Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 12

فِيهَا عَيۡنٞ جَارِيَةٞ

A cikinta akwai marmaro mai gudana



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 13

فِيهَا سُرُرٞ مَّرۡفُوعَةٞ

A cikinta akwai gadaje maxaukaka



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 14

وَأَكۡوَابٞ مَّوۡضُوعَةٞ

Da kofuna a ajijjiye



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 15

وَنَمَارِقُ مَصۡفُوفَةٞ

Da matasan kai a jejjere



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 16

وَزَرَابِيُّ مَبۡثُوثَةٌ

Da dardumai a shisshimfixe



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ

Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 18

وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ

Da kuma sama yadda aka xaga ta?



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 19

وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ

Da kuma duwatsu yadda aka kakkafa su?



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 20

وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ

Da kuma qasa yadda aka shimfixa ta?



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 21

فَذَكِّرۡ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٞ

To ka yi wa’azi, lalle kai mai wa’azi ne kawai



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 22

لَّسۡتَ عَلَيۡهِم بِمُصَيۡطِرٍ

Kai ba mai tilasta su ba ne



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 23

إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ

Sai dai wanda ya ba da baya ya kuma kafirce



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 24

فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَكۡبَرَ

To Allah zai azabtar da shi azaba mafi girma[1]


1- Watau wutar Jahannama inda zai dawwama a cikinta har abada.


Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 25

إِنَّ إِلَيۡنَآ إِيَابَهُمۡ

Lalle zuwa gare Mu ne makomarsu take



Sourate: Suratul Ghashiya

Verset : 26

ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا حِسَابَهُم

Sannan kuma a kanmu ne hisabinsu yake



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 1

وَٱلۡفَجۡرِ

Na rantse da alfijir



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 2

وَلَيَالٍ عَشۡرٖ

Da kuma darare goma[1]


1- Watau kwanaki goma na farkon watan Zulhijja.


Sourate: Suratul Fajr

Verset : 3

وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ

Da kuma abin da yake cika[1] da kuma mara[2]


1- Watau bibbiyu ko hurhuxu ko shida-shida da sauransu.


2- Watau xaya ko uku ko biyar da sauransu.


Sourate: Suratul Fajr

Verset : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ

Da kuma dare lokacin da yake tafiya (cikin duhu)



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 5

هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ

Shin a game da waxannan akwai rantsuwa (mai gamsarwa) ga mai hankali[1]?


1- Watau duk mai hankali zai gamsu da waxannan rantse-rantse.


Sourate: Suratul Fajr

Verset : 6

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ba ga Adawa?



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 7

إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ

(Watau qabilar) Iramu ma’abociyar tsawo



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 8

ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Wadda ba a halicci irinta ba a cikin garuruwa (a tsananin qarfi)



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ

Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 10

وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ

Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 11

ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 12

فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ

Suka kuma yawaita varna a cikinsu



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 13

فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ

Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani



Sourate: Suratul Fajr

Verset : 14

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ

Lalle Ubangijinka tabbas Yana nan a madakata[1]


1- Watau yana wurin da yake hangen xaukacin ayyukan bayinsa.


Sourate: Suratul Fajr

Verset : 15

فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ

Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”