma ka ga jiragen ruwa suna keta shi don kuma ku nema daga falalarsa (Ubangiji) don kuma ku riqa godiya



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 15

وَأَلۡقَىٰ فِي ٱلۡأَرۡضِ رَوَٰسِيَ أَن تَمِيدَ بِكُمۡ وَأَنۡهَٰرٗا وَسُبُلٗا لَّعَلَّكُمۡ تَهۡتَدُونَ

Ya kuma sanya wa qasa turaku don kada ta riqa tangal-tangal da ku da kuma qoramu da hanyoyi don ku riqa gane (inda kuka dosa)



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 16

وَعَلَٰمَٰتٖۚ وَبِٱلنَّجۡمِ هُمۡ يَهۡتَدُونَ

Da kuma alamomin (hanya). Da kuma taurari ne suke gane (inda suka dosa)



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 17

أَفَمَن يَخۡلُقُ كَمَن لَّا يَخۡلُقُۚ أَفَلَا تَذَكَّرُونَ

Yanzu wanda Yake halitta (zai yi) daidai da wanda ba ya halitta? Yanzo ba kwa wa’a zantu ba?



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 18

وَإِن تَعُدُّواْ نِعۡمَةَ ٱللَّهِ لَا تُحۡصُوهَآۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Idan kuma da za ku qirga ni’imar Allah to ba za ku iya qididdige ta ba. Lalle Allah tabbas Mai gafara ne, Mai jin qai



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 19

وَٱللَّهُ يَعۡلَمُ مَا تُسِرُّونَ وَمَا تُعۡلِنُونَ

Allah kuma Ya san abin da kuke voyewa da abin da kuke bayyanawa



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 20

وَٱلَّذِينَ يَدۡعُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ لَا يَخۡلُقُونَ شَيۡـٔٗا وَهُمۡ يُخۡلَقُونَ

Waxannan kuma suke bauta wa ba Allah ba, ba sa iya halittar komai, su ne ma ake halittar su



Sourate: Suratun Nahl

Verset : 21

أَمۡوَٰتٌ غَيۡرُ أَحۡيَآءٖۖ وَمَا يَشۡعُرُونَ أَيَّانَ يُبۡعَثُونَ

Matattu ne su ba rayayyu ba; ba sa kuma sanin sanda za a tashe su