Sourate: Suratus Saffat

Verset : 175

وَأَبۡصِرۡهُمۡ فَسَوۡفَ يُبۡصِرُونَ

Kuma ka ganar da su (sakamakon kafirci), sannan ba da daxewa ba za su gani



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 176

أَفَبِعَذَابِنَا يَسۡتَعۡجِلُونَ

Yanzu azabarmu suke neman gaggautowa?



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 177

فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمۡ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلۡمُنذَرِينَ

To lokacin da (azabar) ta sauka a sararin gidajensu, ai asubar waxanda aka yi wa gargaxi ta munana



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 178

وَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ حِينٖ

Kuma ka rabu da su har zuwa wani lokaci



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 179

وَأَبۡصِرۡ فَسَوۡفَ يُبۡصِرُونَ

Ka kuma ganar (da su sakamakon kafirci), ba da daxewa ba za su gani



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 180

سُبۡحَٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلۡعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ

Ubangijinka wanda yake Ubangiji ne Mabuwayi Ya tsarkaka daga abin da suke sifanta (Shi da shi)



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 181

وَسَلَٰمٌ عَلَى ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Aminci kuma ya tabbata bisa ga manzanni



Sourate: Suratus Saffat

Verset : 182

وَٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Dukkan yabo ya tabbata ga Allah Ubangijin talikai



Sourate: Suratu Sad

Verset : 1

صٓۚ وَٱلۡقُرۡءَانِ ذِي ٱلذِّكۡرِ

SAD[1]. “Na rantse da Alqur’ani ma’abocin xaukaka


1- Duba Suratul Baqara aya ta 1, hashiya ta 8.


Sourate: Suratu Sad

Verset : 2

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي عِزَّةٖ وَشِقَاقٖ

Sai dai waxanda suka kafirta suna cikin girman kai ne da jayayya



Sourate: Suratu Sad

Verset : 3

كَمۡ أَهۡلَكۡنَا مِن قَبۡلِهِم مِّن قَرۡنٖ فَنَادَواْ وَّلَاتَ حِينَ مَنَاصٖ

Al’ummu nawa Muka hallaka gabaninsu, sai suka yi ta kururuwar neman agaji, alhali kuwa lokacin ba na neman tsira ba ne



Sourate: Suratu Sad

Verset : 4

وَعَجِبُوٓاْ أَن جَآءَهُم مُّنذِرٞ مِّنۡهُمۡۖ وَقَالَ ٱلۡكَٰفِرُونَ هَٰذَا سَٰحِرٞ كَذَّابٌ

Suka kuma yi mamaki don mai gargaxi ya zo musu daga cikinsu; kuma kafirai suka ce: “Wannan mai sihiri ne babban maqaryaci



Sourate: Suratu Sad

Verset : 5

أَجَعَلَ ٱلۡأٓلِهَةَ إِلَٰهٗا وَٰحِدًاۖ إِنَّ هَٰذَا لَشَيۡءٌ عُجَابٞ

“Yanzu yaya zai mayar da alloli Allah guda xaya? Lalle wannan abu ne mai ban mamaki.”



Sourate: Suratu Sad

Verset : 6

وَٱنطَلَقَ ٱلۡمَلَأُ مِنۡهُمۡ أَنِ ٱمۡشُواْ وَٱصۡبِرُواْ عَلَىٰٓ ءَالِهَتِكُمۡۖ إِنَّ هَٰذَا لَشَيۡءٞ يُرَادُ

Manyansu kuma suka tafi (suna cewa): “Ku yi tafiyarku, kuma ku yi haquri a kan (bautar) allolinku; lalle wannan wani shiryayyen abu ne ake nufi



Sourate: Suratu Sad

Verset : 7

مَا سَمِعۡنَا بِهَٰذَا فِي ٱلۡمِلَّةِ ٱلۡأٓخِرَةِ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا ٱخۡتِلَٰقٌ

“Ba mu tava jin irin wannan ba a addinin da ya wuce[1], wannan ba komai ba ne sai qage


1- Watau addinin Annabi Isa ().


Sourate: Suratu Sad

Verset : 8

أَءُنزِلَ عَلَيۡهِ ٱلذِّكۡرُ مِنۢ بَيۡنِنَاۚ بَلۡ هُمۡ فِي شَكّٖ مِّن ذِكۡرِيۚ بَل لَّمَّا يَذُوقُواْ عَذَابِ

“Yanzu a saukar masa da Alqur’ani a tsakaninmu?” Ba haka ba ne, su dai suna kokwanto ne game da tunatarwata; bar su, ai har yanzu ba su xanxani azabata ba ne



Sourate: Suratu Sad

Verset : 9

أَمۡ عِندَهُمۡ خَزَآئِنُ رَحۡمَةِ رَبِّكَ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡوَهَّابِ

Ko kuwa a wurinsu ne taskokin rahamar Ubangijinka Mabuwayi Mai baiwa suke?



