Sourate: Suratul Baqara

Verset : 233

۞وَٱلۡوَٰلِدَٰتُ يُرۡضِعۡنَ أَوۡلَٰدَهُنَّ حَوۡلَيۡنِ كَامِلَيۡنِۖ لِمَنۡ أَرَادَ أَن يُتِمَّ ٱلرَّضَاعَةَۚ وَعَلَى ٱلۡمَوۡلُودِ لَهُۥ رِزۡقُهُنَّ وَكِسۡوَتُهُنَّ بِٱلۡمَعۡرُوفِۚ لَا تُكَلَّفُ نَفۡسٌ إِلَّا وُسۡعَهَاۚ لَا تُضَآرَّ وَٰلِدَةُۢ بِوَلَدِهَا وَلَا مَوۡلُودٞ لَّهُۥ بِوَلَدِهِۦۚ وَعَلَى ٱلۡوَارِثِ مِثۡلُ ذَٰلِكَۗ فَإِنۡ أَرَادَا فِصَالًا عَن تَرَاضٖ مِّنۡهُمَا وَتَشَاوُرٖ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡهِمَاۗ وَإِنۡ أَرَدتُّمۡ أَن تَسۡتَرۡضِعُوٓاْ أَوۡلَٰدَكُمۡ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ إِذَا سَلَّمۡتُم مَّآ ءَاتَيۡتُم بِٱلۡمَعۡرُوفِۗ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

Kuma iyaye mata za su shayar da ‘ya’yansu tsawon shekara biyu cikakku, ga wanda ya yi nufin ya cika wa’adi na shayarwa. Kuma wajibi ne a kan wanda aka yi wa haihuwa ya ciyar da su (mata masu shayarwa) da yi musu tufafi ta hanyar da aka saba. Ba a xora wa wani rai sai abin da zai iya. Kar a cutar da uwa saboda xanta, haka kuma kar a cutar da uba saboda xansa. Kuma kwatankwacin irin wannan ya wajaba kan magajinsa. To idan su biyun sun yi nufin yaye bisa ga yarjejeniya da shawara da junansu, to babu laifi a kansu. Kuma idan kun yi nufin nema wa ‘ya’yanku mai shayarwa, to babu laifi a kanku idan kun bayar da abin da ya kamata ta yadda aka saba. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku sani cewa, lalle Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 234

وَٱلَّذِينَ يُتَوَفَّوۡنَ مِنكُمۡ وَيَذَرُونَ أَزۡوَٰجٗا يَتَرَبَّصۡنَ بِأَنفُسِهِنَّ أَرۡبَعَةَ أَشۡهُرٖ وَعَشۡرٗاۖ فَإِذَا بَلَغۡنَ أَجَلَهُنَّ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ فِيمَا فَعَلۡنَ فِيٓ أَنفُسِهِنَّ بِٱلۡمَعۡرُوفِۗ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٞ

Kuma waxanda suke mutuwa daga cikinku, suna kuma barin mata na aure, (su matan) za su yi zaman jira na wata huxu da kwana goma. To idan sun cika wa’adinsu, babu laifi a kanku (waliyyansu) cikin duk abin da suka aikata game da kawunansu ta hanyar da aka saba (a shari’a). Kuma Allah Mai cikakken sani ne game da abin da kuke aikatawa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 235

وَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ فِيمَا عَرَّضۡتُم بِهِۦ مِنۡ خِطۡبَةِ ٱلنِّسَآءِ أَوۡ أَكۡنَنتُمۡ فِيٓ أَنفُسِكُمۡۚ عَلِمَ ٱللَّهُ أَنَّكُمۡ سَتَذۡكُرُونَهُنَّ وَلَٰكِن لَّا تُوَاعِدُوهُنَّ سِرًّا إِلَّآ أَن تَقُولُواْ قَوۡلٗا مَّعۡرُوفٗاۚ وَلَا تَعۡزِمُواْ عُقۡدَةَ ٱلنِّكَاحِ حَتَّىٰ يَبۡلُغَ ٱلۡكِتَٰبُ أَجَلَهُۥۚ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ مَا فِيٓ أَنفُسِكُمۡ فَٱحۡذَرُوهُۚ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ غَفُورٌ حَلِيمٞ

