Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 1

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 2

وَأَخۡرَجَتِ ٱلۡأَرۡضُ أَثۡقَالَهَا

Qasar kuma ta fitar da nauyaye-nauyayenta[1]


1- Watau ta fitar da mutanen da ke cikinta da sauran ma’adanan qarqashinta.


Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 3

وَقَالَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَا لَهَا

Mutum kuma ya ce: “Me ya same ta?”



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 4

يَوۡمَئِذٖ تُحَدِّثُ أَخۡبَارَهَا

A wannan ranar ne za ta ba da labaranta[1]


1- Watau ayyukan da aka yi a kanta masu kyau da munana.


Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 5

بِأَنَّ رَبَّكَ أَوۡحَىٰ لَهَا

Don Ubangijinka Ya umarce ta (da yin haka)



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 6

يَوۡمَئِذٖ يَصۡدُرُ ٱلنَّاسُ أَشۡتَاتٗا لِّيُرَوۡاْ أَعۡمَٰلَهُمۡ

A wannan ranar mutane za su fito a warwatse, don a nuna musu ayyukansu



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 7

فَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٍ خَيۡرٗا يَرَهُۥ

To duk wanda ya yi aikin alheri daidai da zarra zai gan shi



Sourate: Suratuz Zalzala

Verset : 8

وَمَن يَعۡمَلۡ مِثۡقَالَ ذَرَّةٖ شَرّٗا يَرَهُۥ

Wanda kuma duk ya yi aikin sharri daidai da zarra zai gan shi