Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 31

وَأُزۡلِفَتِ ٱلۡجَنَّةُ لِلۡمُتَّقِينَ غَيۡرَ بَعِيدٍ

Aka kuma kusantar da Aljanna ga masu tsoron Allah, ba tare da nisa ba



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 32

هَٰذَا مَا تُوعَدُونَ لِكُلِّ أَوَّابٍ حَفِيظٖ

(Sai a ce da su): “Wannan ne abin da ake yi muku alqawarinsa, (ga shi nan a tanade) ga duk wani mai yawan komawa ga Allah, mai kiyaye (dokokinsa)



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 33

مَّنۡ خَشِيَ ٱلرَّحۡمَٰنَ بِٱلۡغَيۡبِ وَجَآءَ بِقَلۡبٖ مُّنِيبٍ

“Wanda ya ji tsoron Allah a voye, ya zo kuma da zuciya mai komawa ga Allah.”



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 34

ٱدۡخُلُوهَا بِسَلَٰمٖۖ ذَٰلِكَ يَوۡمُ ٱلۡخُلُودِ

(Za a ce da su): Ku shige ta da aminci; wannan ita ce ranar dawwama



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 35

لَهُم مَّا يَشَآءُونَ فِيهَا وَلَدَيۡنَا مَزِيدٞ

Suna da duk abin da suka dama a cikinta, kuma wurinmu akwai wani qari[1]


1- Watau qarin wasu ni’imomi, daga cikinsu akwai ganin Fuskar Allah da samun yardarsa ta har abada.


Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 36

وَكَمۡ أَهۡلَكۡنَا قَبۡلَهُم مِّن قَرۡنٍ هُمۡ أَشَدُّ مِنۡهُم بَطۡشٗا فَنَقَّبُواْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ هَلۡ مِن مَّحِيصٍ

Al’ummu nawa Muka hallaka a gabaninsu waxanda suka fi su tsananin qarfi, sai suka riqa bincike cikin garuruwa ko akwai wata matsera



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 37

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَذِكۡرَىٰ لِمَن كَانَ لَهُۥ قَلۡبٌ أَوۡ أَلۡقَى ٱلسَّمۡعَ وَهُوَ شَهِيدٞ

Lalle game da wannan tabbas akwai wa’azi ga wanda ya kasance yana da hankali ko kuma ya karkaxe kunne (don sauraron wa’azi), alhali zuciyarsa tana tare da shi



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 38

وَلَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا فِي سِتَّةِ أَيَّامٖ وَمَا مَسَّنَا مِن لُّغُوبٖ

Haqiqa kuma Mun halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu cikin kwana shida, kuma wata gajiya ba ta shafe mu ba



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 39

فَٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَا يَقُولُونَ وَسَبِّحۡ بِحَمۡدِ رَبِّكَ قَبۡلَ طُلُوعِ ٱلشَّمۡسِ وَقَبۡلَ ٱلۡغُرُوبِ

To ka yi haquri a kan abin da suke faxa, ka kuma yi tasbihi da yabon Ubangijinka kafin fudowar rana da kuma kafin faxuwarta



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 40

وَمِنَ ٱلَّيۡلِ فَسَبِّحۡهُ وَأَدۡبَٰرَ ٱلسُّجُودِ

Da daddare kuma sai ka tsarkake shi, da kuma bayan salloli



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 41

وَٱسۡتَمِعۡ يَوۡمَ يُنَادِ ٱلۡمُنَادِ مِن مَّكَانٖ قَرِيبٖ

Ka kuma saurara ranar da mai kira zai yi kira[1] daga wani wuri makusanci


1- Watau mala’ikan da aka wakilta domin busa qaho.


Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 42

يَوۡمَ يَسۡمَعُونَ ٱلصَّيۡحَةَ بِٱلۡحَقِّۚ ذَٰلِكَ يَوۡمُ ٱلۡخُرُوجِ

A ranar da (talikai) za su ji tsawa ta gaskiya[1]. Wannan ita ce ranar fitowa (daga qabari)


1- Watau busa ta biyu.


Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 43

إِنَّا نَحۡنُ نُحۡيِۦ وَنُمِيتُ وَإِلَيۡنَا ٱلۡمَصِيرُ

Lalle Mu ne Muke rayawa, Muke kuma kashewa, kuma makoma zuwa gare Mu ne



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 44

يَوۡمَ تَشَقَّقُ ٱلۡأَرۡضُ عَنۡهُمۡ سِرَاعٗاۚ ذَٰلِكَ حَشۡرٌ عَلَيۡنَا يَسِيرٞ

A ranar da qasa za ta tsattsage musu (su fito) da gaggawa. Wannan tattarawa ce mai sauqi a gare Mu



Sourate: Suratu Qaf 

Verset : 45

نَّحۡنُ أَعۡلَمُ بِمَا يَقُولُونَۖ وَمَآ أَنتَ عَلَيۡهِم بِجَبَّارٖۖ فَذَكِّرۡ بِٱلۡقُرۡءَانِ مَن يَخَافُ وَعِيدِ

Mu ne Muka fi sanin abin da (kafiran Makka) suke faxa; kuma kai ba mai tilasta musu ba ne; saboda haka sai ka yi wa’azi da Alqur’ani ga wanda yake tsoron azabata



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 1

وَٱلذَّـٰرِيَٰتِ ذَرۡوٗا

Na rantse da iskoki masu ta da qura



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 2

فَٱلۡحَٰمِلَٰتِ وِقۡرٗا

Sannan da (giragizai) waxanda suke xauke da nauyin ruwa



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 3

فَٱلۡجَٰرِيَٰتِ يُسۡرٗا

Da jiragen ruwa masu gudu a sauqaqe



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 4

فَٱلۡمُقَسِّمَٰتِ أَمۡرًا

Da kuma mala’iku masu raba abubuwa



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 5

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٞ

Lalle abin da ake yi muku alqawarinsa tabbas gaskiya ne



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 6

وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٞ

Kuma lalle sakamako tabbas mai afkuwa ne



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 7

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡحُبُكِ

Na rantse da sama ma’abociyar hanyoyi



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 8

إِنَّكُمۡ لَفِي قَوۡلٖ مُّخۡتَلِفٖ

Lalle ku (mutanen Makka) tabbas kuna cikin magana mai sassavawa



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 9

يُؤۡفَكُ عَنۡهُ مَنۡ أُفِكَ

Ana karkatar da wanda aka karkatar daga gare shi (Annabi ko Alqur’ani)



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 10

قُتِلَ ٱلۡخَرَّـٰصُونَ

An la’anci maqaryata[1]


1- Watau game da Annabi () da kuma Alqur’ani.


Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 11

ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي غَمۡرَةٖ سَاهُونَ

Waxanda suke rafkanannu a cikin jahilci



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 12

يَسۡـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Suna tambayar yaushe ne ranar sakamako?



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 13

يَوۡمَ هُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ يُفۡتَنُونَ

A ranar da su za a azabtar da su kan wuta



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 14

ذُوقُواْ فِتۡنَتَكُمۡ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ

(A ce da su): “Ku xanxani azabarku, wannan shi ne abin da kuka kasance kuna neman gaggautowarsa.”



Sourate: Suratuz Zariyat

Verset : 15

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٍ

Lalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da idanuwan (ruwa)