Sourate: Suratu Hud

Verset : 36

وَأُوحِيَ إِلَىٰ نُوحٍ أَنَّهُۥ لَن يُؤۡمِنَ مِن قَوۡمِكَ إِلَّا مَن قَدۡ ءَامَنَ فَلَا تَبۡتَئِسۡ بِمَا كَانُواْ يَفۡعَلُونَ

Aka kuma yi wa Nuhu wahayi cewa: “Ba wanda zai yi imani daga mutanenka sai waxanda suka riga suka yi. To kada ka yi baqin ciki game da abin da suke aikatawa



Sourate: Suratu Hud

Verset : 37

وَٱصۡنَعِ ٱلۡفُلۡكَ بِأَعۡيُنِنَا وَوَحۡيِنَا وَلَا تُخَٰطِبۡنِي فِي ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ إِنَّهُم مُّغۡرَقُونَ

“Ka kuma sassaqa jirgin ruwa a kan idanunmu da koyarwarmu. Kada kuma ka yi Mini maganar komai game da kafirai. Lalle su nutsar da su za a yi.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 38

وَيَصۡنَعُ ٱلۡفُلۡكَ وَكُلَّمَا مَرَّ عَلَيۡهِ مَلَأٞ مِّن قَوۡمِهِۦ سَخِرُواْ مِنۡهُۚ قَالَ إِن تَسۡخَرُواْ مِنَّا فَإِنَّا نَسۡخَرُ مِنكُمۡ كَمَا تَسۡخَرُونَ

Ya kuma riqa sassaqa jirgin, duk sanda kuma wasu manya daga mutanensa suka wuce ta wajensa sai su riqa yi masa ba’a. Ya ce: “Idan kun yi mana ba’a, to lalle mu ma fa (wata rana) za mu yi muku ba’ar kamar yadda kuke mana (yanzu)



Sourate: Suratu Hud

Verset : 39

فَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَ مَن يَأۡتِيهِ عَذَابٞ يُخۡزِيهِ وَيَحِلُّ عَلَيۡهِ عَذَابٞ مُّقِيمٌ

“To ba da daxewa ba za ku san wanda azaba mai kunyatarwa za ta zo masa, kuma wata azaba madawwamiya ta sauka a kansa.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 40

حَتَّىٰٓ إِذَا جَآءَ أَمۡرُنَا وَفَارَ ٱلتَّنُّورُ قُلۡنَا ٱحۡمِلۡ فِيهَا مِن كُلّٖ زَوۡجَيۡنِ ٱثۡنَيۡنِ وَأَهۡلَكَ إِلَّا مَن سَبَقَ عَلَيۡهِ ٱلۡقَوۡلُ وَمَنۡ ءَامَنَۚ وَمَآ ءَامَنَ مَعَهُۥٓ إِلَّا قَلِيلٞ

Har dai zuwa lokacin da umarninmu ya zo, kuma tanderu ya vuvvugo da ruwa, Muka ce: “Ka xauki ma’aurata bibbiyu daga kowace (halitta) a cikinsa (jirgin) haxe da iyalanka in ban da wanda maganar (halakar da shi) ta gabata a kansa, kuma (ka xauki) waxanda suka yi imani.” Ba kuwa waxanda suka yi imani da shi sai ‘yan tsirari



Sourate: Suratu Hud

Verset : 41

۞وَقَالَ ٱرۡكَبُواْ فِيهَا بِسۡمِ ٱللَّهِ مَجۡرٜىٰهَا وَمُرۡسَىٰهَآۚ إِنَّ رَبِّي لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Ya kuma ce: “Ku shiga cikinsa, da sunan Allah ne tafiyarsa da kuma tsayawarsa. Lalle Ubangijina Mai gafara ne, Mai rahama.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 42