Kuma babu laifi a kanku game da abin da kuka yi wa mata jirwaye da shi na neman aurensu ko kuma kuka voye a cikin zukatanku, Allah Ya san cewa ku za ku riqa maganarsu, sai dai kar ku yi alqawari da su (na aure) a asirce, sai dai in za ku faxi zance wanda yake sananne a (shari’a). Kuma kada ku qulla igiyar aure (da mata masu takaba) har sai faralin idda ya cika wa’adinsa. Kuma ku sani lalle Allah Ya san abin da yake cikin zukatanku, don haka ku kiyaye Shi. Kuma ku sani lalle Allah Mai yawan gafara ne, Mai haquri



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 236

لَّا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ إِن طَلَّقۡتُمُ ٱلنِّسَآءَ مَا لَمۡ تَمَسُّوهُنَّ أَوۡ تَفۡرِضُواْ لَهُنَّ فَرِيضَةٗۚ وَمَتِّعُوهُنَّ عَلَى ٱلۡمُوسِعِ قَدَرُهُۥ وَعَلَى ٱلۡمُقۡتِرِ قَدَرُهُۥ مَتَٰعَۢا بِٱلۡمَعۡرُوفِۖ حَقًّا عَلَى ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Babu laifi (sadaqi) a kanku idan kun saki mata, matuqar ba ku riga kun sadu da su ko kuma kun yanka musu sadaki sananne ba. Sai ku yi musu kyauta (ta kwantar da hankali); mai yalwa daidai yalwarsa; talaka ma daidai qarfinsa. (Wannan) wata kyauta ce (da za a bayar) ta hanyar da aka saba; haqqi ne a kan masu kyautatawa[1]


1- Allah ya yi umarni ga mijin wanda ya saki matarsa kafin ya tare da ita, lalle ya yi mata wata kyauta ta kwantar da hankali gwargwadon qarfinsa.


Sourate: Suratul Baqara

Verset : 237

وَإِن طَلَّقۡتُمُوهُنَّ مِن قَبۡلِ أَن تَمَسُّوهُنَّ وَقَدۡ فَرَضۡتُمۡ لَهُنَّ فَرِيضَةٗ فَنِصۡفُ مَا فَرَضۡتُمۡ إِلَّآ أَن يَعۡفُونَ أَوۡ يَعۡفُوَاْ ٱلَّذِي بِيَدِهِۦ عُقۡدَةُ ٱلنِّكَاحِۚ وَأَن تَعۡفُوٓاْ أَقۡرَبُ لِلتَّقۡوَىٰۚ وَلَا تَنسَوُاْ ٱلۡفَضۡلَ بَيۡنَكُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٌ

Idan kuwa kun sake su ne tun kafin ku sadu da su, alhalin kuma kun yanka musu sadaki, to sai (ku bayar) da rabin abin da kuka yanka, sai fa in su matan sun yi afuwa ko kuma wanda a hannunsa igiyar aure take ya yi afuwa[1]; kuma ku yi afuwa shi ya fi kusa ga taqawa. Kuma kada ku manta da kyautatawar da take tsakaninku. Lalle Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne


1- Wanda igiyar aure take hannusa, shi ne mijin. Yana iya yafe wa, ya bar mata duk sadakin baki xaya.


Sourate: Suratul Baqara

Verset : 238

حَٰفِظُواْ عَلَى ٱلصَّلَوَٰتِ وَٱلصَّلَوٰةِ ٱلۡوُسۡطَىٰ وَقُومُواْ لِلَّهِ قَٰنِتِينَ

Ku kiyaye salloli da kuma salla mafificiya, kuma ku tsaya domin Allah kuna masu nutsuwa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 239

فَإِنۡ خِفۡتُمۡ فَرِجَالًا أَوۡ رُكۡبَانٗاۖ فَإِذَآ أَمِنتُمۡ فَٱذۡكُرُواْ ٱللَّهَ كَمَا عَلَّمَكُم مَّا لَمۡ تَكُونُواْ تَعۡلَمُونَ