Sourate: Suratu Sad

Verset : 10

أَمۡ لَهُم مُّلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَاۖ فَلۡيَرۡتَقُواْ فِي ٱلۡأَسۡبَٰبِ

Ko kuma mulkin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu nasu ne? To sai su kama hanyoyin zuwa sama (domin su aikata abin da suke so)



Sourate: Suratu Sad

Verset : 11

جُندٞ مَّا هُنَالِكَ مَهۡزُومٞ مِّنَ ٱلۡأَحۡزَابِ

(Waxannan) wata runduna ce da za a murqushe ta, kamar sauran al’ummun da suka gabata (waxanda suka qaryata manzanninsu)



Sourate: Suratu Sad

Verset : 12

كَذَّبَتۡ قَبۡلَهُمۡ قَوۡمُ نُوحٖ وَعَادٞ وَفِرۡعَوۡنُ ذُو ٱلۡأَوۡتَادِ

Mutanen Nuhu sun qaryata kafin su (mutan Makka) da Adawa da Fir’auna mai turaku



Sourate: Suratu Sad

Verset : 13

وَثَمُودُ وَقَوۡمُ لُوطٖ وَأَصۡحَٰبُ لۡـَٔيۡكَةِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡأَحۡزَابُ

Da kuma Samudawa da mutanen Luxu da mutanen Sarqaqiya[1]. Waxannan su ne al’ummun


1- Su ne mutanen Annabi Shu’aibu ().


Sourate: Suratu Sad

Verset : 14

إِن كُلٌّ إِلَّا كَذَّبَ ٱلرُّسُلَ فَحَقَّ عِقَابِ

Babu xaya daga cikinsu wanda bai qaryata manzanni ba, sai uqubata ta wajaba (a kansu)



Sourate: Suratu Sad

Verset : 15

وَمَا يَنظُرُ هَـٰٓؤُلَآءِ إِلَّا صَيۡحَةٗ وَٰحِدَةٗ مَّا لَهَا مِن فَوَاقٖ

Kuma ba abin da waxannan suke sauraro sai busa guda xaya wadda ba ta da makawa



Sourate: Suratu Sad

Verset : 16

وَقَالُواْ رَبَّنَا عَجِّل لَّنَا قِطَّنَا قَبۡلَ يَوۡمِ ٱلۡحِسَابِ

Suka kuma ce: “Ya Ubangijinmu, Ka gaggauto mana rabonmu (na azaba) tun kafin ranar hisabi!”



Sourate: Suratu Sad

Verset : 17

ٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَا يَقُولُونَ وَٱذۡكُرۡ عَبۡدَنَا دَاوُۥدَ ذَا ٱلۡأَيۡدِۖ إِنَّهُۥٓ أَوَّابٌ

(Sai Allah Ya ce): “Ka yi haquri a kan abin da suke faxa, ka kuma tuna bawanmu Dawuda ma’abocin qarfi; lalle shi ya kasance mai yawan komawa ne (ga Allah)



Sourate: Suratu Sad

Verset : 18

إِنَّا سَخَّرۡنَا ٱلۡجِبَالَ مَعَهُۥ يُسَبِّحۡنَ بِٱلۡعَشِيِّ وَٱلۡإِشۡرَاقِ

Lalle Mu Mun hore masa duwatsu suna yin tasbihi tare da shi a yamma da hantsi



Sourate: Suratu Sad

Verset : 19

وَٱلطَّيۡرَ مَحۡشُورَةٗۖ كُلّٞ لَّهُۥٓ أَوَّابٞ

Da kuma tsuntsaye a tattare; dukkaninsu suna biyayya a gare shi



Sourate: Suratu Sad

Verset : 20

وَشَدَدۡنَا مُلۡكَهُۥ وَءَاتَيۡنَٰهُ ٱلۡحِكۡمَةَ وَفَصۡلَ ٱلۡخِطَابِ

Kuma Muka qarfafa mulkinsa, Muka kuma ba shi hikima da bayyana hukunce-hukunce (tsakanin masu husuma)



Sourate: Suratu Sad

Verset : 21

۞وَهَلۡ أَتَىٰكَ نَبَؤُاْ ٱلۡخَصۡمِ إِذۡ تَسَوَّرُواْ ٱلۡمِحۡرَابَ

Shin labarin abokan husuma ya zo maka, yayin da suka haura wurin ibada?



Sourate: Suratu Sad

Verset : 22

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَىٰ دَاوُۥدَ فَفَزِعَ مِنۡهُمۡۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ خَصۡمَانِ بَغَىٰ بَعۡضُنَا عَلَىٰ بَعۡضٖ فَٱحۡكُم بَيۡنَنَا بِٱلۡحَقِّ وَلَا تُشۡطِطۡ وَٱهۡدِنَآ إِلَىٰ سَوَآءِ ٱلصِّرَٰطِ

Yayin da suka shiga wurin Dawuda sai ya tsorata da su, suka ce: “Kada ka tsorata, (mu biyun nan) masu husuma ne, xayanmu ya zalunci xaya, sai ka yi hukunci a tsakaninmu da gaskiya, kada kuma ka yi zalunci, kuma ka shiryar da mu hanya madaidaiciya