وَهِيَ تَجۡرِي بِهِمۡ فِي مَوۡجٖ كَٱلۡجِبَالِ وَنَادَىٰ نُوحٌ ٱبۡنَهُۥ وَكَانَ فِي مَعۡزِلٖ يَٰبُنَيَّ ٱرۡكَب مَّعَنَا وَلَا تَكُن مَّعَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Shi kuma (jirgin) yana tafiya da su cikin raquman ruwa kamar duwatsu, Nuhu kuwa sai ya kirawo xansa alhalin ya kasance a ware waje xaya (ya ce): “Kai xana, ka hawo mana tare da mu, kada ka zama tare da kafirai.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 43

قَالَ سَـَٔاوِيٓ إِلَىٰ جَبَلٖ يَعۡصِمُنِي مِنَ ٱلۡمَآءِۚ قَالَ لَا عَاصِمَ ٱلۡيَوۡمَ مِنۡ أَمۡرِ ٱللَّهِ إِلَّا مَن رَّحِمَۚ وَحَالَ بَيۡنَهُمَا ٱلۡمَوۡجُ فَكَانَ مِنَ ٱلۡمُغۡرَقِينَ

(Xan) ya ce: “Ai zan fake a wani dutse wanda zai kare ni daga ruwan.” (Annabi Nuhu) ya ce: “Yau kam babu mai kariya daga al’amarin Allah sai dai wanda Ya yi wa rahama kawai.” Sai raqumin ruwa ya shiga tsakaninsu, ya zamanto cikin waxanda aka nutsar (a cikin ruwa)



Sourate: Suratu Hud

Verset : 44

وَقِيلَ يَـٰٓأَرۡضُ ٱبۡلَعِي مَآءَكِ وَيَٰسَمَآءُ أَقۡلِعِي وَغِيضَ ٱلۡمَآءُ وَقُضِيَ ٱلۡأَمۡرُ وَٱسۡتَوَتۡ عَلَى ٱلۡجُودِيِّۖ وَقِيلَ بُعۡدٗا لِّلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Aka ce: “Ke qasa, ki haxiye ruwanki, ke kuma sama ki riqe ruwanki, aka kuwa qafar da ruwan, kuma aka gama al’amarin, (jirgin) kuma ya tsaya a kan (dutsen) Judi; aka kuma ce: Halaka ta tabbata ga mutane azzalumai.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 45

وَنَادَىٰ نُوحٞ رَّبَّهُۥ فَقَالَ رَبِّ إِنَّ ٱبۡنِي مِنۡ أَهۡلِي وَإِنَّ وَعۡدَكَ ٱلۡحَقُّ وَأَنتَ أَحۡكَمُ ٱلۡحَٰكِمِينَ

Nuhu kuma ya kira Ubangijinsa sai ya ce: “Ya Ubangijina, lalle xana yana daga iyalina, lalle kuma alqawarinka gaskiya ne, kuma Kai ne Ka fi masu hukunci iya hukunci.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 46

قَالَ يَٰنُوحُ إِنَّهُۥ لَيۡسَ مِنۡ أَهۡلِكَۖ إِنَّهُۥ عَمَلٌ غَيۡرُ صَٰلِحٖۖ فَلَا تَسۡـَٔلۡنِ مَا لَيۡسَ لَكَ بِهِۦ عِلۡمٌۖ إِنِّيٓ أَعِظُكَ أَن تَكُونَ مِنَ ٱلۡجَٰهِلِينَ

(Allah) Ya ce: Ya Nuhu, lalle shi ba ya daga cikin iyalinka, lalle shi aiki ne marar kyau; to kada ka qara tambaya Ta abin da ba ka da sani a kansa; lalle Ni Ina gargaxin ka da kada ka zamanto cikin jahilai



Sourate: Suratu Hud

Verset : 47

قَالَ رَبِّ إِنِّيٓ أَعُوذُ بِكَ أَنۡ أَسۡـَٔلَكَ مَا لَيۡسَ لِي بِهِۦ عِلۡمٞۖ وَإِلَّا تَغۡفِرۡ لِي وَتَرۡحَمۡنِيٓ أَكُن مِّنَ ٱلۡخَٰسِرِينَ

Ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni ina neman tsarinka a kan in tambaye Ka abin da ba ni da sani a kansa, idan kuwa ba Ka yafe mini ba, Ka kuma ji qai na, to zan zamo cikin asararru.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 48

قِيلَ يَٰنُوحُ ٱهۡبِطۡ بِسَلَٰمٖ مِّنَّا وَبَرَكَٰتٍ عَلَيۡكَ وَعَلَىٰٓ أُمَمٖ مِّمَّن مَّعَكَۚ وَأُمَمٞ سَنُمَتِّعُهُمۡ ثُمَّ يَمَسُّهُم مِّنَّا عَذَابٌ أَلِيمٞ

Aka ce: Ya Nuhu, ka sauka cikin aminci daga gare Mu da albarka a gare ka da kuma ga al’ummun da suke tare da kai. Wasu al’ummun kuma za Mu jiyar da su daxi, sannan kuma azaba mai raxaxi daga gare Mu ta same su



Sourate: Suratu Hud

Verset : 49

تِلۡكَ مِنۡ أَنۢبَآءِ ٱلۡغَيۡبِ نُوحِيهَآ إِلَيۡكَۖ مَا كُنتَ تَعۡلَمُهَآ أَنتَ وَلَا قَوۡمُكَ مِن قَبۡلِ هَٰذَاۖ فَٱصۡبِرۡۖ إِنَّ ٱلۡعَٰقِبَةَ لِلۡمُتَّقِينَ

Waxannan suna daga labaran gaibu da muke yi maka wahayinsu, don kai da mutanenka ba ku san su ba kafin wannan (labarin); sai ka yi haquri; haqiqa kyakkyawan qarshe yana ga masu taqawa



Sourate: Suratu Hud

Verset : 50

وَإِلَىٰ عَادٍ أَخَاهُمۡ هُودٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥٓۖ إِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا مُفۡتَرُونَ

Kuma (Mun aiko wa) Adawa xan’uwansu Hudu, ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta da gaskiya sai shi; ku ba wasu ne ba face masu qaga wa (Allah) qarya



Sourate: Suratu Hud

Verset : 51

يَٰقَوۡمِ لَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ أَجۡرًاۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَى ٱلَّذِي فَطَرَنِيٓۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

“Ya ku mutanena, ba na tambayar ku wani lada game da shi (wannan saqo); ladana dai yana ga wanda ya qagi halittata. Yanzu ba za ku hankalta ba?



Sourate: Suratu Hud

Verset : 52

وَيَٰقَوۡمِ ٱسۡتَغۡفِرُواْ رَبَّكُمۡ ثُمَّ تُوبُوٓاْ إِلَيۡهِ يُرۡسِلِ ٱلسَّمَآءَ عَلَيۡكُم مِّدۡرَارٗا وَيَزِدۡكُمۡ قُوَّةً إِلَىٰ قُوَّتِكُمۡ وَلَا تَتَوَلَّوۡاْ مُجۡرِمِينَ

“Kuma ya ku mutanena, ku nemi gafarar Ubangijinku sannan ku tuba gare Shi, zai sauko muku da mamakon ruwan sama, zai kuma qara muku qarfi a kan qarfinku, kada kuma ku ba da baya kuna masu aikata laifi.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 53

قَالُواْ يَٰهُودُ مَا جِئۡتَنَا بِبَيِّنَةٖ وَمَا نَحۡنُ بِتَارِكِيٓ ءَالِهَتِنَا عَن قَوۡلِكَ وَمَا نَحۡنُ لَكَ بِمُؤۡمِنِينَ