To idan kuna cikin halin tsoro, sai ku yi salla kuna tafe da qafafuwanku ko a kan ababan hawanku. To idan kun amintu, sai ku ambaci Allah kamar yadda Ya sanar da ku abin da ba ku kasance kun sani ba



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 240

وَٱلَّذِينَ يُتَوَفَّوۡنَ مِنكُمۡ وَيَذَرُونَ أَزۡوَٰجٗا وَصِيَّةٗ لِّأَزۡوَٰجِهِم مَّتَٰعًا إِلَى ٱلۡحَوۡلِ غَيۡرَ إِخۡرَاجٖۚ فَإِنۡ خَرَجۡنَ فَلَا جُنَاحَ عَلَيۡكُمۡ فِي مَا فَعَلۡنَ فِيٓ أَنفُسِهِنَّ مِن مَّعۡرُوفٖۗ وَٱللَّهُ عَزِيزٌ حَكِيمٞ

Kuma waxanda suke rasuwa daga cikinku suke barin matan aure, (to za su yi) wasiyya ga matansu cewa, a jiyar da su daxi har zuwa shekara, ba tare da an fitar da su ba; to idan su suka fita da kansu, to babu laifi a kanku dangane da abin da suka aikata wa kansu na abin da yake sananne a shari’a. Kuma Allah Mabuwayi ne, Mai hikima[1]


1- Wasu malamai suna ganin wannan aya an shafe ta da aya ta 234. Wasu kuma suna ganin umarni ne ga mazaje su yi wasiyya ga magadansu a kan su qale matansu su zauna a gidajensu tsawon shekara xaya, Wannan kuwa ya kasance ne kafin Allah ya shar’anta rabon gado, a inda ya ambaci kason mace daga dukiyar mijinta.


Sourate: Suratul Baqara

Verset : 241

وَلِلۡمُطَلَّقَٰتِ مَتَٰعُۢ بِٱلۡمَعۡرُوفِۖ حَقًّا عَلَى ٱلۡمُتَّقِينَ

Kuma matan da aka sake su suna da wata kyauta ta kwantar da hankali ta hanyar da aka saba, (wannan) haqqi ne a kan masu taqawa



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 242

كَذَٰلِكَ يُبَيِّنُ ٱللَّهُ لَكُمۡ ءَايَٰتِهِۦ لَعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Kamar haka ne Allah Yake bayyana muku ayoyinsa don ku hankalta



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 243

۞أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلَّذِينَ خَرَجُواْ مِن دِيَٰرِهِمۡ وَهُمۡ أُلُوفٌ حَذَرَ ٱلۡمَوۡتِ فَقَالَ لَهُمُ ٱللَّهُ مُوتُواْ ثُمَّ أَحۡيَٰهُمۡۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَذُو فَضۡلٍ عَلَى ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَشۡكُرُونَ

Shin ba ka ga waxanda suka fita daga gidajensu ba su dubbai don tsoron mutuwa, sai Allah Ya ce da su: “Ku mutu”, sannan Ya raya su? Lalle Allah Ma’abocin falala ne ga mutane, sai dai yawancin mutane ba sa godiya



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 244

وَقَٰتِلُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٞ

Kuma ku yi yaqi don xaukaka kalmar Allah, kuma ku sani cewa, lalle Allah Mai ji ne, Masani



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 245

مَّن ذَا ٱلَّذِي يُقۡرِضُ ٱللَّهَ قَرۡضًا حَسَنٗا فَيُضَٰعِفَهُۥ لَهُۥٓ أَضۡعَافٗا كَثِيرَةٗۚ وَٱللَّهُ يَقۡبِضُ وَيَبۡصُۜطُ وَإِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Wane ne zai ba wa Allah kyakkyawan rance, sai Ya ninka masa shi ninki mai yawa? Kuma Allah ne Yake kame (dukiya), Yake kuma shimfixa ta, kuma zuwa gare Shi za a mayar da ku



