Sourate: Suratul Alaq

Verset : 1

ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 2

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ

Ya halicci mutum daga gudan jini[1]


1- Watau bayan yana xigon maniyyi.


Sourate: Suratul Alaq

Verset : 3

ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ

Ka yi karatu alhali Ubangijinka Shi ne mafi karamci



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 4

ٱلَّذِي عَلَّمَ بِٱلۡقَلَمِ

Wanda Ya koyar ta (hanyar) alqalami



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 5

عَلَّمَ ٱلۡإِنسَٰنَ مَا لَمۡ يَعۡلَمۡ

Ya koyar da mutum abin da bai sani ba



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 6

كَلَّآ إِنَّ ٱلۡإِنسَٰنَ لَيَطۡغَىٰٓ

Tabbas! Lalle (jinsin) mutum haqiqa yana yin xagawa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 7

أَن رَّءَاهُ ٱسۡتَغۡنَىٰٓ

Don ya ga kansa yana cikin wadata



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 8

إِنَّ إِلَىٰ رَبِّكَ ٱلرُّجۡعَىٰٓ

Lalle kuma zuwa ga Ubangijinka ne makomar (taka) take



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 9

أَرَءَيۡتَ ٱلَّذِي يَنۡهَىٰ

Ka ba ni labarin wanda yake hana



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 10

عَبۡدًا إِذَا صَلَّىٰٓ

Bawa yayin da ya yi salla



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 11

أَرَءَيۡتَ إِن كَانَ عَلَى ٱلۡهُدَىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi Bawan) ya kasance a kan shiriya



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 12

أَوۡ أَمَرَ بِٱلتَّقۡوَىٰٓ

Ko kuma ya yi umarni da taqawa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 13

أَرَءَيۡتَ إِن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰٓ

Ka ba ni labari idan (shi mai hanawar) ya qaryata ya kuma ba da baya



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 14

أَلَمۡ يَعۡلَم بِأَنَّ ٱللَّهَ يَرَىٰ

Shin bai sani ba cewa lalle Allah Yana ganin (sa)?



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 15

كَلَّا لَئِن لَّمۡ يَنتَهِ لَنَسۡفَعَۢا بِٱلنَّاصِيَةِ

A’aha! Tabbas idan bai hanu ba to za Mu ja shi ta makwarkwaxar kai



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 16

نَاصِيَةٖ كَٰذِبَةٍ خَاطِئَةٖ

Makwarkwaxar kai mai qaryatawa, mai aikata laifi



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 17

فَلۡيَدۡعُ نَادِيَهُۥ

To ya kirawo majalisar tasa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 18

سَنَدۡعُ ٱلزَّبَانِيَةَ

Mu kuma lalle za Mu kirawo (mala’iku) zabaniyawa



Sourate: Suratul Alaq

Verset : 19

كَلَّا لَا تُطِعۡهُ وَٱسۡجُدۡۤ وَٱقۡتَرِب۩

Faufau! Kada ka bi shi, ka kuma yi salla, ka kusanta (ga Allah)