Suka ce: “Ya kai Hudu ba ka zo mana da wata hujja ba, kuma ba za mu bar abubuwan da muke bauta ba saboda maganarka, ba kuma za mu yi imani da kai ba



Sourate: Suratu Hud

Verset : 54

إِن نَّقُولُ إِلَّا ٱعۡتَرَىٰكَ بَعۡضُ ءَالِهَتِنَا بِسُوٓءٖۗ قَالَ إِنِّيٓ أُشۡهِدُ ٱللَّهَ وَٱشۡهَدُوٓاْ أَنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تُشۡرِكُونَ

“Ba abin da za mu faxa sai dai kawai (mu ce) wasu abubuwan bautarmu ne suka sa maka tavuwa.” Ya ce: “Ni lalle ina shaidar da Allah, ku ma kuma ku shaida cewa ni lalle ba ruwana da abin da kuke haxa (Allah) da shi



Sourate: Suratu Hud

Verset : 55

مِن دُونِهِۦۖ فَكِيدُونِي جَمِيعٗا ثُمَّ لَا تُنظِرُونِ

“Wanda ba Shi (Allah) ba; to sai ku shirya min makirci gaba xayanku, kar kuma ku saurara mini



Sourate: Suratu Hud

Verset : 56

إِنِّي تَوَكَّلۡتُ عَلَى ٱللَّهِ رَبِّي وَرَبِّكُمۚ مَّا مِن دَآبَّةٍ إِلَّا هُوَ ءَاخِذُۢ بِنَاصِيَتِهَآۚ إِنَّ رَبِّي عَلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

“Lalle ni na dogara ga Allah, Ubangijina kuma Ubangijinku. Babu wata dabba face Shi ne Yake riqe da makwarkwaxarta. Lalle Ubangijina a kan tafarki madaidaici Yake



Sourate: Suratu Hud

Verset : 57

فَإِن تَوَلَّوۡاْ فَقَدۡ أَبۡلَغۡتُكُم مَّآ أُرۡسِلۡتُ بِهِۦٓ إِلَيۡكُمۡۚ وَيَسۡتَخۡلِفُ رَبِّي قَوۡمًا غَيۡرَكُمۡ وَلَا تَضُرُّونَهُۥ شَيۡـًٔاۚ إِنَّ رَبِّي عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٍ حَفِيظٞ

“To idan kuka ba da baya, haqiqa na isar muku abin da aka aiko ni da shi zuwa gare ku. Kuma Ubangijina zai iya musanya wasu mutanen ba ku ba, kuma ba za ku cutar da Shi da komai ba. Lalle Ubangijina Mai kula da komai ne.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 58

وَلَمَّا جَآءَ أَمۡرُنَا نَجَّيۡنَا هُودٗا وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ بِرَحۡمَةٖ مِّنَّا وَنَجَّيۡنَٰهُم مِّنۡ عَذَابٍ غَلِيظٖ

Lokacin kuwa da umarninmu ya zo sai Muka tserar da Hudu shi da waxanda suka ba da gaskiya da shi, saboda wata rahama daga gare mu, Muka kuma tserar da su daga azaba mai gwavi



Sourate: Suratu Hud

Verset : 59

وَتِلۡكَ عَادٞۖ جَحَدُواْ بِـَٔايَٰتِ رَبِّهِمۡ وَعَصَوۡاْ رُسُلَهُۥ وَٱتَّبَعُوٓاْ أَمۡرَ كُلِّ جَبَّارٍ عَنِيدٖ

Waxancan kuwa su ne Adawa, da suka musanta ayoyin Ubangijinsu, suka kuma sava wa manzanninsa, kuma suka bi umarnin duk wani mai girman kai taqadari



Sourate: Suratu Hud

Verset : 60

وَأُتۡبِعُواْ فِي هَٰذِهِ ٱلدُّنۡيَا لَعۡنَةٗ وَيَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۗ أَلَآ إِنَّ عَادٗا كَفَرُواْ رَبَّهُمۡۗ أَلَا بُعۡدٗا لِّعَادٖ قَوۡمِ هُودٖ

