فِيهَا عَيۡنٞ جَارِيَةٞ
A cikinta akwai marmaro mai gudana
Partager :
فِيهَا سُرُرٞ مَّرۡفُوعَةٞ
A cikinta akwai gadaje maxaukaka
وَأَكۡوَابٞ مَّوۡضُوعَةٞ
Da kofuna a ajijjiye
وَنَمَارِقُ مَصۡفُوفَةٞ
Da matasan kai a jejjere
وَزَرَابِيُّ مَبۡثُوثَةٌ
Da dardumai a shisshimfixe
أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ
Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?
وَإِلَى ٱلسَّمَآءِ كَيۡفَ رُفِعَتۡ
Da kuma sama yadda aka xaga ta?
وَإِلَى ٱلۡجِبَالِ كَيۡفَ نُصِبَتۡ
Da kuma duwatsu yadda aka kakkafa su?
وَإِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَيۡفَ سُطِحَتۡ
Da kuma qasa yadda aka shimfixa ta?
فَذَكِّرۡ إِنَّمَآ أَنتَ مُذَكِّرٞ
To ka yi wa’azi, lalle kai mai wa’azi ne kawai
لَّسۡتَ عَلَيۡهِم بِمُصَيۡطِرٍ
Kai ba mai tilasta su ba ne
إِلَّا مَن تَوَلَّىٰ وَكَفَرَ
Sai dai wanda ya ba da baya ya kuma kafirce
فَيُعَذِّبُهُ ٱللَّهُ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَكۡبَرَ
To Allah zai azabtar da shi azaba mafi girma[1]
1- Watau wutar Jahannama inda zai dawwama a cikinta har abada.
إِنَّ إِلَيۡنَآ إِيَابَهُمۡ
Lalle zuwa gare Mu ne makomarsu take
ثُمَّ إِنَّ عَلَيۡنَا حِسَابَهُم
Sannan kuma a kanmu ne hisabinsu yake
وَٱلۡفَجۡرِ
Na rantse da alfijir
وَلَيَالٍ عَشۡرٖ
Da kuma darare goma[1]
1- Watau kwanaki goma na farkon watan Zulhijja.
وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ
Da kuma abin da yake cika[1] da kuma mara[2]
1- Watau bibbiyu ko hurhuxu ko shida-shida da sauransu.2- Watau xaya ko uku ko biyar da sauransu.
وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ
Da kuma dare lokacin da yake tafiya (cikin duhu)
هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ
Shin a game da waxannan akwai rantsuwa (mai gamsarwa) ga mai hankali[1]?
1- Watau duk mai hankali zai gamsu da waxannan rantse-rantse.
أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ
Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ba ga Adawa?
إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ
(Watau qabilar) Iramu ma’abociyar tsawo
ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ
Wadda ba a halicci irinta ba a cikin garuruwa (a tsananin qarfi)
وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ
Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura
وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ
Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku
ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ
Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa
فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ
Suka kuma yawaita varna a cikinsu
فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ
Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani
إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ
Lalle Ubangijinka tabbas Yana nan a madakata[1]
1- Watau yana wurin da yake hangen xaukacin ayyukan bayinsa.
فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ
Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”