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 246

أَلَمۡ تَرَ إِلَى ٱلۡمَلَإِ مِنۢ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ مِنۢ بَعۡدِ مُوسَىٰٓ إِذۡ قَالُواْ لِنَبِيّٖ لَّهُمُ ٱبۡعَثۡ لَنَا مَلِكٗا نُّقَٰتِلۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ قَالَ هَلۡ عَسَيۡتُمۡ إِن كُتِبَ عَلَيۡكُمُ ٱلۡقِتَالُ أَلَّا تُقَٰتِلُواْۖ قَالُواْ وَمَا لَنَآ أَلَّا نُقَٰتِلَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَقَدۡ أُخۡرِجۡنَا مِن دِيَٰرِنَا وَأَبۡنَآئِنَاۖ فَلَمَّا كُتِبَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقِتَالُ تَوَلَّوۡاْ إِلَّا قَلِيلٗا مِّنۡهُمۡۚ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلظَّـٰلِمِينَ

Shin ba ka ga wasu manyan mutane ba daga cikin Banu Isra’ila bayan (mutuwar) Musa yayin da suka faxa wa Annabinsu: “Ka naxa mana wani sarki, wanda za mu yi yaqi (tare da shi) don xaukaka kalmar Allah?” Sai ya ce: “Shin ba kwa tsammanin idan an wajabta muku yaqi, ba za ku yi yaqin ba?” Sai suka ce: “Me zai sa ba za mu yi yaqi don xaukaka kalmar Allah ba, alhali kuwa an fitar da mu daga gidajenmu da ‘ya’yanmu?” To yayin da aka wajabta musu yaqin sai suka juya baya sai ‘yan kaxan daga cikinsu. Kuma Allah Masanin azzalumai ne



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 247

وَقَالَ لَهُمۡ نَبِيُّهُمۡ إِنَّ ٱللَّهَ قَدۡ بَعَثَ لَكُمۡ طَالُوتَ مَلِكٗاۚ قَالُوٓاْ أَنَّىٰ يَكُونُ لَهُ ٱلۡمُلۡكُ عَلَيۡنَا وَنَحۡنُ أَحَقُّ بِٱلۡمُلۡكِ مِنۡهُ وَلَمۡ يُؤۡتَ سَعَةٗ مِّنَ ٱلۡمَالِۚ قَالَ إِنَّ ٱللَّهَ ٱصۡطَفَىٰهُ عَلَيۡكُمۡ وَزَادَهُۥ بَسۡطَةٗ فِي ٱلۡعِلۡمِ وَٱلۡجِسۡمِۖ وَٱللَّهُ يُؤۡتِي مُلۡكَهُۥ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٞ

Kuma Annabinsu ya ce da su: “Lalle haqiqa Allah Ya naxa Xalutu ya zama Sarki gare ku.” Sai suka ce: “Ta yaya zai samu sarauta a kanmu, alhalin mun fi shi cancatar sarauta, kuma ba a ba shi yalwar dukiya ba?” Sai ya ce: “Lalle Allah Ya zave shi a kanku, kuma Ya qare shi da yalwar ilimi da ta girman jiki, kuma Allah Yana bayar da mulkinsa ga wanda Ya ga dama, kuma Allah Mai yalwa ne, Masani.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 248

وَقَالَ لَهُمۡ نَبِيُّهُمۡ إِنَّ ءَايَةَ مُلۡكِهِۦٓ أَن يَأۡتِيَكُمُ ٱلتَّابُوتُ فِيهِ سَكِينَةٞ مِّن رَّبِّكُمۡ وَبَقِيَّةٞ مِّمَّا تَرَكَ ءَالُ مُوسَىٰ وَءَالُ هَٰرُونَ تَحۡمِلُهُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لَّكُمۡ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Sai Annabinsu ya ce da su: “Lalle alamar (cancantar) mulkinsa ita ce akwatin nan da zai zo muku wanda a cikinsa akwai nutsuwa daga Ubangijinku da kuma sauran abin da iyalin Musa suka bari da iyalin Haruna; mala’iku na xauke da shi. Lalle a cikin wannan tabbas akwai aya a gare ku, in kun kasance muminai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 249