Aka kuma biyar musu da la’ana a duniya, haka kuma a ranar alqiyama. Ku saurara! Lalle Adawa kam sun kafirce wa Ubangijinsu. Ku saurara! Halaka ta tabbata ga Adawa mutanen Hudu



Sourate: Suratu Hud

Verset : 61

۞وَإِلَىٰ ثَمُودَ أَخَاهُمۡ صَٰلِحٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥۖ هُوَ أَنشَأَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ وَٱسۡتَعۡمَرَكُمۡ فِيهَا فَٱسۡتَغۡفِرُوهُ ثُمَّ تُوبُوٓاْ إِلَيۡهِۚ إِنَّ رَبِّي قَرِيبٞ مُّجِيبٞ

Haka kuma Muka aiko wa Samudawa xan’uwansu Salihu. Ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta ba shi ba; Shi ne Ya halicce ku daga qasa, Ya kuma ba ku damar ku raya ta; to ku nemi gafararsa sannan ku tuba gare Shi. Lalle Ubangijina Makusanci ne, Mai amsawa.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 62

قَالُواْ يَٰصَٰلِحُ قَدۡ كُنتَ فِينَا مَرۡجُوّٗا قَبۡلَ هَٰذَآۖ أَتَنۡهَىٰنَآ أَن نَّعۡبُدَ مَا يَعۡبُدُ ءَابَآؤُنَا وَإِنَّنَا لَفِي شَكّٖ مِّمَّا تَدۡعُونَآ إِلَيۡهِ مُرِيبٖ

Suka ce: “Ya Salihu, haqiqa a da ka kasance a cikinmu abin yi wa (kyakkyawan) fata kafin (ka zo mana da) wannan; yanzu ka riqa hana mu mu bauta wa abin da iyayenmu suke bauta wa? Lalle mu kam tabbas muna matuqar shakka game da abin da kake kiran mu gare shi.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 63

قَالَ يَٰقَوۡمِ أَرَءَيۡتُمۡ إِن كُنتُ عَلَىٰ بَيِّنَةٖ مِّن رَّبِّي وَءَاتَىٰنِي مِنۡهُ رَحۡمَةٗ فَمَن يَنصُرُنِي مِنَ ٱللَّهِ إِنۡ عَصَيۡتُهُۥۖ فَمَا تَزِيدُونَنِي غَيۡرَ تَخۡسِيرٖ

Ya ce: “Ya ku mutanena, ku ba ni labari, yanzu idan na kasance a kan bayyananniyar hujja daga Ubangijina, Ya kuma ba ni rahama (ta annabci) to wa zai kare ni daga (azabar) Allah idan na sava masa? Don haka babu abin da za ku qare ni da shi in ban da tavewa.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 64

وَيَٰقَوۡمِ هَٰذِهِۦ نَاقَةُ ٱللَّهِ لَكُمۡ ءَايَةٗۖ فَذَرُوهَا تَأۡكُلۡ فِيٓ أَرۡضِ ٱللَّهِۖ وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابٞ قَرِيبٞ

“Kuma ya ku mutanena, wannan fa taguwar Allah ce a gare ku, sai ku bar ta ta ci a qasar Allah, kada ku cutar da ita, sai azaba ta kusa-kusa ta afka muku.”



Sourate: Suratu Hud

Verset : 65

فَعَقَرُوهَا فَقَالَ تَمَتَّعُواْ فِي دَارِكُمۡ ثَلَٰثَةَ أَيَّامٖۖ ذَٰلِكَ وَعۡدٌ غَيۡرُ مَكۡذُوبٖ

Amma sai suka soke ta, sai ya ce (da su): “Ku ji daxi cikin gidajenku kwana uku (rak). Wannan alqawari ne ba abin qaryatawa ba.”