فَلَمَّا فَصَلَ طَالُوتُ بِٱلۡجُنُودِ قَالَ إِنَّ ٱللَّهَ مُبۡتَلِيكُم بِنَهَرٖ فَمَن شَرِبَ مِنۡهُ فَلَيۡسَ مِنِّي وَمَن لَّمۡ يَطۡعَمۡهُ فَإِنَّهُۥ مِنِّيٓ إِلَّا مَنِ ٱغۡتَرَفَ غُرۡفَةَۢ بِيَدِهِۦۚ فَشَرِبُواْ مِنۡهُ إِلَّا قَلِيلٗا مِّنۡهُمۡۚ فَلَمَّا جَاوَزَهُۥ هُوَ وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ قَالُواْ لَا طَاقَةَ لَنَا ٱلۡيَوۡمَ بِجَالُوتَ وَجُنُودِهِۦۚ قَالَ ٱلَّذِينَ يَظُنُّونَ أَنَّهُم مُّلَٰقُواْ ٱللَّهِ كَم مِّن فِئَةٖ قَلِيلَةٍ غَلَبَتۡ فِئَةٗ كَثِيرَةَۢ بِإِذۡنِ ٱللَّهِۗ وَٱللَّهُ مَعَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

To yayin da Xalutu ya fita (bayan gari) da rundunarsa, sai ya ce: “Lalle Allah zai jarrabe ku da wata qorama, to duk wanda ya sha daga gare ta, to ba ya tare da ni, duk wanda kuwa bai sha ba, to wannan yana tare da ni, sai dai wanda ya kamfata sau xaya da (tafin) hannunsa.” Gaba xayansu sai suka sha daga cikinta sai ‘yan kaxan daga cikinsu (su ne ba su sha ba). To yayin da ya qetare shi, shi da waxanda suka yi imani tare da shi, sai suka ce: “A yau kam ba mu da iko wajen fuskantar Jalutu da rundunarsa.” Sai waxanda suke da yaqinin cewa za su haxu da Allah suka ce: “Sau da yawa wata runduna ‘yan kaxan takan yi rinjaye a kan wata runduna mai yawa da izinin Allah. Kuma Allah Yana tare da masu haquri.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 250

وَلَمَّا بَرَزُواْ لِجَالُوتَ وَجُنُودِهِۦ قَالُواْ رَبَّنَآ أَفۡرِغۡ عَلَيۡنَا صَبۡرٗا وَثَبِّتۡ أَقۡدَامَنَا وَٱنصُرۡنَا عَلَى ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma yayin da suka yi fito-na-fito da Jalutu da rundunarsa, sai suka ce: “Ya Ubangijinmu, Ka zubo mana haquri na musamman, kuma Ka tabbatar da dugaduganmu, kuma Ka taimake mu a kan mutane kafirai.”



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 251

فَهَزَمُوهُم بِإِذۡنِ ٱللَّهِ وَقَتَلَ دَاوُۥدُ جَالُوتَ وَءَاتَىٰهُ ٱللَّهُ ٱلۡمُلۡكَ وَٱلۡحِكۡمَةَ وَعَلَّمَهُۥ مِمَّا يَشَآءُۗ وَلَوۡلَا دَفۡعُ ٱللَّهِ ٱلنَّاسَ بَعۡضَهُم بِبَعۡضٖ لَّفَسَدَتِ ٱلۡأَرۡضُ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ ذُو فَضۡلٍ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Sai suka murqushe su da izinin Allah, kuma Dawudu ya kashe Jalutu, sai Allah Ya ba shi mulki da hikima, kuma Ya sanar da shi irin abin da Ya ga dama. Ba don yadda Allah Yake kare wani sashin mutane da wani sashi ba, to lalle da qasa ta lalace, sai dai kuma Allah Ma’abocin falala ne ga talikai



Sourate: Suratul Baqara

Verset : 252

تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱللَّهِ نَتۡلُوهَا عَلَيۡكَ بِٱلۡحَقِّۚ وَإِنَّكَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Waxannan ayoyin Allah ne, Muna karanta maka su da gaskiya, kuma lalle kai tabbas kana cikin manzanni